New Post

ABUBUWA BAKWAI (7) ABIN KULA GA DAN'ADAM

1. Duniyar da za a barta, me ya kawo hadama? 2. Dukiyar da za a lissafa daya bayan daya, me ya kawo tarata? 3. Rayuwar da zata kare, ina wani farin ciki? 4. Yarintar da tsufa zai zo mzta, me ya kawo takama? 5. Ana sauraren mutuwa, ina wata walwala? 6. Jikin da zai zama gawa, me ya jawo dagawa? 7. Karshe dai makomarsa kabari, me zai sa alfahari? Wanda ya manta da wadannan a ina ya bar hankalinsa? Allah yasa mu dace, yayi mana kyakkaywan karshe. Ameen!

KADA KA RAMA CUTA GA WANDA YA CUCEKA!

Kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka, kai kayi hakuri. Zaka samu abu biyu sakamakon hakan; * Na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. * Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

KADA KA BARI ZUCIYARKA TA ZALUNCEKA!

Kada ka sale zuciyarka ta zalunceka, tabbas zaluncin zuciya ga gangar jiki yake komawa, idan akayi wasa ya zamanto ya shafi rayuwa. Assasa bak'in tunani, yawan zargi da rashin tabbas akan wani aiki, zato, shakku ko kokwanto akan wani al'amari batare da tantance gaskiyarsa ba, shine zaluncinzuciya akan dan Adam. Maza ka hana zuciyarka don akwai hadurra dubu akan hakan.

MAHAKURCI MAWADACI

Tabbas ba kowane dandanon magani ne ke da dadi ba, amma babu shakka shine abu mafi dacewa ga dukkan mara lafiya. A lokuta da dama rayuwa takan dakeka da guduma ta jefaka acikin wani mawuyacin hali, kayi ta fama amma tayi maka tutsu. Amma idan kayi hakuri sannu ahankali zata kwaranye. Hakika ba duk abinda rai yake so yakan samu ba, amma bukata bata taba sauyawa ba kuma bata taba karewa ba. Don haka ka shirya bukatunka da kyau ka bisu daya bayan daya sannu a hankali, kayi gwa- gwarmaya, sannan kayi juriya. Tabbas mafarkinka zai zama gaskiya.

KO KA SAN?

Rayuwa bakin alqalami ce tana bukatar kaifi sannan tana son tsini. Kaifin don ka yanki magauta, tsinin kuwa don ka soki makiya. Haka zalika rayuwa kamar randar ruwan sanyi ce ta kasa tana bukatar tanaji da adani, kodn wata rana ka shayar da masoyanka. Da kyau ka lura da abu biyu a rayuwa; 1. Ka lura da mai zaginka mai aibantaka wata kila wata rana zai iya zama masoyinka mai yabonka 2. Ka lura da masoyinka na kusa mai yawan ambaton alkhairinka, wata kila wata rana zai iya zama makiyinka mai zaginka.

Friday, 12 July 2019

MEYE SANADI? 1

♡ *MEYE SANADI?* ♡
           ♡♡♡♡♡♡
              ♡♡♡♡
                  1
©Rabiatu sk msh
     ®NWA

WATTPAD; Rerbee'art_sk

Wannan littafin nawa, ƙirƙirrare ne, banyi shi don cin zarafin wani ko wata ba, ina maraba da gyara a duk inda yake indai ba na cin fuska bane.

Dole na gaishe da  ƙawayen albarka, RAZ nawa, bazan taɓa gajiyawa da faɗan yanda nakejin ku a zuciyatah ba, ku ne ni, nice ku (Amrah A msh, Zahra BB) Aminan ƙwarai

Bismillahir rahmanir rahim

Wayarta dake hannunta, ta maida gefe bayan ta gama duba abunda takeson gani, sannan ta ɗaga idanunta ta fara ƙarema yalwatacce, kuma ƙayataccen ɗakin da take ciki kallo, anya ta yiwa kanta adalci kuwa idan ta ƙarar da rayuwarta ita kaɗai a cikin makeken gidannan? Tabbas duk warin da zatayi, bata tunanin maƙotanta zasu iya jiyowa ballantana har gawarta ta samu gatan da za'a mata sutura,
      Kasancewar unguwarsu, unguwa ce da babu ruwan wani da wani, bata son ko bayan mutuwarta gawarta taci gaba daa rayuwa a wannan gidan, wannan dalilin ne ya sakata jawo mukullin ɗaya daga cikin motocinta, da wayarta, sannan ta zuba duk wani abunda ta tanada a cikin but ɗin motar, da kanta ta buɗe gate ɗin kasancewar ko mai gadi bata dashi, sannan taja motarta ta doshi hanyar daji bayan ta rufe ko ina.

