New Post

ABUBUWA BAKWAI (7) ABIN KULA GA DAN'ADAM

1. Duniyar da za a barta, me ya kawo hadama? 2. Dukiyar da za a lissafa daya bayan daya, me ya kawo tarata? 3. Rayuwar da zata kare, ina wani farin ciki? 4. Yarintar da tsufa zai zo mzta, me ya kawo takama? 5. Ana sauraren mutuwa, ina wata walwala? 6. Jikin da zai zama gawa, me ya jawo dagawa? 7. Karshe dai makomarsa kabari, me zai sa alfahari? Wanda ya manta da wadannan a ina ya bar hankalinsa? Allah yasa mu dace, yayi mana kyakkaywan karshe. Ameen!

KADA KA RAMA CUTA GA WANDA YA CUCEKA!

Kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka, kai kayi hakuri. Zaka samu abu biyu sakamakon hakan; * Na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. * Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

KADA KA BARI ZUCIYARKA TA ZALUNCEKA!

Kada ka sale zuciyarka ta zalunceka, tabbas zaluncin zuciya ga gangar jiki yake komawa, idan akayi wasa ya zamanto ya shafi rayuwa. Assasa bak'in tunani, yawan zargi da rashin tabbas akan wani aiki, zato, shakku ko kokwanto akan wani al'amari batare da tantance gaskiyarsa ba, shine zaluncinzuciya akan dan Adam. Maza ka hana zuciyarka don akwai hadurra dubu akan hakan.

MAHAKURCI MAWADACI

Tabbas ba kowane dandanon magani ne ke da dadi ba, amma babu shakka shine abu mafi dacewa ga dukkan mara lafiya. A lokuta da dama rayuwa takan dakeka da guduma ta jefaka acikin wani mawuyacin hali, kayi ta fama amma tayi maka tutsu. Amma idan kayi hakuri sannu ahankali zata kwaranye. Hakika ba duk abinda rai yake so yakan samu ba, amma bukata bata taba sauyawa ba kuma bata taba karewa ba. Don haka ka shirya bukatunka da kyau ka bisu daya bayan daya sannu a hankali, kayi gwa- gwarmaya, sannan kayi juriya. Tabbas mafarkinka zai zama gaskiya.

KO KA SAN?

Rayuwa bakin alqalami ce tana bukatar kaifi sannan tana son tsini. Kaifin don ka yanki magauta, tsinin kuwa don ka soki makiya. Haka zalika rayuwa kamar randar ruwan sanyi ce ta kasa tana bukatar tanaji da adani, kodn wata rana ka shayar da masoyanka. Da kyau ka lura da abu biyu a rayuwa; 1. Ka lura da mai zaginka mai aibantaka wata kila wata rana zai iya zama masoyinka mai yabonka 2. Ka lura da masoyinka na kusa mai yawan ambaton alkhairinka, wata kila wata rana zai iya zama makiyinka mai zaginka.

Thursday, 30 March 2017

MATATAH CE 71

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
             71

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

  🙋🏻kuyi hak'uri dani Masoyah, naga k'orafinku, kuma naji daɗi da gyaran da kukamun, kunsan dai ɗan adam ajizine, babu wanda yafi k'arfin kuskure, gaba ɗaya na manta na saka Saude bata gane Yasseer, wasu na cewa ya kamata ta ganeshi tunda ita a ɗan birninshi ta sanshi, maganar gaskia daman Saude bata ganeshi ba, ita da tazo Abuja ma taa canja ballantana shi daya bar k'asar, ga matarshi Rabi'ah dake kula dashi😉 kuma idan baku manta ba Saude ma tana yarinya a lokacin daya tafi ya barta, Nagode sosai da tunatarwar da kukamun, wallahi naji daɗi sosae, don Allah ko a gaba kuka k'aracin karo da wani gyaran ina maraba dashi, Nagode sosai Masoyah, Allah yabar k'auna, LYSM😍

www.babymsh.blogspot.com

  Gabantane ya shiga faɗuwa, har wani kyarma take k'afafunta suka kasa ɗaukanta, tana shirin faɗuwa ya tafi zai rik'ota, ta kauce kawai ta juya zata tafi.
   Zata ita manta kamanninshi, zata iya manta sautin muryanshi, da duk wani abu nashi anma bazata iya manta ɗumin jikinshi ba, bazata iya manta yanayin da takeji a duk sanda jikinta da nashi suka haɗu ba.
   Tana shirin tafiya ya rik'o hannunta, ta juyo suka haɗa ido, zuciyarta ce ke cewa A'ah Saudat, don yana da yanayin mijinki da kuma sunanshi ba lallai ne ya zama Yasseer ɗinki ba, kima fiddarai da sake ganinshi a rayuwanki.
   Bata taɓa tsayawa ta k'are mishi kallo ba, Yayan Najib farine sosai, yafi Najib tsayi da cikar jiki, ga wani irin k'warjini da yake tare dashi, duk da ko ranshi a ɓace yake ka kalleshi kamar yana murmushi, saɓanin Najib da ko murmushin tsadane dashi, yafi Najib sakin jiki da fira da mutane. Kyakkyawane na k'arshe harta kasa gane shida Najib wanne yafi.

   Ji yake kamar ya fito fili ya faɗa mata abun dake zuciyarshi, anma ya kasa koda buɗe bakinshi, idon yana kallonta ganinta yake kamar Saudenshi sai dai ya kasa yarda da zuciyarshi, mezai kawo Saude Abuja kuma gidansu? Kawai dai wata soyayyar ce Allah ya k'addaroma zuciyarshi, a hankali ya saki hannunta, kamar wacce take jira da gudu tabar ɗakin.
    Fitar da basuyi ba kenan. Ranar bata samu halartar partyn da Abokan Najib suka haɗa mishi ba, don gaba ɗaya ji takeyi babu abinda zata iyayi, saima ta fake da ciwon cikinta.
   Washe gari Momie tayi Mother's day, har ranar Saude bata fitowa ko k'ofan ɗakinta, wani tunanin Yasseer ne yake dawo mata sabo, ta rasa gane tsanarshi ne, haushinshi, ko kuma soyayyarsa, ga wani salon da Yayan Najib kezo mata dashi.

  Kowanne ɓangarori anata hidiman biki, su gwaggo ma ana k'yauye anata shagali sai ranar ɗaurin aure zasuzo, Najib ma duk ya damu na daina ganin Saude sai dai suyi waya, anma inya tuna ta kusan zama tashi ma gaba ɗaya sai hankalinshi ya kwanta.

  Ranar ɗaurin aure.
Tunda safe da sak'on Najib ta farka.
     "Yau burina zai cika na samunki, na tabbatar babu sauran wani garkuwa yanzu tsakanina dake, ke tawace, ni naki ne, ina sonki Masoyiyah"
  Murmushi tayi bata maida mishi ba saita kirashi, don a halin yanzu tafiso ta saurari muryarshi fiye da komai, "Masoyi an kusa zama Ango"
   "nama zama dai, waɗannan awoyinma duk zasu shuɗene bayan sun sadani da farin cikina"
   "Me kakeyi yanzu?"
       "tafiya nake"
    "Ango daman yana yawo?"
       "tohh yana iya tunda kina guduna?"
  "hhm" knockn k'ofanta taji anayi, ta sauka tana saka hijabi.
     "ana miki knockn fa"
    "Gashi zan buɗe"
Tana buɗewa sukai ido huɗu dashi, suka sakar ma juna murmushi, "Yadai?"
    "Amaryatah nazo gani" ta tsaya jikin k'ofan bata bashi hanya ba sai so yake ya shiga.
    "ko ba'a maraba dani in koma?"
  "bak'in naka ka baro ka fito?"
   "eeh mana tunda ina son ganinki"
   Ya wuce ta ya zauna ɗaya daga cikin kujerun ɗakin.

  Dai dai lokacin Yasseer na can ɗakinsu ya rasa meke mishi daɗi, tunanin ta yanda zai dakatar da auren kawai yake, ga wani sabuwar rigimar da Rabi'ah ta ɓullo da ita, ciki ne da ita taa rantse mishi bazata haife ba, ita bata shirya haihuwa yanzu ba, dukiyarshi ma gaba ɗaya ya mata alk'awari akan ta haife mishi ɗanshi anma tak'i jin lallashi, ga damuwan zai rasa Saudat kuma.
    Meya kamata yayi? Yana kwance shi kaɗai yasan azabar da yakeji a jikinshi, yaje juyawa yaci karo da wayar Najib ɗayar daya bari, harya maida zai ajje ya hango hotanshi da Saude mak'ale a wallpaper, su duka suna dariya, wani irin daɗi yaji yana kallonta a hotan, gaba ɗaya kewanta yakeji, tunawa yayi da hotunanta da Najib ya taɓa cewa zai nuna mishi, ya shiga dubasu ba wahala sai gashi ya gansu, ya shiga yana dubawa babu wanda baiyi kyau ba, harya jawo wayanshi zai fara turawa yaci karo da wanda Najib yayi mata a tana er k'auye, wani irin zabura yayi ya tashi zaune.
    Zazzafan zazzaɓine a jikinshi, anma ji yayi lokaci ɗaya kamar an yaye mishi shi,  "Saude? Lallai kuwa biri yayi kama da mutum, babu tantama wannan ce Saudenshi" wata zuciyar tace 'anma mezai kawo Saude anan? Wannan sunanta Saudat kuma matar da k'aninshi zai aura! Mezai kai Saude yin aure saman aure? Anma kuma ai ance daga k'auye tazo, gani yayi kamar yana ɓatama ma kanshi lokaci, ya diro da niyyar zuwa ya tambaya Momie, don ta bashi tabbacin abinda zuciyarshi take zargi.

   Cikin farin ciki yake tafiya kamar wanda akama bushara da gidan Aljannah, anan ya wuce abokan Najib en ɗaurin aure, ya wuce can cikin gida, duk taron matan da kema momie hidima da bak'in dake zuwa idonshi rufe ya shiga yana tambayar Momie, dak'yar ya ganota, ya jawo hannunta cikin zumuɗi, "Momie kizo kiji don Allah"
    "Meye zanji? Kai har yau kamar k'aramun yaro, bakaga abunda nake ba?"
     "plz Momie maganar nada muhimmanci ne, don Allah kizo kiji"
    "Ya zanyi da bak'in dake zuwa? Kasan en ɗaurin aurema duk yanzu zasuzo, kaje ka shirya mana"
   Rik'o hannunta yayi duk ya shagwaɓe kaman shine Autan "kizo kiji Momie bazaki daɗe ba"

  Can ya jata ɗakin da babu kowa ciki, "ki zauna kiji don Allah Momie" ta ɗanji daɗi da taga ya fara sakewa, k'ila damuwar tashice ya tashi faɗa mata, ta zauna tana saurarenshi anma duk hankalinta ya tafi ga hidimarta data baro.
    "Momie don Allah ki faɗamun ina aka samo matarnan da Najib zai aura?"
    "lafiyanka kuwa? Wai menene matsalanka da aurennan?"
  "zan faɗa miki Momie, wallahi zan faɗa miki ko menene damuwatah, anma ki fara faɗamun Momie" tayi shiru tana ɗan tunani,
    "Don Allah Momie ki faɗamun" ganin yanda yaketa gamata da Allah ya sanyata fara bashi labarin Saude kamar yanda baba Haja ta faɗa mata, komai bata rage ba harda cewa mijinta ya rasu da kuma er da tazo da ita.
   Cikin farin ciki yake tambayarta shekaran Hafsat nawa sanda sukazo? Ta faɗa mishi harma da sunanta na daa Saude, kamar ya fasa ihu don daɗi yadai daure yace "Momie ya sunan mijin nata?"
      "Yasseer" ai baisan sanda ya k'ank'ame Momie ba yana murna, ya saketa ya duk'a har k'asa yayi sujjada, "Alhamdulillahi" kawai bakinshi ke furtawa, tsananin murna ma ya hanashi cewa komi sai dai yaci gaba da zagaye ɗakin.

   Kallonshi kawai Momie keyi kaman wani zautacce, saida ya gama murnarshi take kallonshi baki buɗe, ya dawo kusa da k'afafun Momie ya zauna, "Momie ta tabbata dai Saude MATATAH CE, wallahi MATATAH CE dana biya sadaki aka ɗaura mana aure"
   Sai yanzu ta ida tsorata da Al'amarinshi, gaba ɗaya kamar k'walwarshi ta taɓu take kallonshi, tausayinshi takeji, kodai damuwar tashi ce ta fara rikita shi?
     "Matar k'aninka fa ce da za'a ɗaura musu aure yanzu ba daɗewa kake ik'irarin cewa matar kace, ba tun yanzu na gane take-taken ka ba, tun wuri ka fita idona karma ka ɗaga maganar nan wani yaji, wannan ai hanyar da zaka haddasa rigima ne tsakaninka da ɗan uwanka"
     "wallahi Momie da gaske nake, Saudat MATATAH CE, nine mijinta Yasseer, na kasa faɗa muku ne don bansan yanda zaku ɗauka maganar ba, anma k'auyensu ne nayi bautan k'asa kuma a can aka bani aurenta"
    "k'arya kake mijinta ya rasu, ka rabani da shirmennan naka ka bani hanya in wuce, sai dai in daman akwai wani abun a ranka"
   Kamar yayi hawaye yake rok'on Momie, "Don Allah Momie karki yanke hukunci a rashin sani, wannan auren wallahi gaba ɗaya bai halarta ba, nine mijinta kuma gani a raye, ki yarda dani aurene za'a ɗaura saman aure"

  Ita dai Momie ko maganganunshi bata fahimta, gaba ɗaya a tsorace take dashi, kallon marar lafiya take mishi, "Momie ki kirata ki tambayeta, zata faɗa miki gaskia da bakinta, idan harta musa na yarda ba Matatah bace"
    "kana cikin hankalinka kuwa? Tun wuri ka dawo da tunaninka, Matar k'anenka ce fa, idan har taji maganar nanma ai girmanka zai faɗi a idanunta, na faɗa maka ka daina maganar nan ko?" ta wuceshi zata tafi.