Tafiyah tayi mai ƴar nisa,  sannan tayi parking dai dai wurin wani icce, sai da ta ƙara jawo wayarta, ta duba hotan sosai sannan ta maida ta aje, ta buɗe but ɗin motar ta fito da wani madaidaicin (Stool) mai kyau, ta ajje, sannan ta ɗauko igiya, ta taka Stool ɗin ta ƙulle igiyar a jikin wani ƙaton reshe, kaman yanda ta gani a jikin hotan, har lokacin babu wani tsoro a ranta ko fargaba, babu kuma tunanin zata fasa abunda tayi niyya

*** ***
Abokinshi yayi ma Rakiya ganin wani fili da yake son mayarwa gidan gona, hakanan yanayin wurin ya burgeshi har yaji yana son zagaya wurin sosai,
    Yana tafiya yanayin wurin na mishi daɗi, har baisan lokacin da yayi nisa sosai da inda yabar Abokin nashi ba, ko wayar da yakeyi ce ta ɗauke mishi hankali? Sai da ya gaji da surutun da take mishi, yana niyyar sauke wayar ya hangota da er tazara tsakaninsu,
    Abun da ya hangone ya tabbatar mishi lallai ƙoƙarin kashe kanta take,  ta taka Stool ga igiya tana ƙoƙarin saƙalawa a wuyanta, da saurinshi ya ƙarasa inda take.
     "Ke! Ke!! Dakata mana, meye haka kike ƙoƙarin yi?",
     Wani irin malalacin kallo ta bishi dashi baki a buɗe ba tare data bashi amsa ba.
      "Awk fahimta, na gane! Ƙoƙarin kashe kanki kike, anma saboda me kina yarinyarki?"
    Wannan karon ma bata bashi amsa ba, duk da shirin da ya ɗanyi ganin da tambaya ya ƙarashe maganar shi.
 
Ganin hakan ma duk baiyi ba, ya ɗan dai daita natsuwarshi,
    "Sauko" yana ƙara mata alama da hannu,
   Ta ƙwalalo idanu tana kallonshi da mamaki,
       "sauko nace"

Sai yanzu tayi magana, karo na farko,
       "Malam wai lafiya, me ruwanka dani?"
     "kashe kanki kikeson yi ko wahala kike son bama kanki? Waya faɗa miki haka ake ma igiyan? Da taji nauyinki zata warware ki faɗo a ƙasa ke kaɗai babu mataimaki,"

     "idan da gaske kashe kanki zaki sauko ki gani in gyara miki"
    Ta wurga idanunta,
"kaga alamun wasa ne a tattare dani?"
   Sannan ta sauko ta koma gefe ta goya hannayenta,
    Tana tsaye ya taka stool ɗin ya gyara ƙullin ta da yima igiyar sosai, sannan ya sauko,
    "Yauwah kinga hakan yayi"
   
Sai da ta dai-dai ta saman kujerar, ta runtse idanunta, sai ga muryarshi ta ƙara dukan kunnuwanta,
      "yanzu duk taimakonki da nayi baza kimin koda godia ba?"
     "koda yake, wake neman godia daga wurin matatta? Ci gaba kawai"
      Ta sake rufe idanuwanta,
     "Yauwah, faɗamun sunanki ma idan na tashi  miki addu'ah"
   Ya ɗan riƙe haɓa (chin) alaman tunani,
      "wacce Addu'ah kuma, bayan tun duniya kin san makomarki? Duk wanda ya kashe kanshi wuta ce zai shiga ko?"
    Ya ɗago yana kallonta, yanayin jikinta duk yaa fara yin sanyi,
    Ya ɗan buge bakinsa da hannu,
    "Awwh Sorry ci gaba"

Shiru tayi da alama ta lula duniyar tunani,
      "kici gaba, ko kina buƙatar wani taimakon nawa ne?"
    Ya koma daga bayanta, ya ɗan saka ƙafarshi kaman zai ture stool ɗin, da sauri ta saka hannayenta a wuya ta riqe igiyar tana jan firgitacciyar ajiyar zuciya, ya mai da stool ɗin yanda yake.
         "Mutuwa babu daɗi ko? Ki kwantar da hankalinki, bazan janye Stool ɗinnan ba, idan nayi hakan ahh kaman nina kasheki, bazaki ɗauramun laifin kisan kai ba"
    Ya ƙarasa maganar yana ware hannuwanshi.

Cikin zafin rai taja wani siririn tsoki can ƙasan maƙoshinta, sai kallonshi take tana maida numfashi, kaman ta shaƙeshi ta huta takeji, ya ɓata mata shirinta na yau, idanunta kaman su ɓalle saboda hararar da take aika mishi, kafin ta sauka kawai, ta faɗa cikin motarta, ta jata da gudu ta bar wurin.

Ta fasa kashe kanta ne?
Meye Sanadin da take son kashe kanta?
Wacece ita ɗin?
Zata ƙara haɗuwa da wannan saurayin daya kawo mata cikas?

Muje zuwa domin amsa dukkan tambayoyinku

Rabiatu sk msh

Sunday, 18 February 2018

MAFARIN SO 1-5

♡♡MAFARIN SO♡♡
   ♡♡♡♡♡♡♡♡      
         ♡♡♡♡♡
                1-5

©Rabiatu sk mashi
         ®NWA

Rerbeeart_sk @wattpad

www.babymsh.blogspot.com

Tafiya take cikin nutsuwa, burgewa, da takun Isa, Sanye take cikin doguwan rigan material, kalan brown da milk, saita yafa k'aramin mayafi akai, tana rik'e da wasu littafai a hannunta.
      Bata ankara ba sai dai taji abu ya dakar mata goshi harta kusa faɗuwa, kafin ta ɗago kanta kawai taji an kwashe da dariya, cikin k'unar zuciya ta ɗago da kanta tana k'arema wurin kallo, gaba ɗaya cike wurin yake da ɗaliban jami'ar kuma kusan duka hankalinsu na akanta. Dariyarshi tafi shigar mata kunne, juyawa tayi ta watsa mishi harara.
    Dariya yayi irinta gogaggun en iskannan,
    "zo mana" ya kirata da hannu, yana zaune saman motah da en korenshi zagaye dashi, taso ace zata iya komawa ta sauke mishi duk masifan dake ranta, anma jin kanta da tak'ama bazai taɓa barinta ba, kuma shi bai kai ajin da zata tsaya gaban mutane tana maida magana dashi ba. Juyawanta kawai tayi taci gaba da tafiyanta,
      Batasan sanda ya diro daga saman motan ba, sai dai kawai taji yana neman rik'o hannunta, cikin zafin nama ta juyo ta wankeshi da marin da yazo mishi a bazata, ɗaga kanshi yayi yana kallon mutanen da sukayi cincirindo suna kallonsu, sannan kowa ya fara k'ok'arin riƙe dariyanshi don babu wanda baisan halin Abdallah ba.
       "Ni kika mara?"
     "an mareka ɗin, wannan shine gargaɗin dazan maka na ƙarshe akan shiga harkata da kake"
        "ke kinsan waye Abdallah, wallahi sai kinyi dana sanin marina da kikai"
     "Anma bakasan wacece Rabi'ah ba, kuma ina mai baka shawaran karka zaƙe akan saika sani ɗin"
     Nunata yayi da ɗan yasha, "zan ramane a inda zaifi miki ciwo, kuma ki sani ban taɓa son abu na rasa ba, ko bakiso dole kiyi soyayya dani"
    Tofar da yawu tayi a k'asa, "Allah ya kiyayemun soyayya da ɗan shaye-shaye" ta juya ta barshi wurin a tsaye yana huci yama kasa maida mata magana, ya watsa ma mutanen wurin kallo ba shiri kowa ya ɓace, ya shige motanshi ya jata a guje.

Hankalinta kwance ta gama lecturenta suka fito tare da Aminiyarta Amrah,  hannunta taja suka koma gefe,
      "Faɗamin Rabi'ah meye gaskiyar abinda naji wai kin mari Abdallah"
     "toh meye naga duk kin wani ruɗe kaman wani babban abune ya faru?"
    "haba Rabi'ah, naga hankalinki kwance kaman bakisan halin Abdallah ba"
    "ni mamaki kike bani wallahi, siyasa ne kawai zai nunamun, anma kuɗi kam har ke kinsan Yayana yafi mahaifinshi sosae, don haka duk abunda zaiyi nima zan iya, ban taɓayin abunda nayi dana sani ba"
     "hakane fa, anma ni dai duk a tsorace nake"
     "kinma warware,"

Tun daga bakin gate, ma'aikatan gidan ke kawo mishi gaisuwa anma ko kallo basu isheshi ba, ganin motoci da yawa ya tabbatar mishi Daddyn nashi na a ciki, don haka kai tsaye falon Mai girma mataimakin Governor ya wuce,
      Zaune yake yana amsa waya, bodyguards nashi zagaye dashi, yana ganin yanayin da Abdallah ya shigo dashi, ba tare da yaa gama ba ya katse wayan.
     "Yadai Son?" cikin sham ƙamshi ya kalli bodyguards ɗin, sannan ya maida kallonshi kan Dad din nashi, alama ya musu da su fito, cikin bin Umarni duk suka fita.
      "waye kuma ya taɓomin kai?"
   Saida ya ƙara ɓata fuska sannan ya fara magana, "Haba Dad! Ni bansan me yasa baka damu da abinda nakeso ba, ba ruwanka dani sai harkan siyasarka kawai"
     "akwai abinda ka taɓa nuna kanaso banyi maka bane?"
     "A'ah kawai dai wannan ne nake tunanin bazan samu ba"
    "babushi, indai Kuɗi da Mulki na iyayin komai a duniya babu abinda zaka nema bazanyi maka ba"
      "I know Dad, but uh should promise me"
     "promise"
   "thank you Dad, i love you"
Sannan ya fara fara'a, jinsa yake wasai kaman yama riga da yaa rama abinda Rabi'ah ta mishi.