  Ya buɗa baki yanda zata jiyoshi, "Momie kinamun kallon mahaukaci ko" wallahi gaskiyatah nake faɗa, don Allah ki saurareni Momie, ina cikin hankalina" tsayawa tayi.
    "ki aika aka kira miki ita, idanta k'aryata abunda na faɗa na yarda da duk wani hukunci da zaku yankemun"
   Jikinta duk yayi sanyi da maganganunshi, ta dawo ta zauna, yananan zaune ta buga waya, sannan ya sauke ajiyar zuciyah.
    Najib na ɗakin Saudat Abokan wasanshi sun sanyasu gaba suna tsokanarshi, yama kasa hak'urin akai mishi ita zaizo ya mata zaune ko shirin ɗaurin auren bazai tafi yayi ba, shine ma mai k'ok'arin maida musu, don dagashi har ita babu mai yawan magana cikinsu, kiran Momie ne ya fiddasu wurin ya tafi ya rakata. Tsayawa tayi kafin su shiga ɗakin.
   "ka jirani karka biyoni kaji me Momiena zata cemun"
       "kina da sirrin daya fini ne? Ai duk wani sirrinki nawa ne, don haka daga yanzu duk inda kika sanya k'afarki ina tare dake, bazan taɓa barinki ba"
    "Gaskia na more miji dake matuk'ar k'aunatah, kaine sirrina Ya Najib, idanna zama matarka dukkan wani burina ya gama cika"

Maganan Momie sukaji, "Saudat ce anan?"
   Da sauri ta shiga, "eeh Momie gani", "keda waye?" sai gashi shima ya shiga.
   Sai lokacin suka kula da Yasseer da yayi zaman dirshan a gaban Momie, gaba ɗaya itama yanayinta ya canja, tayi niyyar korar Najib don bai kamata ayi maganar gabanshi ba, sai kuma taga ai shima ɗan uwane,
  Cikin hikima don kar Saude tayi saurin gano yanayin da suke ciki tace "kince mijinki ya rasu ko?" Saude ta ɗaga kai ita mai gaskiyarnan,
  Momie ta nuna Yasseer, sannan take kallon Saude cikin ido "wannan fa kin sanshi? Ki faɗamun miye tsakaninki dashi" k'walalo ido tayi tana kallon Yasseer, gaba ɗaya hankalinta ya tashi, cikin sark'ewar murya tace "Ya Yasseer, anan gidan na sanshi"
    Najib yace " Meke faruwane Momie? Wacce irin magana ce wannan?"
  Hannu ta ɗaga mishi alamun dakatarwa, "ki faɗamun gaskia" ta ɗaga kai tana kallon Yasseer, ita tsakaninta da Allah a farko gaskia ta faɗa, toh me Momie ke nufi?

Yasseer ne ya katse mata tunani, sai dai ta ganshi kawai a gabanta,
   "ki faɗi gaskia Saude, ki faɗa musu ke MATATAH CE, nine Yasseer mijinki, nasan laifin dana miki fiye da mutuwa saiki ɗaura mun, ki faɗa musu gaskiya, ki faɗa musu mijinki ba mutuwa yayi ba"
   Najib ne ya tureshi daga gabanta cikin hucin zuciyah yace "wannan wane irin abune kakeyi bruhh? Karma ka soma, Saudat MATATAH CE, kuma munan bamusan da wani maganar aurenka ba"
   Momie ce ta mishi tsawa, yayi shiru anma sai huci yake.
    "Saude kiyi magana don Allah, karki bari ku aikata HARAMTACCEN ZAMA, nine Yasseer naki wanda naje bautan k'asa k'auyenku aka bani aurenki, wallahi nasha wahala nemanki, don Allah ki buɗa baki ki faɗa musu gaskia, kada laifin dana miki ya kaiki aikata zunubi, ni mai laifine, ki hukuntani da duk hukuncin da zaisa kiji sauk'i a zuciyarki, anma karki aikata saɓon ubangiji, karki bari a ɗaura aurennan, don har yanzu ke MATATAH CE!"
  "Ya isa haka" momie ta dakatar dashi, sannan ta kalla Saude, "ki faɗamun tsakaninki da Allah mijinki yana raye, Yasseer ɗana shine mijinki?"

  ©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 70

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
              70

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Da Yasseer yayi Sallah yaso ya koma barci abun ya gagara, wani irin azababben ciwon kai ya saukar mishi ko motsin kirki dak'yar yake da kan, gaba ɗaya ji yake kaman duniyar ne duka yake ɗauka.
    Hayaniyarsu da yake jiyowa a falonne ya k'ara hargitsashi, daganan yana jiyo dariyar Najib da Saudat, a hankali yake fita zuwa falon ya ɗaura hannuwanshi duka biyun yaa dafe, yana tafiya dak'yar.
  Sun baje I.V tana gani, ba k'aramun kyau sukai ba da gani an kashe kuɗi da yawa, ko meya haɗosu? Cikin wasan ta tilla mishi filon kujera, ya tare da hannuwanshi biyu bai sameshi ba yana mata gwalo ta k'ara jefa mishi wani sai saman k'afan Yasseer.

   Su duka suka ɗaga ido suna kallonshi, da gani yanajin azabar ciwon kan lokaci ɗaya har ya faɗa, Najib ya mik'e a ruɗe yaje inda yake.
   "lafiyanka bruhh? Meke damunka?"
  Yak'e kawai ya mishi yace "ba komai" ya raɓa gefenshi zai bar musu ɗakin, Saude ta gaisheshi, hakanan ya tsinci kanshi da sakar mata fuska.
    "lafiya lau Saudat ya kika tashi?"
     "Alhmdlh" sai kuma ya fita yanajin haushin zuciyarshi da rigimar da take shirin kunno mishi, me yasa zuciyarshi zata mishi haka? Da gani basai an faɗa ba Saudat da Najib masoyane da suke matuk'ar son junansu, tayayama zaiyi nasara?
   Yana fita Najib ya zauna jikinshi a sanyaye, damuwa ce bayyane a fuskarshi, "gaskia bruhh yana da damuwa, kuma nasan zurfin cikinshi bazai taɓa bari ya faɗamun ba, koma menene tunda kika ganshi haka yana matuk'ar damunshi da yawa, shi mutum ne da bai ajje damuwa a ranshi"
  Itama sosai ta tausayama halin da Yasseer yake, "Allah sarki, Allah yasa dai ba wani matsala bane"
    "Ameen"

Ɗakin Momie ya shiga, tana duba zannuwan gadon data saima Saude, da ganin yanayinshi ta maida hankalinta kanshi, zaman dirshan yayi a saman carpet ya jinginar da kanshi a bango,
     Momie duk hankalinta ya tashi ta koma inda yake "Baka lafiya ne?" ya girgiza kai kuma ya ɗaga.
    "meke damunka?" wasu siraran hawayene suka gangaro mishi, cikin muryan tausayi yace "nima ban sani ba Momie"
    "bazai yiwu ba, dole zakasan dalilin damuwarka, sai dai in yauma bazaka faɗamun ba"
   Tohh ciki waccema zai faɗa mata? Labarin Saude Matar daya aura a k'auye ya gudu ya barta da har yanzu soyayyarta da tunaninta suka hana zuciyarshi sukuni, har yanzu dana sanin abunda ya aikata yake? Ko kuma matsalar Rabi'ah ta kullum take damun k'wak'walwarshi? Bata rageshi da komai ba, duk wani soyayyar miji da mata tana nuna mishi, matsalanshi ɗaya da ita rashin son haihuwa, kuma Allah ya yishi da son yara, shima yanason yaga k'wanshi a duniya, ko kuma babban matsalan da shi kanshi kunyar kanshi yakeji, wai yanason matar da k'aninshi zai aura!
     "ban sani ba Momie, anma inajin kaman duniya gaba ɗaya ta juyamun baya"
      "meyasa kace haka?"
   "ba komai Momie, anma ina neman Alfarma a wurinku"
  "ka faɗi koma menene"
     "Don Allah Momie a taimakamun a ɗaga ranar ɗaurin aurennan"
   "saboda me?"
       "yayi shiru ya kasa bata amsa"
  "Karka damu, insha Allah kafin lokacin kaa warware, ka yawaita addu'a akan damuwarka, shi Allah maji rok'on bawansa ne, akwai wata addu'ah a cikin husnul muslim: Allaahumma 'innee 'abduka, ibnu 'abdika, ibnu 'amatika, naasiyatee biyadika, maadhin fiyya hukmuka, 'adlun fiyya qadhaa'uka, 'as'aluka bikulli ismin huwa laka, sammayta bihi nafsaka, 'aw 'anzaltahu fee kitaabika, 'aw 'allamtahu 'ahadan min khalqika, 'awista'tharta bihi fee 'ilmil-ghaybi 'indaka, 'an taj'alal-Qur'aana rabee'a qalbee, wa noora sadree, wa jalaa'a huznee, wa thahaaba hammee ."
   "fassarar addu'ar shine: Ya Allah! Ni bawanka ne, kuma ɗan bawanka, kuma ɗan baiwarka. Goshina a hannunka yake, hukuncinka zartacce ne a kai na, kuma k'addararka gareni mai adalci ce. Ina rok'onka da kowane suna naka, wana ka ambaci kanka dashi, ko ka saukar dashi a cikin littafinka, ko ka sanar dashi ga wani daga cikin halittarka, koka keɓance kanka da saninsa a cikin ilmin fake da ke wurinka, da ka sanya Al-Qur'ani ya zama kaka ga zuciyata, da haske a k'irjina, da kwaranyewa ga bak'in cikina, da kuma mai tafiyar da damuwata."
    "insha Allah zaka samu sauk'i a zuciyarka, bansan meke damunka ba, anma duk ɗan adam daka gani Allah yana jarrabarshi, kuma imanin mutum baya cika saiya yarda da k'addara mai kyau da marar kyau, komai kaga ya faru dakai k'addarane, idanma matsala tsakaninka da Rabi'ah ne kayi k'ok'arin gyarawa tun wuri, kada ka taɓa raunana zuciyar mace, kada kace zaka juya mata baya don matsalar dake tare da ita na rashin haihuwa"
    "kodai matsalan data ɗaurawa kanta?" ya faɗa a zuciyarshi, baison ya faɗama Momie tsakaninshi da Rabi'ah ne, don bazaiso ya haɗasu ta dinga ganin bak'in taba, anma dai duk yanda zaiyi da Rabi'ah batajin lallami ko shawara,
      "Na gode Momie" ya furta yana zubar da hawaye, saiga Hafsat ta shigo da gudu Najib ya biyota, baisan sanda ya mik'a hannunta tazo wurinshi ba, ta zulle ko kallanshi batayi ba ta faɗa kan Momie.
    "Guje-gujenne ko Hafsa? Bana hana ba?"
  Tana shesshek'ar gudu sai dariyarta take "Momie Daddy ne ya biyoni"
    "shine kika rugo haka ko ɗayan Daddynki bazaki gaisar ba?"
   "ni Daddy na ɗaya mai sona, ban haɗashi da kowa ba Momie"
   "Wannan ma babanki ne, ki gaisheshi nace" ta kalleshi tana tura baki, hakanan yarinya da ita gaba ɗaya haushinshi takeji, sai kuma ta ganshi yana hawaye sosai ya bata tausayi.
   Ta tafi inda yake, ta saka k'asan rigarta tana share mishi hawaye, ya ɗago yana kallonta, murmushi ta mishi, "Mamana taa hana kukan rigima, idan ta ganka kana kuka Momie zata faɗa mawa kuma Daddyna bazai kaika shan ice cream ba"
    Murmushi yayi yarinyar sai k'ara burgeshi take, inama ace tashi ce? Lallai iyayenta ba k'aramin Sa'a sukai da samunta ba.
    "na daina kuka, anma saikin yarda mun shirya bazaki k'ara guduna ba"
  Ta mak'ale kafaɗa "nina daina shiri da kowa, best frnd na ɗaya"
   "wanene?"
     "Daddy na"

Najib ne ya shigo ɗakin yana nemanta, ganin Yasseer zaune gaban Momie harya juya zaiyi baya, Yasseer ya mik'e yabar ɗakin duk kalanshi ya canja.
   Momie ta kalleshi, "yayanka ya faɗa maka damuwarshi?"
    "A'ah Momie, kin sanshi dai da zurfin ciki"
    "tohm Allah ya kyauta"
       "Ameen"
  "Ina Saudat ɗin?"
      "ta wuce ɗaki tasha maganin ciwon cikinta"
   "ni wannan ciwon ciki da tak'i yarda aje asibiti"
     "ai tace da tasha magani yake tafiya"
    "Allah ya bata lafiya"
  "Ameen"

  Hidimar biki kawai ake, ranar  laraba za'a fara shagulgulan, don ita Saude in yanda takeso nema baza'ayi komai ba, tunda safe take jiran Najib shiru bai fito ba, tana ta mishi waya bai ɗauka ba, ta wuce ɗakinsu a falo ta tsaya tana k'wala mishi kira, taji shiru dai saita shiga ɗakin don bataga alaman Yasseer na ciki ba.
   Najib ne kwance shi kaɗai, ganinshi da shirin fita ne ya tabbatar mata ba barci yake ba.
    "Masoyi kaifa nake jira" ya mata shiru kawai,
   "in tafiyatah bazaka kaini ba?" saima ya k'ara gyara kwanciya.
   Ta ɗan saka hannu tana buga filon da yake kwance, yanaso yayi dariya ya rufe fuskarshi da filo,
    "daman nasan ba barci kake ba" tayi dariyar mugunta, a ranta tace yanzu zaka tashi.
  Ta ɗauko wayanta ta fara mishi video, "idan kana barcinma kafi kyau, tunda bazaka kaini ba bara in maka video, wow! Kaaga yanda kayi kyau kuwa?" duk ta kashe mishi ido da flasher ya kasa rufe idon da daɗi.
    "wai da gaske videon kike?"
  "ina ruwan mai barci da abunda nake?" ya diro daga saman gado.
    "in gani inda gaske ne"
        "nak'i fa" ta tashi ya biyota da gudu, suka fara zagaye ɗakin taa hanashi ya gani.