Follow me On wattpad @Rerbeeart_sk

©Rabiatu sk msh

Tuesday, 15 August 2017

HAKKIN KISA 81-100

☠HAK'K'IN KISA☠
      👽👽👽👽
             81-100

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
Wattpad @Rerbeeart_sk

www.babymsh.blogspot.com

🔚🔚🔚

  Maman Hajna tayi gyaran murya cikin damuwa ta fara magana.
    "Nice nan na haifa Hajna, kuma babu wanda yake da Hakkin Kisanta saini, nasan kowa zaiyi mamaki dajin hakan, anma ba abun mamaki bane idan kunji bayanin dazai fito bakina, fatana kawai sauran mutane zasu ɗauka darasi karsu aikata irin aikin wautar da nayi"
     "tun lokacin da likita yayi bayani kan mutuwan Hajna, na shiga k'ok'onto, domin bansan wanne irin hukunci za'a yankemun ba, shiya hanani magana"
    "na kasance tun kafin haihuwar Hajna, nakejin mutane na magana kan indai kana da yarinya ɗiya mace, kamata yayi tun kafin ta girma ka fara gyarata da magungunan mata ba saita girma an mata aure ba, da wannan burin nayi aure harna samu cikin Hajna, kuma cikin sa'a Allah ya bani rabo da ɗiya mace, tana da shekara 7 muka haɗu da Hajia karime mai bada magani, tun daganan take kawomun magungunan da bansan asalinsu ba, nake ɗurama Hajna, kullum cikin bata magungunan tsumi nake, hardana tsarki dana matsi, da kaina nasan Hajna badon tanaso ba take amsar magungunan nan, anma ko a fuska bata taɓa nunamun ba, da yake yarinya ce mai biyayya"
      Alk'ali ya nisa sannan yace "kenan magungunan da kike batane silar cutar data sameta?"
    Hajia Saratu tayi karaf tace "k'waraima kuwa, domin nima mutane da yawa na kokamun akan wannan matsalar"
     "kenan kunsan yana cutarwa kuma kuke saidawa?"
    "Itama ae mun faɗa mata yana cutarwa"
   Kallonsu kawai yake da mamaki, gaba ɗaya kotun jikinsu yayi sanyi, ya kalli maman Abdul,
    "menene abunda zaki faɗama kotu kan mutuwar Hajna?"

    "tabbas ni nake da abun faɗa, duk da bayanin da tayi yayi kama da nawa, ta faɗi silar cutan Hajna, anma nice nan nayi Silar mutuwarta, domin kuwa tunda aka saka ranar auren Abdul da Hajna, na fara amsar magunguna a hannun wannan mutumin da yake tare dani, shine yake kawomun magungunan k'ara ma maza k'arfi, ni kuma nake ba Abdul ba tare da saninshi ba, duk da baisan ko miye ba, anma a dole nake matsa mishi yasha, bayanin da zanyi kenan yamai shari'ah"

   Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abunda wasu daga cikin mutane kotun ke ambata, gaba ɗaya Meerah a firgice take dajin wannan bayanin, ballantana Abdul da yake jin maganar kaman saukar aradu.
    Alk'ali ya ringa girgiza kai cikin mamakin wannan iyaye, gaba ɗaya abun ya ɗaure mishi kai.
     "wannan wanne irin iyayene nake gani a gabana? Iyayen da zasu bama yaransu abu bayan kuma sunsan zai cutar dasu kawai da sunan gyara? Gyaran da ɓacinshi yafi amfaninshi yawa, yau wa gari ya waya? Abunda kika daɗe kina mata gyaran kanshi ya k'are a daren farko? Wallahi wannan kuskurene babba, gareku iyaye da kuma ku masu saida magungunan da bakusan asalinsu ba da sunan gyara, abun kunya ma wasu matan ne da kansu keshan abunsu"
    Ya kalla Hajia salame, "kina da aure? Yaranki nawa?"
      girgiza kai tayi cikin jin kunya, "bani da aure a yanzu, ban taɓa haihuwa ba sanadiyyan shan magungunan matan da nake"
      "kefa?" ya tambaya Hajia karime "aurena huɗu anma babu ko ɗaya"
     "kun gani ba? Wallahi magungunan nan ba k'aramin illa sukewa mutane ba, gaba ɗayama kun sanya ɓacin rai na manta abunda ke gabana"

     Duk'awa yayi yana en rubuce-rubuce, sannan ya ɗago kai kowa yayi shiru yana jiran yaji mezai faɗa,          
    "Bayan nazari da dogon bincike akan wannan shari'a, mun gane cewa Abdul bashi da laifi ko kaɗan akan mutuwan Hajna, domin kuwa gasha magungunannan ne a bisa rashin sani, sannan kuma abunda ya faru dashi a ranar aurensu da Hajna ba laifinshi bane, ya faru ne akan Maganin da yasha cikin rashin sani, don haka kotu ta wankeshi daga zargin da ake mishi"
    "Sannan kuma gaba ɗaya mutanen nan, babu wanda HAKKIN KISAN Hajna bai rataya a kansu ba, don haka kotu ta yanke musu hukuncin shekaru goma a gidan yari, Maman Hajna, Umman Abdul, da kuma sauran masu maganin nan guda Uku"
   Kotu.....!!!  

Umman Abdul anan wurin ta duk'e tana kuka, Umman Hajna kam Ɗaura hannu tayi akai tana ta ihu kaman wacce ake zarema rai, Hajia karime ta rungume Hajia saratu,
    "kaicon mu, kaicon duk wata macen dake bama er uwarta mace maganin dake cutarwa akan gyara, kaicon wannan hali namu yanzu gashi abunda ya jawo mana"

    Tsananin farin ciki Meerah batasan sanda ta taso ta rungume Abdul ba tana dariya, anan inda yake tsaye yana ma mahaifiyarshi wani irin kallo na tausayawa, ganin Abbanshi na zuwa inda yakene, cikin dubara ya cire Meerah daga jikinshi.
    Yana ɗaga ido ya hango Hajna tsaye cikin farare kaya, tana murmushinta mai kyau, kallon Meerah tayi tana mishi alama cikin murmushi, a haka harta ɓace gaba ɗaya.

Alhamdulillah
Anan na kawo k'arshen wannan gajeran labari nawa, kuskuren dake cikin Allah ya yafemun, Allah kuma ya bamu ikon amfani da darasin dake ciki.

SADAUKARWAR Takice Auntie Sis, Allah ya k'ara girma, tabbas babu wanda yasan halin karamcinta sai wanda ya zauna da ita.

Godia Mai yawa ABDULAZEEZ ILILEE, Allah ya k'ara basira da ɗaukaka, muna tare dakai a littafin BARE

Jinjina ta musanman ga k'ungiya mai Albarka, NAGARTA WRITERS ASSOCIATION, Allah ya k'arama mana haɗin kai, Ameen.

RAZ nawa, banda kamanku Amrah A msh, ZahraBB, Alah yabar k'auna.

Gaisuwa ga dukkan makaranta littafinnan, dama masoyana gaba ɗaya, Allah yabar k'auna, kuci gaba da kasancewa dani a littafin ZAMAN AURE, wani zaman ma yanzu za'a fara.

Domin gyara da shawarwarinku +2348032133670

©Rabiatu sk msh

HAKKIN KISA 76-80

☠HAK'K'IN KISA☠
      👽👽👽👽
            76-80
©Rabiatu sk msh
      ®NWA

www.babymsh.blogspot.com

Rerbeeart_sk @wattpad

Kotu....!
Ta cika ta tumbatsa, ko ina mutanene ba masaka tsinke, a can na iske en RAZ novella sun riga kowa zuwa, su Maryam tapeeda, dr meenert, murjar baba, umman sayyida, da marymaama kam suna gaba baba, en KHADIJA CANDY novels gayya guda sukayo, ASHNUR ma naa hangota da tawagarta, PHERTY zahra exam take anma ta ajje sai da tazo kotu jin yanda zata kaya, en MU FARKA MATA daman a can gari ya waye musu, en ILILEE novels kowa yazo sai hange nake ina zan hangoshi? Ga UMMU ABRAR ma tazo da Abrar ɗinta a gaba (if u knw wat i mean😆).
     Wasu en mata dake kusa dani naji suna maganan wata mata da miji, ae ba k'aramin burgesu suke ba, mijin sai ririta matan yake kaman ita kaɗaice er gata a dunia, jin yanda suke zuzuta couples din ya sakani waiwayawa ba shiri, "wazan gani haka?" abunda nace kenan.
    Dariya yayi yana nunata  "MATATAH CE"
     "kaikam Najib har yanzu baka daina faɗin matarka bace?"
     "ina ae har a Aljannah na ringa faɗa kenan Saudat Matatah ce"
    Sama-sama muka k'arasa gaisawa da Sauden Najib, saboda hango best couple ɗina da nayi, Majeeda da Majeeda rik'e da kyawawan yaransu, sai mita yake mata shifa baison zuwa irin wurin hayaniyarnan ta kawoshi, kusa dasu HAFSATUL KIRAM ne da Ya Umar ɗinta.

    Shigowan Alk'ali ne yasa kotun tayi tsit, kowa ya nutsu, shari'arsu ce ta farko, aka gabatar da ita, barrister Ahmad ya fara mik'ewa, shima da ganinshi  yana cikin yanayi. Idan ya kalla Abdul da yanayin da yake duk sai yaji ya k'ara sarewa, don yaune ranarsu ta k'arshe.
      "Shaidar da nake da ita a yau, itace cikakken bayanin likita akan cutan data kashe Hajna, wanda suka k'ara zurfafa bincike suka gano"

Likitan ya fara bayani, da takardar report a hannunshi.
       "wannan report ɗin mun nemo bayani ne a wurin likitan dake duba Hajna lokacin da take raye kan Matsalar infection da take fama da ita. Report din ya nuna cewa tana yawan fama da infection wanda hakan kesa tana zuwa asibiti don duba lfyrta. Likitan yace duk zuwa ana mata HVS/MSC( High viginal swab/microscopic, culture and sensitivity) don ganin kalar microorganisms din dake cikin gabanta da neman maganin da zai kashe kwayar cutar Dan da nan.
Wani lokacin ma idan abun yayi kamari sai anyi mata ECS/MCS(endo cervical swab/microscopic, culture and sensitivity) Wanda idan ta dace magani tana dadewa abun bai tasar mata ba. Amma kuma mun dauki hakan ne a makaranta take kwaso infection din sbd kwamacala ta bayin makaranta da kuma fitsari inda bai kamata ba.
     A binciken da mukayi kan vigina din Hajna mun gano wani tsuro wanda haduwar wasu abubuwa da bamu san ko miye ba suka dunkule waje daya duka tsuro sai ya zama kamar tumour. Sai ya tsiro mata daidai idan an wuce labia majora, labia minora wajen vulva dinta kafin a kai cervix. Shine abinda ya fashe a gaban Hajna har ya kawo wannan jinin mai yawa da muka gani faca faca a jikinta da gadonta.
    Tambayarmu a kan Abdul itace shin yana shan wani abu ne da ke kara karfin maza kafin yayi aure ko kuma kasha kwaya ne ranar da aka kawo maka Hajnah
      Sbd yadda yaje ma Hajna abun tambayane,babu yadda zaayi namiji ya sadu da mace na tsawon wannan lokacin tun wajen 11 na dare har asuba) alhalin lfyrshi lau bai sha komai ba.
    Dadewar da yayi yana saduwa da ita ne ya kawo fashewar wannan abun
Amma da ya sadu da ita na kankanin lokaci ta kuma hanyar hankali da ko tsautsayin zai faru zai zo ne da sauki sosai."
    Barrister Ahmad yayi gyaran Murya bayan an mik'a ma alƙali takardan,
      "wannan shine bayanin ɓoyayyar cutan da Hajna ta daɗe tana fama da ita, Ya mai girma mai shari'ah, ina fatan wannan hujjar zata zama gamsarshiya wurin wanke Abdul daga laifin da ake zarginshi dashi"
     "ina da ja Ya mai shari'ah" inji barrister Alqaseem.
     "bai kamata shari'arnan ta k'are a haka ba, idan mukai nazari akan bayanin likita na k'arshe, mun yarda da batunshi na cewar Hajna nada cutan Infection wanda har iyayenta basusan da tana zuwa wurin likita yana dubata ba, anma shida kanshi likitan yayi bayani kan cewan inda Abdul baisha wani abu dazai k'ara mishi k'arfi ba abun zaizo da sauk'i, kenan har yanzu HAKK'IN KISAN hajna yana kan Abdul"
    Ya maida kallonshi akan Abdul, "Malam Abdul, tunda har anzonan, bai kamata kaci gaba da wahalan da shari'ah ba, wanne irin magani ne kasha ka jema Hajna a daren data rasu?"
    Girgiza kai kawai yake, "babu abunda nasha, wallahi tunda nake da idona ba ban taɓa ganin maganin k'arama maza k'arfi ba, ban taɓa sha ba, mezai sakani shan abunda zai cutar da Hajna ma?"
    