    Suna cikin zagaye ɗakin ya samu dak'yar ya kamota ya rik'e, ɗaga wayan yayi, "kinga irin videon da zaki ɗauka nan"
   Ta fara k'ok'arin zamewa, shikam hankalinshi kwance yanata mata dariya dak'yar ta k'wace, da gudu tabar ɗakin,  yace, "Matsoraciya kawai"
  Da yake ba kallon gabanta take ba, tana fita sai dai taji ta faɗa ma mutum, kwance saman k'irjinshi, wani iri takeji a jikinta, gaba ɗaya ma ta kasa ɗagowa, ko ban faɗa ba kunsan ko waye.
    Tafe yake shima gaba ɗaya komai nashi ya canja, ko tafiya yake tunani ne kawai. Zuciyarshi, ga tarin damuwa data mishi yawa.

©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 69

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
             69

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

  Banda Rabi'ah babu wanda ya lura da irin kallon da Yasseer ke yima Saude, Najib da Momie ma maganarsu suke hankalinsu baya wurin, tuni ta ɓata rai fuska a cusgune tace "Hniee ana gaidaka fa"
    baimasan tana yi ba, tana ta mishi magana hankalinshi duk yana kan Saude, saida taje har inda yake ta taɓoshi sannan ya ɗauke idanunshi a rikice, "me...meya faru" ya tambayeta yana susar k'eya.  
   "gaisheka ake mana"
Ya k'ara kallon Saude da har lokacin idanunta ke a k'asa, "Lafiya lau ya gida?"
    "Alhmdlh ya hanya?"
   "ba gajia" duk a ɗan rikice yake maganar, muryarta da haɗuwar idanunsu ba k'aramin rikitashi yayi ba, ita dai bata wani ja maganar ba.
   Jin bazai iya juya kanshi ba, yaja Najib suka bar ɗakin, yana tafiya yana lek'en Saude harya kusa yima k'ofa karo.

  Ko kaɗan Yasseer bai gane Saude ba, shi dai Saudat ya gani, Najib ma farkon ganinshi da ita a Saudat ya kasa ganeta, ballantana Yasseer da kusan shekara biyar rabonshi da ita, a can k'auyen katsina ya barota tayaya zaiyi tunaninta a Abujama? Gashi tayi wani irin kyau da wayewa, maganarta ma kawai abun kallone, ga wani irin haɗaɗɗen murmushi, komai nata cikin wayewa da nutsuwa, ko a Moscow baiga kyakkyawa kamanta ba. Wani irin yanayi yakeji a kanta daga kallo ɗaya, yanayin da baisan ta yanda zai fassarashi ba(soyayyar gaskiyar kenan😄).
    Koda suka zauna cin abincin dare, gaba ɗaya ya kasa ɗauke idanunshi a kanta, su duka sun kasa cin abinci sai juya cokali suke, shi ya kasa cin komai saboda baison daina kallon kyakkyaqar fuskarta, ita kuma kallon da yake mata duk ta tsargu, gaba ɗaya zaman wurin ya isheta jikinta ya bata ita kawai yake kallo, mik'ewa tayi kawai ba tare da taci wani abun kirki ba.
    Momie tace "kar dai ki cemun kin k'oshi"
   "wallahi kau Momie"
   Najib ya mik'e yabi bayanta, a falo suka zauna.
   "ki faɗamun gaskia kodai abincinnan bakijin daɗinshi in nemo miki wani?"
   "A'ah na k'oshi fa"
       "me kikaci da zaki k'oshi? Ina lura dake fa babu abinda kikaci"
   "na k'oshinne fa, anma mezai hanani cin abinci"
   "shikenan, dare yayi da munje amsar ɗinkuna"
   "sai muje da safe ai"
  Yasseer ne yazo wucewa, ya gansu zaune a falon yanajin Najib ya mishi magana anma ya share, wani haushi yakeji a ranshi ganinsu tare, hakanan yakejin kishin ganinshi da Saude, shi kanshi baisan dalili ba.

  Wuri ya samu ya zauna a falon, kallo ya kunna ya koma nesa dasu anma hankalinshi na a kansu duk da ba saurarensu yake ba, wani irin bak'in ciki yake ji a zuciyarshi ganin yanda suke firarsu da nishaɗi, sai dariya suke, dariyan tata abin sha'awa, daga nesa yake hangen fararen hak'oranta.
    Rabi'ah ce ta iskeshi, ita ta katse mishi tunani.
    "Hniee gidan fa sai yaushe?"
  A harzuk'e ya kalleta, "Biki kikazo ko ganin gida? Ki jira nan ayi hidiman biki dake"
   Ta sassauta murya, "duka nazo, don Allah banijin daɗin halinnan daka koya na saurin faɗa, idan kuma baka da lokaci in faɗama Momie a haɗoni da driver"
   Kallon sama da k'asa ya mata cikin k'unar zuciya, "kuma a haka zakije gidan?"
    "A'ah zuwa nayi in tuna maka, bara in ɗauko mayafi"
  Ba daɗewa tayima su Momie sallama ta fito, Anan suka bar su Saude har tana cewa "auntie kodai muyi rakiya?"
    "A'ah waceni in wahalar da Amarya? Na yafe jibi zan dawo mu fara shagali ai"
   "Tohm auntie saikun dawo" ganin ya tsaya tace "muje mana" ya tafi tabi bayanshi.

   Yanda Yasseer yaga ranar haka yaga daren, ga tunanin Saude da kullum dare yake dawo mishi sabo fil, da kuma tunanin Saudat daya rufe ido suffarta ce ke dawo mishi, idan ya buɗe ido kyakkyawan murmushinta ne ke dawo mishi, Najib na gefenshi yana barci hankali kwance, anma shi tunani ya hanashi, duk yanda yaso daina tunaninta, hotanta ya kasa ɓacewa a zuciyarshi.
    Meke shirin faruwa dani? Saudat fa matar k'anenah ce kuma ɗan uwana da muka shak'u sosai, wanda yake shirin aura nan da sati ɗaya. Meyasa zuciyatah zatamun haka? Kullum tana kamuwa da soyayyar abunda zan rasa.
   Ina bazan taɓa rasa Saudat ba!, ya bama zuciyarshi amsa, Saudat MATATAH CE, dani ta dace, ya zama dole inyi wani abu kafin in rasata.

   ©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 68

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
             68

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

  Watansu shidda da komawa, suka fara zana s.s.c.e, daman tuni aka saka sunanta, sai karatu ya k'aru, kullum cikin karatu take fiye da lokacin data zana j.s.c.e, tun kafinta fara jarabawar Najib ya biya mata ta rubuta jamb.
    Karatun da take da maida hankalinta yasa komai yazo mata cikin sauk'i, babu abunda ya shige mata duhu.
    Ranar yayesu sunsha kuka, duk da bata da k'awa ɗaya anma duk ta shak'u dasu, tasha kyaututtuka ba kaɗan ba, duk da bata rik'e wani muk'ami ba, ita ta samu kyautan tsabta, kyautan biyayya, kyautan zuwa da wuri, wacce tafi kowa cin english, maths, har teacher n su mai physic da suka sanyama ido saboda mak'o saida ya mata kyauta, da aka fiddota speach yanda take zuba turanci ba k'aramin burge mutanen wurin tayi ba, en makarantarsu kamar su haɗiyeta don murna, ta samu kyautuka sosai wanda bata taɓa tunanin samu ba.

  Da dare kuma Najib ya haɗa mata nashi Partyn, duk wasu Abokanshi da yakeji dasu sun halarta a wurin, tun daga na Abuja har wanda suke aiki a Kaduna, itama ta gayyaci k'awayenta sosae har wanda bata tunani sunzo.
   Ba k'aramin haɗuwa Saude tayi a wurin ba, cikin doguwar rigarta fara tas mai kwalliyan duwatsu, duk inda ta saka k'afarta Najib na biyu da ita, sosai suka haske a wurin.
  A hankali tace mishi, "nafa lura duk en matan wurinnan kishi suke dani"
    "Saboda kinfiso kyau da iya kwalliya ba"
   Tayi dariya har hak'oranta suka fito, "Saboda ni nake da saurayin da yafi kowanne dai, kaga dole suyi kishi don nawa yafi nasu"
   "laah! Kin nusar dani ma shiyasa su Jabir keta binki da kallo ko, bakinsu ya kasa shiru sai yabawa suke da haɗuwarki, aikam partynnan an tashi hakanan"
   "Saboda me?"
       "Saboda ina matuk'ar kishinki mana, na gaji ana ganemun matah hakanan"
   "haba! Abokankane fa"
  "koda en gidanmu ne, bakisan yanda nakesonki da kishinki bane, komai zan iyayi idan wani ya raɓeki"
   Shiru tayi don yama rufe mata bakin magana, da yake da wuri aka fara Partyn dare baiyi wani nisa ba aka tashi, abokansu da yawa sunso yima Saude da Najib hotuna a wayansu, anma yak'i yarda, sukace ai indai sun dawo bazai hana suyi mata na biki ba.

   Saida aka tashi Ahmad yazo, duk Abokansu sun gama tafiya, tare suka fito da Saude tarbanshi, cikin girmamawa suka gaisa sannan tace,
      "mufa da har munyi fushi"
   "Haba Matar Aboki, keda nake cewa da zaki tayani ban hak'uri"
     "ai kamar nama fishi fushin fa"
   "tohh afuwan, wallahi abubuwa da yawa na bari na taho, don dai kawai bazan iya hak'urin nan da sati biyu biki ba sannan inga Saudat ɗinnan data sacemun abokina gaba ɗaya"
    Tayi dariya sosae "shiɗinne ma na sace duka ba zuciyarshi ba kenan?"
      "ai tunda kina da zuciyarshi, ke kikeda ragamar janshi duk inda kikeso, yanzu banda wani sauran damuwa, don naa tabbatar da abokina ya bada zuciyarshi a inda ta dace"
   "anma kinason gulma?"
   "inasonji, anma gulma fa babu kyau"
   "an gama tunda kinason ji, sirri zan faɗa miki ba gulma ba. Kinga abokina da kike ganinshi, son matane dashi don haka kisan yanda zaki rabashi da kallon mata"
   Ta waro ido, "Na shiga daɗi" ya k'yalk'yale da dariya, "yanzu nasan kina sonshi yanda ya kamata, anma maganar gaskia wallahi tunda muka tashi ban taɓa sanin budurwar Najib ba bayanke, bai taɓa soyayya ba, a kanki ya fara, kuma yana matuk'ar sonki, yana tsoran yaudara, don Allah ki rik'eshi amana, kada ki raunana wannan jaririyar zuciyar tashi"
   "Insha Allah, kamar yanda nasan shima bazai taɓa barin soyayyatah ba"

   "Kai! Wai me kake faɗa mata ne tun ɗazu ka tsayar da matar mutane?"
    "abunda basai kaji ba, yau na fara ganinta ma baza'a barni mu gaisa ba"
   "nak'i ɗin, komai za'ace ayi gabana"
  Mik'ewa tayi, "bara in fara tafiya, barci nakeji"
   "tohm masoyiya, kiyi barci mai daɗi" Ahmad ma ya mata saida Safe, anan gidan ya kwana da Najib, washe gari tunda safe ya wuce, duk da Najib yaso ya tsaya sai bayan biki.

  Saura sati biyu biki, Momie taje babban wurin sayarda furnitures na Abuja, ta zaɓar mata fitinannun kayan ɗakin masu hegen kyau, gaba ɗaya kayan sun tasarma 3million, koda aka faɗa ma Momie ko ɗar bataji ba ta biya kuɗin.
   Kayan kitchen ma mak'udan kuɗi ta kashe wurin haɗa mata su, jin Saude take kamar ɗiyar data haifa, gaba ɗaya taa ɗaukema su kawu duk wani hidima, komai ita takeyi.
   Haɗaɗɗen lefe Najib ya haɗoma er gatan tata, faɗan irin haɗuwar kayan da kuma kashe kuɗin ɓata lokaci ne, idan kuka tuna wanda yasai mata a tana Saudenta, akwatinan kansu abun kallone, Momie kanta ta yaba da kayan, don farko jira take kawai ya kawo ta raina saiya ƙaroma Saudenta, sai gashi ma ya wuce yanda take tunani, Saude kam har kukan murna tayi, bazata taɓa mantawa da karamcin dasu Momie suka mata ba, kullum addu'arta Allah ya bata ikon fita kunyarsu, don sun nuna mata gata sosai a rayuwah.
   Gyan jiki kam kullum cikin yi mata ake, fatarta tayi kyau sosai sai santsi take, har wani ɗaukan ido take. Ta k'ara kyau fiye da daa, kamar ba Saudat ba.

   Sauran sati ɗaya biki su Yasseer suka sauka k'asar, motoci akayi da yawa zuwa tarbansu, banda Saude da Najib suna gida yana tayata aikin tarban babban ɗan Momie. Tana gyaran kitchen bayan ta gama, yana zaune ya kasa ɗauke kallonshi daga gareta.
     "kallonnan fa ya fara yawa Masoyi" ta ɗauka plate ta kare fuskarta.
   "idan ma na kalla ai MATATAH CE, nake kallo, ki barni in kalleki, hakanan yau naji inason inyi ta kallonki"
    "nidai banson kallo fa"
  "ni kuma inason inyi ta kallon fuskarki, bazan taɓa gajia da hakan ba" ya janye plate ɗin a hannunta, jin k'arar motocine ya sakashi fita daga kitchen ɗin, ta rakashi da murmushi.

   Ɗakinta ta koma, ta sake shek'a wani wankan, ta fito ta shirya cikin wani orange ɗin atamfa, mai zanen yellow da fari, tayi kyau sosai bama kaman data zuba ɗaurin ɗan kwalinta mai kyau, ba wani Make-up tayi ba, anma tayi kyau sosai.
   Ɗakin Momie ta wuce, Rabi'ah ce kawai, ta taso da fara'arta ta tarbeta, "Sai yanzu kike fitowa? Har ina shirin zuwa ɗakinki in fito dake"
    "waceni in saka matar yaya aiki? Sannunku da zuwa"
   "yauwah Amaryarmu, kinga yanda kika k'ara kyau kuwa? Dak'yarma na ganeki"
   "ballantana ku Aunty Rabi'ah dake k'asar waje"
   "nifa da gaske nake, yanzu dai sai mun zauna kafin hidimar bikinnan ta ida haye miki za'a k'ara koyamun wasu girke-girken"
    "tohm Aunty"
  Fira suka shigayi da Rabi'ah, da yake Momie bata ɗaki, tana shirin tambayar Rabi'ah Momie sai gashi ta shigo.

  Momie tace "yanzu na aika kiranki ashe kinanan"
    "sannunku da dawowa Momie"
   "yauwah sannunki da hidima"
   Sai ga Najib da Yasseer sun shigo a tare, suna dariyansu da alama cikin farin ciki suke, Najib yace "Saudat, yau dai ga babban Yayana Yasseer" ya juya kan Yasseer, "Broda, ga MATATAH, Saude na gaji da wannan saɓanin da kuke samu"
   Yasseer yace "A'a'tohh karma sai anyi auren mu haɗu a hanya bamusan juna ba" gaba ɗaya ɗakin saida sukai dariya, kowannensu ka kalla yana cikin farin ciki.
   Hakan ya sanya Saude ta jiyo cikin ladabi ta gaishe da Yasseer, wani irin shock yaji sauraren muryarta kawai tun basu haɗa ido ba, gaba ɗaya ya kasa buɗa baki ya amsa, jin yayi shiru ya sanyata ɗago kanta, su duka saida gabansu ya faɗi, da sauri ta ɗauke kanta.
    Shikam kasa ɗauke idanunshi yayi a kanta, kallonta kawai yake kaman babu kowa a wurin.

©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 67

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
             67

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    Kafinsu tashi barci, an gama haɗa musu break fast, daman da Momie zasu tafi sunsha rok'onsu su dawo nan su karya kumallo, sai gashi sun dawo tunda wuri, sabuwar tabarma aka shimfiɗama Momie ta zauna sannan aka jere mata kayan break fast kala-kala.
   Koko da k'osai, fura, ɗan wake, shinkafa da wake, alala,  sabon tuwo, da shayi ruwan bunu (marar madara), Momie dai sai godiya take, "wannan kalaci duk mu kaɗai? Ai daa baku wahalar da kanku da yawa haka ba"
   Gwaggo tace "haba Hajia, ai babu komi, so muke kici ki k'oshi,"
   Ɗan waken kawai taci, don Momie akwai son ɗan wake, ta kora da ruwan koko ko kaɗan bata nuna musu k'yamata ba, zama tayi taci kamar yanda zataci a gidanta, Saude ta ɗauka na Najib ta tafi kai mishi yana cikin mota ya kasa shiga.

Ta ajje mishi, suna gama gaisawa ta tashi zata tafi, ya rik'o hannunta
   "wannan kayan break fast ɗin duk ni dawa?"
       "kai da cikinka mana"
    "wasa kike, sai dai ni dake"
        "nawa yana ciki fa yanzu zanje inyi"
    "A'ah wannan ya ishemu" ta mak'ale kafaɗa, "shikenan kwashesu ki koma dasu"
   "rigima ko?"
  Ya kashe mata ido, "mijinki na sonki kusa dashi ne"
   Jiranshi dai tayi harya gama, don a waje suka shimfiɗa tabarma, duk da ba mutane anma saita kasaci, shima Fura kawai yasha, qila itama don a gabanta ne, don gaba ɗaya tsantsamin kwanukan yake da ruwan garin, yana sha yanajin tashin zuciya dak'yar dai yasha da yawa.

  Tana maida kwanukan, ta kwashi tsarabar Hanne k'awarta ta fito, tare da Najib suka jera suka tafi shima yanaso yaga k'auyen. Nan su Gwaggo suka shiga rabon tsaraba suma, don daɗi bakunansu har kusa da kunne, wai yau sune suke fantamawa haka duk sanadin Saude da suka tsana.
   Suna tafiya tana mishi bayanin k'auyen, duk inda sukayi ana nuna su 'ga Saude can tazo da bak'on ɗan birni, Saude ce tazo daga birni taa waye, Saudece ta zama er gayu' kowah dai da abunda yake faɗa.
    "mutanen garinku fa ke kaɗai suke kallo"
    "A'ah ai kaine bak'o a wurinsu"
   Dai dai gidan da suka zauna ita da Yasseer ta tsaya tana kallo, bazata taɓa mantawa da gidan ba, abubuwa da yawa a gidan da bazata iya mantawa dasu ba.
   A gidanne aka fara ajjeta a matsayin amarya, a gidanne ta zama cikakkiyar mace, a gidanne ta samu farin cikin da bazata taɓa mantawa ba, a a gidanne ta samu bak'in cikin da har yanzu yakenan mak'ale a ranta, a gidan ta samu cikin Hafsat kuma anan ta haifeta, bazata taɓa mantawa da gidannan ba.
    Zagayowa yayi saitin fuskarta, ya ɗan kaɗa mata yatsunshi guda biyu, firgigit ta dawo daga dogon tunanin data tafi, "sau nawa zan faɗa miki banson ganin wannan fuskar a tare dake?"
   Murmushi tayi, "idan hakan ya maka mu tafi ko?"
   "Yayi anma saikin faɗamun nan inane?"
   Hawayen data daɗe tana maidawa ne suka fara kwararo mata, girgiza mata kai yayi, yasa hannu yana share mata hawayen, kama hannunta yayi sukabar wurin,
    "ga gidan Hanne can"
       "tohm ki fito inanan ina jiranki, kuma bance kiyi sauri ba don kawai kin barni anan, zan jiraki ko yaushene"
  Murmushi tayi ta ansa ledar hannunshi. Hanne najin sallamarta da gudu ta fito ta tarbeta, har suna kusan faɗuwa.
    "sai yanzu zakizo tun jiya ake kawomun labarin Saude tazo garinnan"
  "kuma shine bakizo kin ganni ba? Wai jirama tukunna ya akai kika ganeni"
  "inafa na ganeki, yanda aketa kwatantamin kene dai"
  "wai kinga yanda kika koma kuwa? Lallai birni taa ansheki, wallahi Hajjaju komai naki ya canja fa" sai shafa jikin Saude take yanda yayi laushi tana ta surutu.
    "kemafa kin canja k'awatah, don dai bazan mantaki bane anma dak'yar na ganeki, kin zama wata babbar mace, haba duk ina gayun naki kike nema ki tsofe da wuri?"
   "Hmm Saude kenan" ta lura tana cikin matsala, kuma ita bamaison jin sirrin mata da miji bane, bazata manta taimakon da Hanne tayi mata ba, ta kawo tsarabarta ta bata, da kuɗi masu ɗan yawa tace tayi jari, godia sosai take mata har suka fito k'ofar gida.

  Wurare da yawa sukaje da Najib a k'auyen, daga k'arshe suka wuce rafi.
    "Gaskia yanayin garinnan naku da daɗi yake, bana gajia da shak'ar sanyayyar iskarnan"
    "saimu barka anan kayita zamanka ai"
   "bazan damu bafa, indai tare dake ne"
   "daman ai kawu yace indai zai baka aurena tohm sai dai mu zauna anan"
   "ke! A ina? Anma dai da wasa kike ko?"
  Babu alamun wasa a fuskanta tace "Da gaske nake mana"
   "abincin k'auyennan? In kwana cikin k'auye? Kawu ya taimakamun mana"
   Dariya tayi sosae, "Matsoraci, daman nasan duk faɗi ne kawai"
     "ba haka ba, nafison na ajeki inda zakiji daɗi ne"
   "daɗin baki ko?" ta faɗa tana dariya, sai dai taji tayi tuntuɓe har saida ta faɗa jikin Najib, da sauri ya rik'ota, ta dafe k'irjinta dake faɗuwa sannan ta tashi a jikinshi.
     Duk'awa yayi wurin k'afar tata, "Sannu, baki daiji ciwo ba ko?"
   "A'ah, bara dai a ɗauke dutsin saboda kar wani ya k'ara faɗuwa"
  Ta duk'a zata ɗauke, ya riga ya zauna wurin, kamar dutsin daya taɓa mata ciwo a k'afa sanda ta faɗo daga bishiya, da sauri ta ɗaga kanta sama, bishiyar mangwaronnan ce wacce ta faɗo daga samanta lokacin da zata ɗeboma su Kabiruwa.
    Juyawa tayi tana kallon Najib, ta k'ura mishi ido sosae ji take kamar Yasseer ne take gani, bazata manta da haɗuwarsu ta farko ba, duk abubuwan da suka faru jikin bishiyarne suke dawo mata a ranta.
    Gatanan Zaune lokacin da ake mata Kamu, tuna rik'on da Yasseer ya mata a lokacin tayi, saida duk tsikar jikinta ta tashi, gabanta ya faɗi taja wani ajiyar zuciya, maganarshi ce ta dawo mata a kunne kamar lokacin yake mata ita, lokacin data mishi godiyar taimakon daya mata.
    "ni nake da godia, da kika bani dama harna taimakeki, kuma na samu lada"
   Najib ne ya hure mata ido, "kamar dai yau kika fara ganina" lumshe ido tayi, kamar dai Yasseer a haɗuwarsu ta farko.
   Tana murmushi mai ɗauke da damuwa ta kalla bishiyar, "wannan ne dalilin haɗuwatah da mijina na farko, ananne na ganshi, kayi hak'uri anma bazan iya tsaida tunaninshi ba duk sanda nazo wurinnan"
    "Shi kike tunani, anma ni kike gani domin nine a gabanki yanzu, bazan hanaki tunawa dashi ba, don nasan idan kika sake dawowa, nida shine zakina tunawa"
    Ɗaga mishi kai tayi, "Allah yaji k'anshi, yakai haske a kabarinshi"
   "Ameen ta amsa tana murmushi"

  Sai kusan Azahar suka koma gidan, Momie na jiransu har tayi shirin tafiya, yanayinta kawai suka gani gaba ɗaya hanjin cikinsu suka kaɗa, bama kamar Saude da gabanta ya fara faɗuwa, shikenan kawu ya gama tona mata asiri.
    Najib ne ke mata magana a ruɗe, "Meke faruwa Momie? Don Allah karkicemun zan rasa Saudat" ganin yanda duk suka tada hankalinsu, Momie ta kasa rik'e dariyarta, sannan suka sauke ajiyar zuciya.
   "mun gama magana, kawunka ya yarda zai baka auren Saude, da munje kawunanka zasu zo a saka rana, saura ka bani goran Albishir" kafin Momie ta rufe baki ya zaro komai na aljihunshi ya aje a gabanta, saida ya jiyo dariyarsu Kawu ne, ya fita daga gidan a kunyace, donshi baimasan suna wurin ba.
   A ranar sukai bankwana suka koma, duk kuɗinta da Najib ke bata harma da wanda Momie ke bata, bata kashewa ta damk'ama Kawu yayi gyaran gida, har mota ya bisu yana godia, harda en k'wallansu shida Gwaggo.
   Gaba ɗaya kuɗi sun rufe mishi ido, yama manta da wani auren Saude da Yasseer, don daman shi baida wani matsala da aurenta.

   ©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 66

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
             66

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    A baya Saude ta zauna, ta koma can gefe ta rakuɓe tanata zullumi a ranta, yana drivin yana hangenta ta mirrow, k'arar shigowan message taji a wayanta, ta duba daga Najib ne.
        "Ya dai?" kallonshi tayi ta mirrow, ya ɗaga mata gira yana murmushi.
   "Meka gani?" ta mayar mishi.
  "Kinyi shiru kamar kina da damuwa, ko duk kunyar Momie ne?"
   Sai data murmusa data gama karantawa, sai ga wani text ɗin nashi ya k'ara shigowa, "wannan fuskar nakeson gani har muje, murmushi yafi miki kyau" dariya tayi kawai ta tsura mishi ido ta mirrow shima tana kallonshi, duk Momie na lura dasu, ciki-ciki take musu dariya.
  Mik'a hannu tayi ta anshe wayar tashi, "kana wannan gudun kuma bazaka maida hankali a tuk'i ba" da sauri yabi hannunta zai ansa wayan,
  "plz momie ba wani abu nake ba, lokaci nake dubawa"
   "kana duba na motan tohh"
Ta cikin mirrow ta mishi gwalo tana dariya, ya harareta da wasa, bata daina mishi dariyar ba.

  Kwata-kwata ta manta da Momie a wurin, ta kwanto jikin kujerar da yake, suna kallon juna ta cikin mudubin kowanne ya kasa ɗauke idonshi, sak'on soyayyar da suka kasa furtawa a baki saboda Momie na wurin ne suke aika ma juna ta kallo.
   Garin kallo sunje shiga wani gari, bai lura da bump ba ya faɗa mishi kawai, su duka saida suka razane banda Momie da daman tana sane dashi, ta wutsiyar ido yake kallonta, saida taga abun nasu bamai k'arewa bane, ta saka hannu ta juya mirrow ɗin, su duka har saurin kai hannu suke su gyara, saida Saude ta lura Momie ce ta koma a kunyace ta zauna.
    Saida suka isa garin Katsina suka tsaya sukayi Sallah, wani restaurant sukaje sukaci suka k'oshi, sannan suka kama hanyar k'auyensu Saude.
 