    Barrister Alqaseem ya juya kan Alk'ali, "ina ganin duk hujjojin da kotu take buk'ata kan dalilin mutuwan Hajna sun kammala, Abdul yayi amfani da matarshi Hajna tun daga k'arfe 11 na dare har zuwa Asuba, wanda wannan ba k'aramin cutarwa bane a gareta, bayannan kuma bai tashi je mata ba saida yayi amfani da maganin daya k'ara mishi k'arfi, bisa duba da wannan hujjojin nake rok'on kotu da tayi gaggawan yankewa Abdul hukunci, domin babu wanda yake da HAKK'IN KISAN hajna bayanshi"
    Barrister Ahmad dafe kai yayi kawai ya koma ya zauna domin kuwa yama rasa da wanne kalamin zai k'ara kare Abdul, Alƙali ya duk'a yana en rubuce-rubucenshi, gaba ɗaya kotun tayi tsit kowa da abunda yake sak'awa a ranshi, k'aran kukan Meerah kawai ake jiyowa, Abban Abdul ma duk da k'arfin halinshi saida ya zubda hawaye, Umman Abdul daman baizo da ita ba saboda Halin da take ciki na tsorata.
      Anan wurin Abdul ya duk'ar da kanshi yana hawaye, kanshi na matuƙar sara mishi, tunanin Hajna na dawo mishi sabo, ɗaga kanshi yayi yana kallon Meerah, yanda take kuka da alama tama fishi shiga tashin hankali, Allah sarki khadija, yasan tana can gida tana ta mishi Addu'a.

    Maman Hajna ce Zaune, idonta rufe tamak'i buɗewa saboda wani abubuwa dake mata yawo saman kai, tana jin hayaniya anma tayaya zata iya buɗa baki ta faɗi gsky gaban wannan jama'ar? Buɗe ido tayi da niyyar ta k'ara k'are musu kallo, wani k'aton kai ne mai ban tsoro, babu tsoka ko kaɗan sai k'ashi ya taho baki buɗe ya kusan kaima fuskarta karo, ta fasa wani uban ihu ta rufe ido.
     Cikin kunnanta ake mata wani irin tsawa, "Bazaki faɗa ba? Ki buɗe baki kiyi bayani, ki faɗi gaskia nace"
    A ruɗe ta mik'e, "zan faɗa! Wallahi zan fafa" kowa ya juya kallo ya koma kanta, harta alƙali tsawa yayi da rubuce-rubucenshi.
    Saiga Umman Abdul tare da wani mutum irin en k'auyennan, kaman an jefosu sun dira gaban kotu,
   Umman Abdul tace "a dakata, ba shine ya kasheta ba"
     Maman Hajna tace "eeh bashi bane, nice nan nayi silar mutuwar y'ata"
    Umman Abdul tace "A'ah nice dai, nice nayi silar mutuwarta" ta kalla mutumin da sukazo tare,
     "gaskia mukazo mu faɗa ko?"
   Shikam Abdul kallonsu kawai yake da mamaki, Ummanshi kuma? Meya haɗasu da mutuwan Hajna?
   Mutumin yace "k'warai ma kuwa, babu mai HAKKIN KISAn baiwar Allahn nan Ya mai shari'a sai mu, domin kuwa ni naga abunda na gani, sati guda kenan HAKKIn ta ya hanani runtsawa, idan na kwanta na ringa ganin kawuna kenan, kai ido buɗe ma cikin tsorata nake"
   Daga can baya suka jiyo murya na cewa "muma haka, Mune nan Mukai silar mutuwan Hajna, gaba ɗaya mutuwanta ta hana mana sukuni" su Hajia karime ne, hango Maman Hajna da sukai a tsaye ne ya saka har suna rige-rigen K'arasawa inda take.
     Hajia saratu tace "kiyi hak'uri Hajia, anma dole mu faɗi komai a gaban kotu yanzunnan, domin kuwa rayuwanmu na cikin hatsari indai bamu faɗi gaskia ba"
    "k'warai ma kuwa, duk kwanakinnan cikin tashin hankali muke, hak'uri zakiyi kawai Hajia mu muka ga abunda muka gani"