  Da yake akwai nisa daga katsinarma, saida suka k'arayin tafiya mai nisa sannan suka isa k'auyen, Najib dai bin k'auyukan wurin kawai yake da kallo, wai anan Saude tayi rayuwa, nan wurin  har akwai halittar dake rayuwa.
   Itama bin k'auyen kawai take da kallo, tayi kewarshi da yawa, shekara ɗaya da en watanni ko zagayoshi bata k'arayi ba, ba laifi k'auyensu an samu en canje-canje, anma bazata iya mantawa da k'auyenba, kai tsaye take nuna mishi hanyan gidan Kawu duk da k'auyen ba yawane dashi ba. Yananan inda yake, sai dai yaa k'ara lalacewa, ginin jar k'asar duk ya zaganye sai tsummuna ne aka ɗaure akayi kamar katangar dasu, suma duk sun ciccire, wurin dai babu kyaun gani, cikin zuciyarta tayi mutuk'ar tausaya musu,
   Momie tace ta shiga ta fara sanar musu zuwansu,ta buɗa motan ta fita, tana k'ara k'arema wurin kallo.

  Cikin gidanma duk ya lalace, k'asan tayi gamsa kuka da ciyayi ko ina, ɗaki ɗaya tal ya rage a gidan, shima rufin duk ya zazzare, tana daga bakin ƙofa sai rangaɗa sallama take babu alamun kowa a gidan, harta fara gajia, saiga Gwaggo ta fito daga bayan gida, can gefen ɗakin aka zagaye wani wuri shima da tsummokara, tana ganin Saude ta washe baki.
    "A'a'aah sannu da zuwa, sannu da zuwa" duk ta rasa inda zata sakata don murna, don ko kaɗan bata ganeta ba.
  Can gefe ta tillar da gwangwanin ruwan hannunta, ta shiga ɗaki ta ɗauko tabarma da tsintsiya, ta share wuri sannan ta shimfiɗa mata tabarmar ta zauna, ita dai Saude sai binta da murmushi take ganin yanda take ta zakwaɗi tasan lalle gwaggo bata gane ta ba.
   "daga ina? Halan bak'in gidan mai gari ne? Sannu fa kunsha hanya"
   "A'ah nan gidan nazo gwaggo"
   "Gwaggo kuma? Kai gaskia badai ni ba, bansan kowa a birni ba, ki dai tuna gidan da kike nema"
   "Gidan da nake nema nazo Gwaggo bilki, gidan Kawo Ado"
  "eeh gaskia gidanne kikazo" gwaggo ta faɗa cikin sanyin jiki tana ja da baya, "Allah yasa dai ba wani abunne kikazo dashi ba baiwar Allah"
   "ki kwantar da hankalinki Gwaggo, Alkhari kawai nazo dashi"
  "tohh wacece ke?"

  Kawu Ado ne ya shigo gidan har yana tuntuɓe, yake k'walama gwaggo kira, burki yaja a tsakar gidan ganinta da bak'uwar fuska. Shima dai washe bakin yayi suka gaisa da ita, sannan yaja gwaggo can gefe.
   "Ina Mak'era aka faɗamun bak'i sun tsaya da k'atuwar mota k'ofar gidannan, nama ɗauka matsiyacin yaronnan ne"
  "bashi bane, bak'uwa ce dai mukayi daga birni"
  "gidan mai gari tazo ko gidan sarkin noma?"
   "gidannan tace tana nema, anma dai bata faɗi daga inda tazo ba"
   "tohh fa, Allah yasa ba sace mana kawuna tazo cikin k'atuwar motarnan ba"
   Suka jiyo su duka sunason tambayarta, su duka sun k'ara tsufa, kawu Ado duk gashin jikinshi ya cika da furfura.
    "baiwar Allah daga ina? Kuma wa kikazo nema?" kawu Ado ya mata tambayar.
  Tana murmushi tace, "Kawu daman Saude...."

   "Sauden K'aniya, idan ma nemanta kikazo kinzo gidan da bazaki dace bane, tunda tsohin mijinta ya gudu ya barta itama ta gama gabanta, tun kafin magana tayi nisa tsakaninmu kibar gidannan kije can kici gaba da dubata gidan karuwai"
   Rumtse idonta tayi sosai maganar ta soketa
  Gwaggo ta tari numfashinshi, "Malam anyi haka?"
  Idonta a rufe, tanajin k'una a zuciyarta tace "Sauden ce kawu"
    "Saude?" suka maimaita a tare, ta ɗaga musu kai, kunya saita kama kawu ya fara kame-kame.
   "Saude kece kika zama haka? Kin tafi birni kin manta damu, munanan muna ta addu'ah Allah ya kawoki, yasa kina cikin k'oshin lafiya, ko bilki?"
   "eeh eeh mana"
      "Alhmdlh Saude ina kika shige haka? Don bamu muka haifeki ba shikenan kika manta damu, anma dai aimu muka rik'eki har girmanki"
   "eeh mana, baki kyautaba Saude kinbar iyayenki cikin fargaba, ni banmasan ta inda zan fara bayyana farin cikin dana shiga da ganinki ba" kawu ya k'arasa maganar yana sharar k'walla.
   "kuyi hak'uri kawu, nima kuna raina"
   Nan fa suka sanyata gaba, ganin yanda ta koma lallai tayi kuɗi tana cikin jin daɗi, sunma rasa inda zasu sakata.

Saida taga sun ɗan natsa, tace "bani kaɗai nazo ba, harda hajiar da nake gidanta, da kuma ɗanta, kuma dai da maganar da sukazo da ita"
    "tare kukazo kuma bazaki shigo dasu ba? Kai Saude kinanan dai da halinki na kawaici" kawu ya faɗa, harda dariya shinan ya faɗa abun kirki.
    "tohm malam a shigo dasu bara a musu shinfiɗa"
   Gwaggo ta kwaso wasu tabarmun ta shimfiɗa musu kafin ya shigo dasu, su Kawo har kyarmar jiki ake, da hannu bibbiyu suka tarbesu, aka shimfiɗesu saman tabarma.

  Gwaggi da kanta ta saka mayafi, bashin ruwan laida mai sanyi an sakashi a randa ta anso musu, ta kawo sannan suka shiga gaisawa, en k'auyen har an fara cika gidan suna murna Saude ta dawo, ta canja ta zama er gayu. Bata k'yamacesu ba ko kaɗan, ta shiga cikinsu suna ta labari, har dare suna tare. Najib dai fita yayi ya basu wuri bayan sun gama gaisawa.
   Da yake dare yayi, kuma babu wurin da zasu kwanta a gidan, sai suka koma cikin gari babu nisa da k'auyen, a can suka samu hotel zasu kwana, banda Saude, cewa tayi a gidansu zata kwana.
  Gatan da bata taɓa tunanin samu ba su kawo suke nuna mata, don gaba ɗaya fita sukai daga ɗakin sukace ta kwanta ita zasu kwana a waje, tace su barta ta kwana inda ta saba anma sukak'i, duk yanda taso, anma a ɗakin dai suka bar mata ta kwana ita kaɗai.
  Su Momie sun tafi a zuwan sai gobe zasu dawo ayi magana.

   ©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 65

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
            65

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Saudat ta gama jere ma Rabi'ah kayan ciye-ciye, Husna sai sannu take mata, sai gata ta dawo daga rakiyan Yasseer.
    "Sannunku da zuwa Aunty Rabi'ah" kallonta ta ɗanyi.
   "Saudat ko?" ta ɗaga mata kai tana murmushi, "Sannunki kinsha aiki, ya gajia?"
   "ai ba wani aiki bane"
Taje zata kama Husna dake k'ok'arin tashi dak'yar, "Sannu Aunty"
   "Yauwah Aunty Saudat"
  Rabi'ah tace "waih! Sannu kinji, gaskia kina k'ok'ari"
   "ai saima yazo kanki zaki sani" inji Husna.
   "ni? Allah ya rufamun asiri, wahalan ɗaukan ciki, haihuwa ga raino mutum ya tsofe tunda wuri"
   "Miye abun rufin Asiri? Kardai kicemun har yanzu kina da wannan Ra'ayin naki tun muna ckul, wollah garama ki canja kin sanmu dangin miji dai"
      "akwai hanyar samun yara da yawa ko ban haihu ba, yanzu dai a barni in gama cin amarcina  dan Allah ki dainamun maganarnan kina kadamun gaba"
   "Baki ma da hankali wallahi, wannan ba tunani mai kyau bane, inma bazaki haifa mana ba zamu auro mai haifa mana"

  Filon kujera ta ɗauka ta jefa mata, "bakinki ya faɗama mak'iyanki, kinsan Allah ko wata naji anyi ma kishia zuciyatah tafasa take" Husna daria kawai take mata, ta k'ara ɗaure fuska, "Allah wannan ba abun dariya bane"  bata saurareta ba, dariyarta kawai taci gaba dayi, yanda takeyi dariya take bata sosae.
   Da yake Saude da Najib suna waje, Rabiah da ɗan rage murya, "wai da gaske wannan ce Saudat ɗin Najib?"
    "itace mana"
  "daga ina ya samota?"
     "ɗiyar Momie ce, daga k'auye tazo"
   "lallai kice kyawawan en matah na k'auye, na birni kwalliya da wayewa zasu nuna musu kawai"
   "eeh mana, Yayanmu ma a can zamu samo mishi ta biyu"
   "Allah idan bazaki dainamun maganarnan ba yanzu zanbar miki gidanki"
  Ta rufe baki tana dariya, "yi hak'uri matar babban yaya, na daina"
    "karma ki daina ɗin"

  A gidan Husna Rabi'ah ta yini har dare, sai fira suke da Saudat kamar wanda suka saba, da yake taji ita Najib zai aura kuma dai yanzu bazata nuna mata wayewa ba, har abincikan data girka ta nemi ta koya mata, taji sun mata daɗi sosae, nan ta koya mata harma da wanda bata nema ba.
   Dare ya fara nisa Yasseer yazo ɗaukan Rabi'ah, bai shiga ciki ba yayi parking wajen gidan sannan ya mata waya ta fito, yana zaman jiranta a mota cikin duhun daren Saudat tazo wucewa, cikin tafiyarta ta nutsuwa a hankali take saka k'afafunta, ta amso ma Husna sak'o mak'waftansu.
   Hakanan yaji yanason ganin fuskar kowacece, ya bita da kallo cikin duhun darennan har lek'enta yake gashi ta juya baya, Rabi'ah na tsaye ta fito ga mota a kulle, sai k'wank'wasawa take baimasan da ita a wurin ba, gaba ɗaya taa gama k'ulewa. Saida ta dawo ta gabanshi sannan ya lura ya buɗe mata.
  A harzuk'e ta shiga ta zauna sai maida numfashi take, juyawa tayi ta fara dukan k'irjinshi, "matah kake kallo ko, bakama lura ina tsaye ba" rik'e hannuwanta yayi sai k'ok'arin k'wacewa take.
   "Waya faɗa miki mata nake kallo? Nifa ginin unguwarne suka burgeni, nake tunanin ko nan zamu gina gida idan mun dawo?"
  "mak'aryaci, wallahi saika faɗamun ko wacece kake kallo"
     "wa kikaga ina kallo nifa banmasan da wata mace a wurin ba"
    "k'arya kake" ta k'wace hannuwanta taci gaba da dukanshi, duk ta hargitsa mishi tunani cikin motar dak'yar ya iya rik'eta, gam ya haɗata da k'irjinshi yana sumbatarta, bai saketa ba saida ta nutsu sannan, saida ta k'ara kai mishi duka a k'irji tana harara sannan ta gyara zama tana maida numfashi.

   Kwana ɗaya suka k'ara, suka ɗaga moscow bayan Momie ta mishi gargaɗin ya daina daɗewa bai dawo ba,
    Ranar da suka tafi, da yamma a ranar  Husna ta haifi jaririyarta mace, ba k'aramin murna sukai da zuwanta ba, sai Saudat hidima ta k'aru, har ranar suna itace mai hidima da bak'i  ko kaɗan bata nuna gajiyawarta, yarinya taci suna Maheera, kamar Najib na jira, washe garin suna yazo ya koma da ita, aka samo mata mai kula da ita da jaririn.
   Ranar Monday ta koma makaranta SS1, gaba ɗaya hankalinta ta maidashi akan karatunta, soyayyarta da zuciyarta kuma duk ta mik'asu wurin Najib.

A moscow, tun komawar Yasseer abubuwa suka dawo mishi sabo, gaba ɗaya yanzu addu'anshi daya ɗaga hannu Allah ya nuna mishi Saude, yasan yaa cutar da rayuwarta kullum cikin nadama yake, so yake su haɗu kota yafe mishi laifin daya mata, gaba ɗaya ko wurin aiki baida sukunin yin komai, a gida ma yafison ya zauna shi kaɗai yana tunanin rayuwarsu ta baya, tohh idan Saude bata k'auyensu tana ina? Kullum tambayar da yake ma kanshi kenan.
    Rabi'ah ta shigo ɗakin da wata irin shiga mai jan hankali, a kusa dashi tayima kanta masauki, ta saka hannu ta shafi fuskarshi cikin shauk'i.
    "Yauma tunanin kake? Banson ganinka cikin damuwa, kuma kak'i faɗamun damuwarka"
   "Rabi'ah plz, inason hutu" ya faɗa idanunshi a rufe da alama damuwan ta fara fin k'arfinshi.
   "Yaushene ka fara korata a ɗakinka? Nifa damuwarka kawai na tambaya, ka faɗamin ko miye saimu zauna mu tattauna"
    "babu abunda ke damuna, don Allah ki k'yaleni hakanan"
   "bazan tafi ba, saika...."
  Wani irin tsawa ya daka mata, "kece damuwatah! Ki fita na..." yanda ta zabura ya sanyashi shiru duk baiji daɗi ba, gaba ɗaya tunanin Saude ya fara zautashi.
   Hannuwanta ya kamo ya rik'e, "don Allah Rabi'ah, ina cikin damuwa ki barni in samu kaɗaicewa kona ɗan lokaci ne" duka takai mishi, sannan ta mik'e ta fice daga ɗakin, binta yayi da kallo, ita dai dukan miji bai mata wahala, daya ɓata mata rai sai duka, Allah sarki Saude da ko magana yake mata kanta na a k'asa take saurarenshi.

    Su Saude suna samun hutu Momie ta fidda ranar zuwa k'auyensu, Najib kamar ya jawo ranar yakeji, gani yake kamar anma riga da an bashi Sauden.
    Daren ranar suna zaune a falo kamar kullum suna fira, kallon Ball yake taa biye mishi itama tana tayashi, gaba ɗaya hankalinshi na wurin.
   "wai nida ball ɗinnan waka fiso?"
  Aje remote yayi ya maida hankalinshi kanta, "karki k'ara haɗamun soyayyatah da wani abu, nafi sonki fiye da yanda nakeson kaina ma"
     "luv uh as much dear, in hakane meyasa ka k'yaleni"
    "farin ciki nakeji Saudat, wanda ban taɓayi ba, gobe zamuje k'auyenku kawu ya bani aurenki, idan harya bani ke babu sauran abunda zai min shamaki da mallakarki"
    "ka ɗauka ma ya baka fa"
 
   Fargaba ce kawai a ran Saude daren ranar, batasan yanda kawu zai amsa maganarta da Najib ba, tasan ya tsaneta komai zai iyayi don ya k'untata mata, kuskurenta tun farko data faɗa mishi Yasseer bai saketa ba ya gudu.
   Ranar batayi barcin kirki ba, cike take da fargabar yanda gobe zatazo mata. Barci bai daɗe da ɗaukarta ba aka kira Sallah, a kasalance ta tashi tayi Sallah, ta jawo Qur'an ɗinta ta fara karatu, tana gamawa dai Addu'anta kawai Allah yasa komai yazo musu da sauk'i wurin kawu.
   Bata samu komawa barci ba, Momie ta aiko mata ta fito idan taa shirya don safko zasuyi, Najib ne zai kaisu ita da Momie, da wuri suka kama hanya zuwa k'auyensu Saude.

©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 65

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
            65

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Saudat ta gama jere ma Rabi'ah kayan ciye-ciye, Husna sai sannu take mata, sai gata ta dawo daga rakiyan Yasseer.
    "Sannunku da zuwa Aunty Rabi'ah" kallonta ta ɗanyi.
   "Saudat ko?" ta ɗaga mata kai tana murmushi, "Sannunki kinsha aiki, ya gajia?"
   "ai ba wani aiki bane"
Taje zata kama Husna dake k'ok'arin tashi dak'yar, "Sannu Aunty"
   "Yauwah Aunty Saudat"
  Rabi'ah tace "waih! Sannu kinji, gaskia kina k'ok'ari"
   "ai saima yazo kanki zaki sani" inji Husna.
   "ni? Allah ya rufamun asiri, wahalan ɗaukan ciki, haihuwa ga raino mutum ya tsofe tunda wuri"
   "Miye abun rufin Asiri? Kardai kicemun har yanzu kina da wannan Ra'ayin naki tun muna ckul, wollah garama ki canja kin sanmu dangin miji dai"
      "akwai hanyar samun yara da yawa ko ban haihu ba, yanzu dai a barni in gama cin amarcina  dan Allah ki dainamun maganarnan kina kadamun gaba"
   "Baki ma da hankali wallahi, wannan ba tunani mai kyau bane, inma bazaki haifa mana ba zamu auro mai haifa mana"

  Filon kujera ta ɗauka ta jefa mata, "bakinki ya faɗama mak'iyanki, kinsan Allah ko wata naji anyi ma kishia zuciyatah tafasa take" Husna daria kawai take mata, ta k'ara ɗaure fuska, "Allah wannan ba abun dariya bane"  bata saurareta ba, dariyarta kawai taci gaba dayi, yanda takeyi dariya take bata sosae.
   Da yake Saude da Najib suna waje, Rabiah da ɗan rage murya, "wai da gaske wannan ce Saudat ɗin Najib?"
    "itace mana"
  "daga ina ya samota?"
     "ɗiyar Momie ce, daga k'auye tazo"
   "lallai kice kyawawan en matah na k'auye, na birni kwalliya da wayewa zasu nuna musu kawai"
   "eeh mana, Yayanmu ma a can zamu samo mishi ta biyu"
   "Allah idan bazaki dainamun maganarnan ba yanzu zanbar miki gidanki"
  Ta rufe baki tana dariya, "yi hak'uri matar babban yaya, na daina"
    "karma ki daina ɗin"

  A gidan Husna Rabi'ah ta yini har dare, sai fira suke da Saudat kamar wanda suka saba, da yake taji ita Najib zai aura kuma dai yanzu bazata nuna mata wayewa ba, har abincikan data girka ta nemi ta koya mata, taji sun mata daɗi sosae, nan ta koya mata harma da wanda bata nema ba.
   Dare ya fara nisa Yasseer yazo ɗaukan Rabi'ah, bai shiga ciki ba yayi parking wajen gidan sannan ya mata waya ta fito, yana zaman jiranta a mota cikin duhun daren Saudat tazo wucewa, cikin tafiyarta ta nutsuwa a hankali take saka k'afafunta, ta amso ma Husna sak'o mak'waftansu.
   Hakanan yaji yanason ganin fuskar kowacece, ya bita da kallo cikin duhun darennan har lek'enta yake gashi ta juya baya, Rabi'ah na tsaye ta fito ga mota a kulle, sai k'wank'wasawa take baimasan da ita a wurin ba, gaba ɗaya taa gama k'ulewa. Saida ta dawo ta gabanshi sannan ya lura ya buɗe mata.
  A harzuk'e ta shiga ta zauna sai maida numfashi take, juyawa tayi ta fara dukan k'irjinshi, "matah kake kallo ko, bakama lura ina tsaye ba" rik'e hannuwanta yayi sai k'ok'arin k'wacewa take.
   "Waya faɗa miki mata nake kallo? Nifa ginin unguwarne suka burgeni, nake tunanin ko nan zamu gina gida idan mun dawo?"
  "mak'aryaci, wallahi saika faɗamun ko wacece kake kallo"
     "wa kikaga ina kallo nifa banmasan da wata mace a wurin ba"
    "k'arya kake" ta k'wace hannuwanta taci gaba da dukanshi, duk ta hargitsa mishi tunani cikin motar dak'yar ya iya rik'eta, gam ya haɗata da k'irjinshi yana sumbatarta, bai saketa ba saida ta nutsu sannan, saida ta k'ara kai mishi duka a k'irji tana harara sannan ta gyara zama tana maida numfashi.

   Kwana ɗaya suka k'ara, suka ɗaga moscow bayan Momie ta mishi gargaɗin ya daina daɗewa bai dawo ba,
    Ranar da suka tafi, da yamma a ranar  Husna ta haifi jaririyarta mace, ba k'aramin murna sukai da zuwanta ba, sai Saudat hidima ta k'aru, har ranar suna itace mai hidima da bak'i  ko kaɗan bata nuna gajiyawarta, yarinya taci suna Maheera, kamar Najib na jira, washe garin suna yazo ya koma da ita, aka samo mata mai kula da ita da jaririn.
   Ranar Monday ta koma makaranta SS1, gaba ɗaya hankalinta ta maidashi akan karatunta, soyayyarta da zuciyarta kuma duk ta mik'asu wurin Najib.

A moscow, tun komawar Yasseer abubuwa suka dawo mishi sabo, gaba ɗaya yanzu addu'anshi daya ɗaga hannu Allah ya nuna mishi Saude, yasan yaa cutar da rayuwarta kullum cikin nadama yake, so yake su haɗu kota yafe mishi laifin daya mata, gaba ɗaya ko wurin aiki baida sukunin yin komai, a gida ma yafison ya zauna shi kaɗai yana tunanin rayuwarsu ta baya, tohh idan Saude bata k'auyensu tana ina? Kullum tambayar da yake ma kanshi kenan.
    Rabi'ah ta shigo ɗakin da wata irin shiga mai jan hankali, a kusa dashi tayima kanta masauki, ta saka hannu ta shafi fuskarshi cikin shauk'i.
    "Yauma tunanin kake? Banson ganinka cikin damuwa, kuma kak'i faɗamun damuwarka"
   "Rabi'ah plz, inason hutu" ya faɗa idanunshi a rufe da alama damuwan ta fara fin k'arfinshi.
   "Yaushene ka fara korata a ɗakinka? Nifa damuwarka kawai na tambaya, ka faɗamin ko miye saimu zauna mu tattauna"
    "babu abunda ke damuna, don Allah ki k'yaleni hakanan"
   "bazan tafi ba, saika...."
  Wani irin tsawa ya daka mata, "kece damuwatah! Ki fita na..." yanda ta zabura ya sanyashi shiru duk baiji daɗi ba, gaba ɗaya tunanin Saude ya fara zautashi.
   Hannuwanta ya kamo ya rik'e, "don Allah Rabi'ah, ina cikin damuwa ki barni in samu kaɗaicewa kona ɗan lokaci ne" duka takai mishi, sannan ta mik'e ta fice daga ɗakin, binta yayi da kallo, ita dai dukan miji bai mata wahala, daya ɓata mata rai sai duka, Allah sarki Saude da ko magana yake mata kanta na a k'asa take saurarenshi.

    Su Saude suna samun hutu Momie ta fidda ranar zuwa k'auyensu, Najib kamar ya jawo ranar yakeji, gani yake kamar anma riga da an bashi Sauden.
    Daren ranar suna zaune a falo kamar kullum suna fira, kallon Ball yake taa biye mishi itama tana tayashi, gaba ɗaya hankalinshi na wurin.
   "wai nida ball ɗinnan waka fiso?"
  Aje remote yayi ya maida hankalinshi kanta, "karki k'ara haɗamun soyayyatah da wani abu, nafi sonki fiye da yanda nakeson kaina ma"
     "luv uh as much dear, in hakane meyasa ka k'yaleni"
    "farin ciki nakeji Saudat, wanda ban taɓayi ba, gobe zamuje k'auyenku kawu ya bani aurenki, idan harya bani ke babu sauran abunda zai min shamaki da mallakarki"
    "ka ɗauka ma ya baka fa"
 
   Fargaba ce kawai a ran Saude daren ranar, batasan yanda kawu zai amsa maganarta da Najib ba, tasan ya tsaneta komai zai iyayi don ya k'untata mata, kuskurenta tun farko data faɗa mishi Yasseer bai saketa ba ya gudu.
   Ranar batayi barcin kirki ba, cike take da fargabar yanda gobe zatazo mata. Barci bai daɗe da ɗaukarta ba aka kira Sallah, a kasalance ta tashi tayi Sallah, ta jawo Qur'an ɗinta ta fara karatu, tana gamawa dai Addu'anta kawai Allah yasa komai yazo musu da sauk'i wurin kawu.
   Bata samu komawa barci ba, Momie ta aiko mata ta fito idan taa shirya don safko zasuyi, Najib ne zai kaisu ita da Momie, da wuri suka kama hanya zuwa k'auyensu Saude.

©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 64

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
              64

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Yasseer ya mik'a hannu zai amsa wayan kenan kiran Saude ya shigo a wayan Najib, murmushi yayi,
    "Halan ita ke maka waya?"
        "itace fa, Bara inje in amsa"
  "ai naga alama kam tunda kake murna, wani lokacin naga hotan"
   "tohm shknan bruz"
Falo Najib ya koma ya amsa kiran Saude, kusan raba dare sukai suna waya, lokacinda ya koma d'aki Yasseer har yayi barci, tunda safe kuma ya wuce k'yauyensu Saude.
   Tafiya mai nisa sosae yayi kafin ya isa k'yauyen, yasha bak'ar wahala sosai ga gajia da zaman mota, dak'yar ya iya gano gidansu Saude inda su kawu Ado suke, a waje ya tsaya aka mishi sallama dashi.
  Saiga Kawu ya fito yana washe baki, da sauri ya koma kawo mishi tabarma a soro ya shimfid'a mishi, sannan suka gaisa.
    "Sannu fa da zuwa Yaro"
        "Yauwah baba, baka ganeni ba ko?"
    "eeh tohh gaskia bangane ba"
  "Yasseer ne mijin Saude" ya fad'a yana sunne kai. Nan take Kawu Ado ya d'aure fuska.
    "toh toh, toh naji sai akai yaya?"
   "daman zuwa nayi inji kota dawo ko kuma an samu labarin inda take"
   "babu abunda ya shafemu da Saude da labarinta, tunda muka baka aurenta muka gama fita sha'aninta, yanzu wama yasan inda take? Oho! K'ilama tana can yawon karuwanci, ko kuma namun daji sun cinye namanta!"
   Cikin k'ara Yasseer yayi magana har saida ya tsorata kawu, "na rok'eka kawu karka danganta Saude da wannan maganganun naka"
   Kallonshi kawu yayi yana tab'e fuska, "da rayuwar Saude, da mutuwarta bata da wani banbanci a wurinmu, karka k'ara zo mana da maganar Saude, bamusan inda take ba, itama in tana da sauran hankali bazata nememu ba, don bazamu tab'a sonta ba"
    "zan koma, anma don Allah idanta dawo a sanar dani"
   Juya mishi baya kawu yayi bai k'ara cewa komi ba, ya zaro kud'i Aljihunshi masu yawa ya mik'a mishi, hannu ya zuro ya warce kamar yana tsoran karya maida, haka ko godia bai mishi ba harya tafi.

   En k'auyen ya shiga tambaga ko akwai wanda yasan inda Saude take, anma babu wani labari mai dad'i, gashi baba Haja bata cika zama k'yauyen ba daman babu wanda yasan takai Saude birni, har dare yana yawo k'auyen babu wani nasara.
   Duk ya gaji ga yunwa da kishirwa, sai da duhu yayi sannan ya hak'ura ya koma cikin gari, wani d'an k'aramin hotel ya kama ya kwana, washe gari ma ya koma k'auyen, babu dai labarin Saude haka ya hak'ura ya koma Abuja.