   Gaba ɗaya kotun ta hargitse, kowa da abunda yake faɗa, mamaki faal a zuciyoyin mutane, sai da Alk'ali ya tsawata sannan kowa yayi tsit.
    "ya isa haka, kotu ba wurin sauraren hayaniya bane, idan da maganar da zakuyi a gaban kotu zaku fito ku faɗeta" su duka kamar walk'iya sai gasu sun wuntsilo gaban kotu.
    Alk'ali yama Maman Hajna Umarni akan ita za'a fara saurara.

Kumin Uzuri, wallahi hannuna ya gaji naso kuji komai a yau, anma ku k'ara hak'uri zuwa next page plz

©Rabiatu sk msh

HAKKIN KISA 71-75

☠HAK'K'IN KISA☠
      👽👽👽👽
            71-75
©Rabiatu sk msh
      ®NWA

www.babymsh.blogspot.com

Wattpad
@Rerbeeart_sk

    Abubuwan Maman Hajna sun fara munana, ko ita kaɗai take zaune kaman mai shirin zaucewa, ta ringa ihu tana faɗin Hajna ta dawo a fatalwa zata kasheta. Sai su Muhseen sun ringa rufe mata baki, buge hannun take.
     "ku barni in faɗa, Hajna ce ta dawo ba kowa ba"
    Sai dai suyi shiru kawai suna kaɗa kai.

   A daren Ranar da za'a koma kotu, tana zaune Umman Hajna da k'aton carbi tana ja, batasan ma me take faɗa ba tunda hankalinta ba wurin yake ba.
     Giftawan mutun take gani, ta k'ara zare ido tana ci gaba da jan cazbahanta da sauri, nan da nan zufa ta fara karyo mata, ta buɗe baki da k'arfi tana karatun da batasan ma me take faɗa ba, sai dai taga tsayuwan mutum a gabanta, ta kasa ɗago kanta, sai dai taji kaman an ɗago da kanta.
   Kallon mummunan fuskan take jikinta na kyarma ko ina, har ya suɓuce a hannunta.
      "Kin shirya zuwa kotun kiyi bayani kuwa"
    "don Allah kimun rai, wallahi na tuba na daina"
   "karma ki tuba ɗin, Gobene zaman k'arshe a kotu, babu wanda yasan gaskia saike, don haka idanma baki je kinyi bayani ba..."
        "Hmm nice nan zan ɗauka hukunci da kaina"
    "zanje, zanje wallahi...."
Kafin ta gama rufe baki fatalwan ta ɓace.

    Umman Abdul na kwance gefen Abbanshi, tuni yayi barci ya shareta, yanzu kwata-kwata barcinta bai wuce na minti biyar, sama-sama tanayi tana tashi dube-dube.
   Can idonta yakai kan madubi, rubutu ne da jan pen an rubuta.
      "Idan har kinason ci gaba da rayuwa, ki faɗi gaskia a gaban kotu gobe"
      Jikinta na kyarma ta fara tattaɓa Abban Abdul, yana jinta ya mata banza, don ya riga da yasan halinta haka zasu kwana fana firgita sai ya tashi babu komai, tun tana tadashi a hankali harta fara dukanshi tana kuka.
    Tashi yayi a harzuk'e, "miye kuma? Meya faru?"
    Hannunta na kyarma take nuna mishi mirrow, kaman yanda ya zata, babu komai.
     "miye a jikin mirrown?"
   "Gashinan, rubutu ne, wlhy kasheni zatayi?"
    "wacece? Ni banga rubutun komai ba"
   Ta juya tana nuna mishi, itama bata ga komai ba, ta rirrik'eshi tana kuka kawai. Shareta yayi ya tashi ya shiga toilet ɗauro Alwala.

      Daren ranar dukkansu kwana sukayi saman sallaya, Meerah, Khadija, Abban Abdul, da kuma Abdul ɗin, kowannensu Addu'an neman nasara yake mishi akan shari'ar da zasuyi gobe.
   Banda Abdul daya gama fidda rai daga fita zargi, kullum addu'anshi Allah yakai haske a kabarin Hajna, mantawa yake da kanshi a addu'anma, addu'anshi kawai Hajna yake mawa, saiya tuna halin daya shigane hankalinshi yake tashi.