  Cikin wani irin yanayi ya isa gidansu, d'aga k'afa kawai yake anma baisan inda yake sakata ba, cikin sa'a babu kowa a falon, kai tsaye d'akinsu kawai ya wuce, kamar yanda ya zata Najib bainan, ya fad'a saman gado kawai dafe da kanshi.   Momie taji shigowarshi anma shiru bata ganshi ba, duk ta damu ta ganshi daman, kuma tunda taji shiru tasan ba lafiya ba, ta tashi ta nufi d'akin nasu.
   Yana zaune ya had'a kai da gwiwa, sautin shesshek'ar kukanshi ne kawai ke tashi, ta tsaya bak'in k'ofa tana kallonshi cikin mamaki da tashin hankali, kuka yake sosae yana dukan kanshi kamar wanda yaji sak'on mutuwa, a rikice Momie ta k'arasa shiga falon ta rirrik'e mishi hannuwa.
    "ki barni Momie, ki barni don Allah in hukunta kaina akan laifin dana aikata da har yanzu nake biyan bashinshi, qila hakan zaisa na rage zugin da zuciyatah kemun, Momie na aikata laifi, wallahi na aikata babban laifi a rayuwatah" ya k'arasa maganar yana fashewa da wani kukan.
    "Subhanallahi! Yasseer wane irin laifi ne wannan dake ma farin cikinka katsalandan? Fad'amun wanne irin laifi ne wannan da har ya sakaka zubda hawaye haka"
    "Bazan iya ba Momie, lokaci ya riga ya k'uremun, yanzu fad'a mikin baida wani amfani"
   "nifa mahaifiyarka ce, kana da wacce ta fini ne?"
   "babu Momie, shiyasa nakeso ki tayani da addu'ah, don Allah karki matsa saikinsan abunda ke damuna"
   "tohh shikenan, Allah ya yaye maka"
   "Ameen Momie, kaina ciwo yakemun sosai, jikina ko ina zafi, na rasa inda zan saka raina"
   "ka sauk'ak'a zuciyarka Yasseer, komai yayi zafi, ka dage da Addu'ah, bara inma Najib waya yazo muje Asibiti"
   "A'ah zanji sauk'i Insha Allah Momie basai munje ba"
   "Tohh kasha magani dai, saika kwanta ka huta, zuwa anjima in bai bari ba sai muje asibitin"
   "tohm Momie" dak'yar yake magana, hawaye kawai ke fita a fuskarshi, saida ta tabbatar ta d'an kwantar mishi da hankali sannan ta fita ta barshi.

    Tana fitowa saiga Najib da Saudat sun shigo, sun dawo daga wurin k'unshi da gyaran gashi, ta taresu tanama Saude sannu da zuwa, har k'asa ta gaishe da Momie.
    "Ya gajiyan hidima, ya Auntynki?"
   "lafiya lau take, tace a gaisheku" taci gaba da wasa da yatsunta su duka sunyi shiru, sai Najib ne ya fad'ama "wai sannu da zuwa mukazo tayima bruz, munyi waya dashi yace yana hanya"
    "Ayyah! Aikam bai dad'e da dawowa ba, baijin dad'i ya d'an kwanta ya huta"
    "Allah sarki, Allah ya sauwak'e"
     "Ameen"
   Tsarabar Husna ta had'a mata, da kuma nata duk da bada sunanta aka siyo ba, tayi godia sosae, basu dad'e ba suka tafi don zata fara aiki, gashi daren Sallah, Momie tana ta sa mata albarka.
    Suna fita Yasseer ya fito da shirin zuwa Masallaci, jikinshi duk ba k'wari daka ganshi yana cikin damuwa.

Bayan Sallah da kwana biyu, Yasseer da Rabiah sukaje gidan Husna bankwana sun kusa komawa, tunda yazo bai ganta ba ko sallah bata iya zuwa gida ba, kamar tayi me don murna da ganinshi.
   Saude na kitchen ita da Najib, don har gidan Husna ma ko yaushe suna tare, cewa yake bai damu gidan k'anwarshi bane, ko ina yake Saudat kawai yake gani, kuma bazaiso tasha wahala ba.
   Yana jinsu ya fita falon, suka fara mishi tsiyar yanzu har aiki yakema Husna kawai don Saude na gidan.
   "ai ba don ita nake ba, Saudat nake tayawa, idan kuma aka matsa in d'auke matata mu tafi"
    Rabi'ah tace "lallai mai Matah"
   "eeh Aunty MATATAH CE Saudat, laifine don na fad'i?"
   "A'ah mamakin yanda so ya canjaka nake, kamar ba Yaya Najib d'in da ko Motsa baki wahala yake mishi ba"
   "Da kenan Matar Yayanmu"
   Husna tace "Ai kad'an kikaji indai labarin soyayyar Najib da Saudat ne"
   Yasseer na gefe sai faman duba Agogo yake, ta rik'o hannunshi, "badai tafiya ba?" ya d'aga mata kai, "kinsan dai sauri nake" a gabansu ta marairaice fuska kamar zata fad'a mishi, "nidai ka bari muyi yinin tare, saimu tafi"
  "Zan dawo d'aukarki, nima ban gama gaisawa da sista ba"

  Husna tace "Munata fira ma Yayanmu ko ruwa bakasha ba, bara a kawo muku" ta k'wala ma Saude kira, "Aunty Saudat, a kawoma su Yayanmu drinks" Najib ya mik'e, "yanzu wannan d'inma ita zaki saka?"
     "Nikam dai Allah ya bani lafiya in huta da fad'a, ni don su gaisa da Yayan ma nasan itama har yau basu had'u ba"
   A hanyar fitowa suka had'u da Saude, ya ansa na hannunta sannan ya juya yakai musu, ruwan roba kawai Yasseer ya d'auka, "ba'a k'inshan ruwan zumunci anma a k'oshe nake"
    "Ai nasan Auntyna bata wasa da bama Yayana Abinci"
   "kamar tafiya zakayi, ka jira Saudat tazo ku gaisa plz"
  "Sauri nake, idanna dawo ma gaisa" suka fita da Najib ya rakashi, yana fita Saudat ta fito da kulolin Abinci.

©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 63

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
             63

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
      Labari        
               Ililee...  

www.babymsh.blogspot.com

   Saude na zaune gefen Momie bayan ta aika kiranta, saiga Najib ya shigo yana fad'a mata su Yasseer sun sauka yanzu zaije ya d'aukoshi, tsayar dashi tayi.
   "da yanzu zan tura Saude gidan Husna da driver, anma tunda zaka fita saika wuce da ita, anma ka hanzarta tana jira"
    "Gidan Husna kuma? Me zatayi?" ya tambaya Momie cikin mamaki.
   "Wai aikin azumi ta fara, taa kasa k'arasawa kaasan yanzu tayi nauyi (cikinta ya tsufa) shine zataje ta dinga tayata"
   "kuma sai Saudat d'inne zata tayata dole?"
   "kasanta dai batason er aiki, shiyasa ta nema taimakon k'anwarta, sauri fa zakayi taa cemun girkinta nakan wuta" ya k'ara b'ata rai duk baiso ba, "yaushene zata dawo?"
    "idan ta haihu mana, nikam Daddy bansanka da haka ba"
   "ai dole in damu Momie, tunda zatayi nesa dani"

  Kunya ya bama Saude ta mik'e, "bara inje in had'a kayan dazan tafi dasu,
Momie ta tsayar da ita, "Daddy zai kai miki daga baya, ki d'auko mayafinki dai"
    "tohh" ta tashi ta tafi, ba don yaso ba ya hak'ura ta koma gidan Husna.
  A hanya suna tafiya duk sunyi shiru, ta d'an karkad'a mishi yatsunta biyu ya jiyo.
    "wai bazakace komai ba?"
  "Nama rasa mezance Masoyiya, tunaninah kawai yanda zanyi rayuwa koda na rabin awa ne baki a kusa dani"
       "kana magana kamar wacce zata bar garin ko zata maka nisa, nasan ai duk inda nake zaka kasance tare dani"
   "Hakane fa, don yanzu zama gidan Husna ya kamamu" dariya tayi, ta bud'a baki zatayi magana dai dai lokacin sun isa gidan, ya shiga da motan yayi parking harta bud'e zata fita ya kalleta.
    "Sai sauri kike ki barni ko" da sauri ta d'aura hannunta saman leb'enta.
    "babu wannan kalmar tsakanina dakai, ni taka ce, bazan tab'a barinka ba"
   Murmushi yayi "nima duk da wasa nake miki, anma saida harshena yayi nauyin fad'a"
   "Yayanmu fa yana jiranka a airpot, kayi sauri plz"
   "Aww! Nifa ina tare dake mantawa da komai nake, saina dawo" tana murmushi take d'aga mishi hannu harya fice sannan ta shiga gidan.

  Tayi sallama sannan ta shiga gidan, Husna na zaune falo ta baje da gani ta tara gajia, ta amsa sallamar Saude.
    "Sannu Aunty Husna"
  "Yauwah Aunty Saudat" ta fad'a tana tsokanarta.
   "yau dai zan saka Matar yaya aiki"
   "Aunty Husna zolaya ko? Yanzu dai dame zan fara? Lokaci ya kusa"
    "komai yananan kitchen na fara na kasa k'arasawa"
   "Tohh Aunty bara inje" tana tafiya hanyar kitchen d'in Husna ta mata magana da d'an k'arfi yanda zataji.
   "Yaya Yasseer ya dawo kuwa?" saida gabanta ya buga yanda takeji kullum aka ambaci sunanshi.
     "A'ah yanzu dai yaa tafi ya d'aukoshi"
  "Wlhy naso aje tarbansu dani, anma dai duk jikina ba dad'i nakeji"
       "Ayyah! Aikam yaronnan yazo duniya fad'a zanyi dashi tunda yana takura Auntyna"
   "tohh bara Abbanshi yazo in fad'a mishi" tana dariya ta k'arasa shiga kitchen d'in, "ba ruwana fa wasa nake" itama Husna dariyan take. Ta shige kitchen ta fara aiki, ba wani mai yawa bane, kafin a kira Sallah taa kammala komai, ta wuce d'akin da Husna ta nuna mata ta zauna.

   Kamar ba abunda ya faru, Momie ta tarbi su Yasseer hannu biyu sai nan-nan take dasu, Rabi'ah sai wannan shisshigema Momie take ita mai suruku, sunje bud'a bakima a kusa da ita ta zauna sai fira take mata kamar ba surukarta ba ko er kunyarnan babu. Shidai Yasseer sai d'ari-d'ari yake don yasan ya b'ata ma Momie rai da yawa, sai da ta koma d'akinta yaje ya sameta jikinshi a sanyaye, ya d'uka saman gwiwoyinshi kamar zaiyi kuka.
     "Na sani ni mai laifi ne, kuyi hak'uri Momie hakan bazata sake faruwa ba, don Allah karkiyi fushi da d'anki"
   "Kaga alaman ina Fushi dakai? Damuwata na rashin zuwanka gidane daman, tunda na ganka kuma sai hankalina ya kwanta, ai babu wata uwa dake fushi da d'anta" rarrafawa yayi kusa da ita cikin farin ciki ya kwantar da kanshi saman cinyarta, "Hakan bazata k'ara faruwa ba insha Allah, nagode Momie"  murmushi tayi tana shafar kanshi kamar k'aramin yaro. Magana takeson mishi akan jikokinta da bataga alamansu ba, anma taa rasa ta inda zata fara mishi.
   Rabi'ah ce ta shigo d'akin,
      "Momie ya zaki barshi kamar k'aramun yaro? Kaifa nake jira hniee"
   "Ki barni inji d'umin mahaifiyatah mana, yaushe rabon da in ganta?"
   "Oh! Tohm ai bakai kad'ai keda ita ba, nima Momien tawace" ta k'arasa shigowa d'akin itama zata kwanta cinyar Momie tana musu dariya tace "Maza dai ku k'arasa er tsohuwar tun kafin jikokina suzo", cak Rabi'ah ta tsaya duk ta b'ata rai, ta d'auka wayarta dake gefen Gadon Momie.
    "Yanzu zan wuce gida Momie, sai Allah ya kaimu"
  Baki bud'e Momie ta bita da Kallo, "Allah ya kaimu" Yasseer ya mik'e da sauri, "Bara inje in kaita Momie" sai kuma ya lura da yanayin da take ciki.
    "nima haka nake fama da ita Momie duk sanda na mata maganar haihuwa" kad'a kai kawai Momie tayi, har suka tafi.

  A tsakiyar falo suka had'u da Najib ya sab'a Hafsat a kafad'arshi,
    "broda sai ina?" ya juyo muryar Yasseer ya tsaya sannan ya juyo, "Gidan Husna zanje"
   "Daa kuwa aron Motarka nakeso zankai Rabi'ah gida"
       "tohh ai sai in d'auka wata" yana zaro mishi mukullan a aljihu, ya saka hannu ya shafi fuskar Hafsat.
   "Ina kuma ka samu kyakkyawar babynnan?" da sauri ta fizge fuskarta daga hannun Yasseer,
    Murmushi yayi da wasa Najib yace "Tawah ce".
   "aifa da shekarun da nayi bananan sunkai shekarunta a duniya, tohm bazanyi tantama ba don kuwa komai naka ta d'auko" inji Yasseer
   Najib yace "haka aketa cewa yanayinmu d'aya, shiyasa nakeji da d'iyar Momien nan, Hafsat bazaki gaida Uncle ba?"
   Zumb'ura baki tayi ta kauda fuska gefe kamar ta sanshi, "Sunan Momie kuma kuke kiranta dashi ko sayawa bakuyi?"
   "ai Momie ta hana a b'oye sunan"
   "Mai kyau da ita, Inama kuka samota?" Najib ya bud'a baki zai bashi amsa suka jiyo muryan Rabi'ah, "Hniee kaifa nake jira" ya juya zai tafi kuma ya dawo ya mik'a mata hannu.
   "Hafsat zaki rakani?" mak'ale kafad'a tayi,  Najib yace "anma dai nayi Mamaki, Hafsat bata tab'a yima wani haka ba, akwaita da sakin jiki da Mutane"
   "aini bak'one a gareta, zamu saba ko Hafsat? Hakanan ina son yarinyar sosae"
      "ai haka take da saurin shiga rai" ya juya ya tafi. Shima wasu mukullan ya d'auko sannan suka fito, cikin irin fushinta na yara ta cema Najib, "ka fad'a mishi karya k'ara tab'ani"
  Cikin mamaki yace "Sabodame Hafsat?" shiru ta mishi, har sukaje gidan yanata tambayarta tak'i ta amsa, ya k'yaleta kawai sannan ta saki jikinta. Can ta wuce cikin gidan wurinsu Husna da yake ta saba dasu sosae, har so suke tazo musu yini, Masoyan biyu kuma suna can waje ta musu shimfid'a suna fira.

   Sai da dare yayi sosai basuma sani ba, har Hafsat tayi barci, sannan sukai sallama zai tafi ya ciro sabuwar waya a kwalinta ya mik'a mata, ta amsa tana murna ta bud'a, Iphone7 ce komai irin tashi, sai murna take.
   "ni banmasan ta inda zan fara nuna maka farin cikina ba, babu abinda zan biyaka dashi da soyayyar da kake nunamin"
       "ai kin riga da kin gamamin komai tunda kika mallakamun soyayyarki, kici gaba damun Addu'ah karna rasaki Saudat"
   "bazaka rasani ba, ka kwantar da hankalinka Saudat takace"
   "zai kwanta dai, anma sai sanda kika k'arasa zama tawa d'in" murmushi tayi, "ka d'aukama na zama" ta ciro wayan daga kwalinta, a kunne take da simcard d'inta,
     "Allah yasa dai ka faramun saving numberka, don ita zan fara sakawa"
   "Abunda na fara yi kenan ranki shi dad'e"
   "gaskia nagode sosai dear" harararta yayi cikin wasa, ta rufe bakinta da hannu, "Sorry na daina, wallahi dad'ine har yamun yawa"
    "Kin rik'eni da yawa, so kike Momie tace nayi dare gobe ta hanani fitowa?"
  Yanda yayi maganar saida ta bata dariya sosae "Momie bazata hanaka ba" ta gano Camera a wayanta.
     "first selfie?" ta kanne mishi ido, ta matsa inda yake ya duk'o zasu d'auka hotan, ya d'aura yatsanshi d'aya saman yatsanta mai d'aukan hotan, sannan suka d'auka a tare su duka suna dariya.
 
  Sunyi kyau su dukansu, nan take ta mayar dashi wallpaper, "Haka zaiyi zamanshi" shima a wallpaper d'inshi ya maidashi, sunyi kyau sosae, ba don sunso ba sukai bankwana, sai da ta daina ganinshi, ita kuma ta shige gida tana nunama Husna wayanta.
    Yana mik'a Hafsat wurin mai kula da ita, kai tsaye d'akinshi ya wuce don yasan Momie tayi barci yanzu, Yasseer harya kwanta, da yake daman d'akin nasu ne su biyu
     "Big bruz harka dawo?"
   "Kasan kuwa lokaci yanzu?"
       "anma dai tashi zakayi ka bani labari, yau babu barci"
   Girgiza kai Yasseer yayi, "So nake in kwanta da wuri, gobe da safe akwai inda nakeson zuwa"
      "Haba bruz daga dawowanka? Ina zakaje kuma?"
   "K'yauyen da Naje Bautan K'asa, akwai abinda na barone mai matuk'ar mahimmanci da nakeso inje in duba, abun yana raina bazan iya k'ara lokaci banje ganinshi ba"
    "Tohh ka bari ka k'ara hutawa zuwa jibi sai muje tare, anma yanzu ga azumi ga gajia"
   "jibi daren Sallah kenan mu dawo ranar sallah? Ba komai fa kasha zamanka, namafiso inje ni kad'ai, kai dai kamun addu'ah Allah ya bani sa'ar abinda zanje nema"
     "Ameen d'an uwah, Momie dai taa barka ko?" cikin wasa yace "ai aikin lallashin ta barni zuwa nayi tun dawowatah daga gidansu Rabiah" dariya sukayi,
     "Yaka baro Saudat d'in?" Yasseer ya tambayeshi
  "ya akai kasan wurinta naje?"
  "Momie ta fad'amun mana, ko wacce mai sa'ah ce ta iya samun zuciyar little bruz har haka?"
   "Saika ganta zakasan nima mai sa'ahne sosae dana sameta"
   "kana sonta da yawa gaskia"
   "sosai kuwa bruz, ina sonta fiye da rayuwatah"
   "gaskia naso ganin wannan Saudat d'in taka, da alama Momie ma tana ji da ita, anma ai zanje ganin Husna"
    "yanzu ma bara in nuna maka hotunanta"
    "karfa in ganta tafi kyau a hoto akan zahiri"
   Dariya yayi "Saudat ganinta ai yafi jinta"
   Folder da yake ajje hotunanta ya shiga, sannan ya mik'a mishi wayar bayan ya gano mishi hotunanta.

©Rabiatu sk msh

MATATAH CE 62

♡MATATAH CE♡
   ♡♡♡♡♡♡
            62

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
                   
            Labari....Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

  Sun gama exam suka fito, anata bankwana kamar an tafi kenan, wasu nata hotuna, itama ta d'auko wayanta Iphone7 da Najib ya bata aro don kawai tayi pictures, nan aka dinga zuwa aro kowa sai so yake tayi dashi, daga k'arshe ma ta bar musu suyi kawai. Tana tsaye gefe wata class mate d'inta tazo inda take.
   "Alhmdlh! Saudat muhammad Allah ya taimakeni baki tafi ba"
   "tohh Allah yasa dai lafiya"
       "Da sauk'i dai, tunda ciwon daga zuciyatah ne, number Yayannan namu nakeso ki bani"
    "Yayanmu kuma? Wa kenan?" ta tambayeta kamar bata gane.
    "Plz ki gane mana, wannan kyakkyawan dake kawoki makaranta yanzu"
    "Yaya Najib ne yake kawoni, karma in tsaidake ni bani da waya"
   "haba wancan Iphone d'in fa? Nifa numbershi kawai zaki bani"
   "tashi ce ba tawa ba"
       "Yazo da sauk'i, sai ma in saka mishi tawa, in kira inga numbern"
   "ke babu fa simcard a ciki"
        "Yau ni ya zanyi? Ki jirani plz ina zuwa" ta tafi da gudu tabar wurin, Saude ta bita da kallo tana tab'e baki, tana daina ganinta ta amsa wayarta tasan yana can yana jiranta, ta kusan kaiwa wurinshi sai gata ta dawo da gudu, tana kawowa inda take ta fara tafiyar yanga.

    Takarda ta mik'a mata
   "plz ki kai mishi" hannu kawai tasa ta amsa, sannan ta wuce tana mata godia, duk taa b'ata rai ta shiga motan. Saida ya tada ta mik'a mishi.
   "Ga sak'onka fa"
       "Sak'ona kuma?"
    "wata er class d'inmu tace in kawo maka"
   "Shiyasa kike ta b'ata rai kenan?"
  Harararshi tayi, "Meye na b'ata rai kuma daga sak'o? Ni gajia nayi"
   "tohh yarda ta"
      "me? Ai tunda na amso saika karanta ta"
   "nikam bazan amsa ba, ki d'auka in kina so"
   "inaso mana, bara ma in karanta" ta bud'eta ta fara karanta.
   “zuwa ga kyakkyawan saurayin da yafi kowanne namiji kyau a doron k'asa”
    Ta k'yalk'yale da daria "wao!"
     "ke ita ta rubuta hakan?"
   “bansan meke faruwa dani ba aduk lokacin dana ganka, zuciyatah sai ta dinga bugawa da sauri, dole akwai wani abu na musanman tattare dakai dake sanyani jin hakan a koda yaushe"
    "Ciwon zuciyah ne da ita"
   Saude ta k'ara tuntsirewa da daria, "Sirrin zuciyah dai"
  Tana dariya taci gaba da karantowa
    “bana tunanin komai sai naka a kullum, ko yaushe cikin tunaninka nake ko abinci bana iya ci”
   "taje asibiti kota nema maganin zafi"
   "ba wani Asibiti, kai dai..."
  "me kikace?" ya amsa takardar ya cukuikuye ya jefar da ita, "komai saikin karanta kenan? Cikin jin dad'i har wani daria kike"
       "kaifa ka bani ya zaka anshe?" ta fad'a cikin dariyar.
   "ni ba ruwana da wani er ajinku,"
   "tohm shikenan na daina, saura maganar da kace zamuyi"
    "aina d'auka kin manta" ya jawo wata linkakkiyar takarda a hannunshi ya mik'a mata.

   "naga yau karatu kikeji, ki karanta wannan ma duk abinda zan fad'a miki yana rubuce a ciki"
   Ta amsa ta fara karantawa a fili.
    “You are so funny, you are so nice,
You are the girl with whom I fell in love twice.
The first time was love at first sight,
The second time I feel for you was when I got to know you,
I realized that this was love, because the feeling was completely new.
I will never ever let you go away and leave me.
I will hold your hand and stand by you forever,
I will always be your Man, will leave you never!
I love you today and for always!”

  Tana fara karantawa ta daina fad'a a fili, ya kalleta yana d'auke da wani murmushin dake tafe da wasu sak'onnin, "nasan dai yanzu kin gama karantawa, abunda ke zuciyatah ne na fad'a miki, ina fatan zuciyarki zatayi maraba dani.
   Bai lura da yanayin data shigane tun sanda ta fara karantawa, gaba d'aya ta shiga tashin hankali, anya kuwa abunda takeyi dai-dai ne? Itafa matar aurece tayama zata fara tarayya da wani? Anya ta kyautawa Najib kuwa data b'oye mishi mijinta yana a raye?
   "Ina saurarenki, Allah yasa ba lokaci zakice in baki ba, domin kuwa nayi hak'uri da yawa, bazan iya jure lokacin da zaki d'auka kina tunani ba, idan har kina sona, baki buk'atar nazari akai, ki fad'amun abunda ke zuciyarki game dani, plz ki fad'amun da sauri Saudat"
   Kamar yasan abun da zata nema kenan a wurinshi, lokacin da zatayi tunani, idan har tace batason Najib tohh tayi babbar k'arya a rayuwarta, bata da wani buri yanzu saina kasancewa dashi, anma idanta amincema soyayyarshi anya kuwa taa kyautawa auren dake kanta? Wata zuciyarce ke mata tuni da cewa wanne irin auren? Yanzu k'ilama ya gama mantawa dake, ke kad'aice kika damu dashi, ki manta da Yasseer kiyi sabuwar rayuwar dake jiranki a gaba.
  Ba tare da wani dogon nazari ba, itama takarda ta samu mai kyau ta tsara mishi rubuta ta ninketa sannan ta bashi, murmushi yayi a motan ya bud'e ya fara karantawa shima a fili, lokacin yayi parking, ta bud'e da gudu ta fita.
   “You make me feel so special every time. There is not a single moment when I am with you and I don't smile. So many lovely moments with you and so many memories that we make is all imprinted in my heart. I am so lucky that I have someone like you in my life. I love you a lot”
    Yana gama karantawa yayi murmushin jin dad'i har saida ya sumbaci takardar. Daganan nasu labarin soyayyar ya fara.

Tun daga ranar gaba d'aya Saude ta manta da Yasseer a rayuwarta ko tunashi ma ta dainayi, soyayya suke ma junansu fiye da kowanne Masoya, Momie idan tana ganinsu a haka ba k'aramin dad'i takeji ba, babu inda Najib ke kunyar nunama Saude soyayya, ko yaushe yana tare da ita, kulawa ta musammam yake bata, shiyasa gaba d'aya ta manta da duk wata damuwarta.
     Yanzu tashin hankalinta d'aya Momie tace bayan Sallah zasuje k'yauyensu ayi maganar aurensu da Najib, gaba d'aya damuwarta yanzu idan Momie taje k'yauyen aka fad'a mata cewar itafa matar aurece, mijinta nanan da ranshi guduwa kawai yayi ya barta, a wane matsayi zasu ajeta ita da Najib?.

Watan Azumi ya kama, har yayi tsakiya babu Yasseer, Momie gaba d'aya tayi fushi dashi ko kiranshi ta daina d'agawa, kullum cikin yima Najib waya yake ya tayashi bata hak'uri.
   Masoyan guda biyu Saude da Yasseer, kullum suna tare, idan ya farka zaiyi sallar tsakar dare saiya buga mata k'ofa ya tasheta, kullum asuba a falo suke zama yana k'ara mata karatun Qur'ani, shiya zama malaminta a b'angaren addini ma, yana k'ara mata sani akan sauran littafan, idan kuma suka tashi soyayyarsu sunfi kowa iyawa.
     Tare suke zuwa siyayyar sallah, komai kala d'aya yake sai musu, ko atamfane ya sai mata saiya sayi yadi kalan, kaya masu tsada ya dinga sai mata kamar baison kud'in, kowanne da takalminsu, jikka, da gyale duk kalar masu tsadar gaske, Momie ma tayi mata kayan sallah masu kyau, ita har rasa bakin godia take ga wannan mutanen.
   Anata shirye-shiryen Sallah saura kwana uku, Yasseer yama Najib waya gasunan zasu baro Moscow, koda ya fad'a ma Momie bata wani yarda da gaske yake ba don tafi kowa sani k'aryarshi kullum zaizo kuma ba zuwan yake ba, sai dai d'a da mahaifi, duk da tana fushi dashi saida tasa aka shirya musu abinci kala kala, tarba dai ta musamman.

  Suna sauka yayi ma Najib waya gasunan fa a tura musu driver, "Haba ina garin zakace driver, ganinan tafe yanzu bruz"
    "Tohm sai kazo"  daman a shirye yake yana jiran wayarshi, su Saude ma an zuba ido tanaso taga wanene wannan Yasseer d'in nasu Najib?

©Rabiatu sk msh

Popular Posts

 
]]>All content on thisblog are copyright protected and cannot be reproduced on other websites without permission.