     Tuna maganarshi yake da Meerah marecen ranar, tana son kwantar mishi da hankali anma ta kasa ɓoye kukanta.
    "ka kwantar da hankalinka Abdul, koda mun rasa Hujja, Addu'an da muke bazata taɓa faɗuwa a banza ba, insha Allah, Allah zai kawo mana mafita"
     "yanzu shikenan duniya zata ci gaba da kallona a matsayin wanda ya kashe matarshi?"
    "koda duk duniya zata yarda da hakan, ni bazan taɓa yarda ba Abdul...."
   Kukane ya hanata k'arasawa, ta juya zata bar inda yake a rufe.
    "meeerah!!" ya k'wala mata kira, tsayawa tayi ba tare data waigo ba.
       "Nagode Meerah, ngde da taimakon da kikamun, ko bayan raina bazan manta da abunda kikamun ba, inama ace Hajna tana raye? Na tabbata zatayi Alfahri fiye da wanda take na samunki a matsayin k'awarta"
    Bata iya cewa komai ba saboda kukan da take, sai dai ta juya kawai tabar wurin.
     Share hawayenshi yayi ya jingina da bango, inda hawaye na k'arewa shikam da tuni ya daɗe da manta yana dasu, shikenan gobe za'a yake mar hukuncin kisa?
  
Baradai muje mezai faru goben, matsoratan masoyana😜😄😄

©Rabiatu sk msh

HAKKIN KISA 66-70

☠HAK'K'IN KISA☠
      👽👽👽👽
            66-70
©Rabiatu sk msh
      ®NWA

   A gigice ta dawo baya, nan danan kurmin idonta ya canja launi, Karime ta tashi tana rik'ota,
    "lafiya dai Hajia saratu?"
   Ai batasan sanda ta saketa ba sabida wani lafiyayyen mari da taji yaa sauka a fuskanta.
      "A'ahh hajia daga tambaya kuma sai mari?"
  Sannan hajia Saratu ta fara dawowa, "Uban waye ya mareki? Ki barni in tashi in rama naushi na dai"
    "wurin wa? Ni wlhy ban nausheki ba"
  Nan fa rigima ta kaure, kowa yana cewa ɗan uwanshi ne ya dakeshi, suna can hayaniyarsu sai dai sukaji gidan ya cika da wata mahaukaciyar dariya. Cikin wata irin murya aka fara daria.
     Duk suka k'ank'ame juna, suna sauraren ta inda ginin gidan zai fara faɗo musu, gashi sun rasa daga inda dariyan ke fitowa.
    "waye nan? Wake tsorata mu?"
    Aka gaggaɓe da wata irin daria, cikin muryar da tayi matuk'ar razana su akace "daga cikin waɗanda kukayi sanadin mutuwansu ne, na dawo ɗaukan HAKKIN KISANA"

    "mu bamu kashe kowa ba, na rantse da kwarankwatsa ta faɗomun babu wanda na kashe" babu amsa, sai dai dariyar da aka ci gaba dayi, a hankali kuma sai sukaji ashe dariyan daga cikin kwalban ne, duk suka zuba ido suna kallo.
      Sai da wurin yayi tsit, saiga wasu munanan k'wari sun fara fitowa, gasunan ba kyaun gani, bak'ik'irin da jajayen idanun da sunfi jikinsu girma.
   Duk sunyi matuk'ar firgita da ganinsu, gashi suna son su rufe ido kaman an kafesu, kowannensu kyarma yake, sun dunk'ule wuri ɗaya.
   A hankali k'warin suka fara haɗewa wuri ɗaya, suna zama kaman yanayin kai, sai da ya zama k'aton kai, marar kyaun gani ga idanuwa ta ko ina da k'aton baki, ihu kawai suke don ba k'aramin firgitasu yayi ba.

    Nan take ya fara aman k'warin suna zuwa suna baibayesu, ae basusanma sun saki juna ba kowanne ya kama gabanshi yana ta kanshi. Wani irin cizo suke mai gigitawa, gashi in suka kama fata basusan su saki ba, kowannensu ihun azaba kawai yake saida suka fara shinshino mutuwa sannan k'warin suka bar jikinsu kowanne ya jigata.
      Awa Uku suna jinyar wurin da k'warin suka cijesu, ko ina yayi fari tas ba jini, sai dai ko yaya iska ya shiga wurin kaman ana hura wuta suke ji, ko magana ba mai iyayi. Sai da sukasha wahala sosae, sannan wurin ya koma yana haɗewa, tsaf ciwon ya koma kaman ba'a taɓayi ba.
    Cikin mamaki suka tashi suna dudduba jikinsu, kaman babu abunda ya faru.
     "Na shiga Uku ni Saratu, yau mike shirin faruwa dani?"
    "nice nan na shiga tamanin Hajia, ko uwarme ya kawoni gidannan? Wallahi tashi zaki ki fiddani in tafi"
    "inaaa, ae nima bazaki barni ba"
   Ko mayafi bata tsaya ɗauka ba su duka sukayi k'ofan gida da gudu, Hajia Saratu itace me saurin zuwa buɗe gida, tana taɓa k'ofan sai dai taji anyi jifa da ita baya har saida ta dangana da bango, idonta da yasha naushi ta fara lalube, don ji take kaman an k'arasa cireshi.

     Aka k'ara kwashewa da wata gigitacciyar dariya,
     "ae kuda barin gidannan, sai kun shirya zuwa kotu kuyi bayani, ku amsa HAKKIN KISAN dake kanku"
    
     Hajiya karime ta rarrafa inda Hajia saratu take, kaman abun kirki ta sak'ala hannunta cikin nata ta fara ihu.
     "Wayyo Allah mun shiga Uku ni da Hajia saratu! Mun shiga Uku nida Hajia saratu!! Wayyo Allah mun shiga Uku"
    Da wata kakkausar murya akace "Ae babu wanda zai jiyoku balantana a kawo muku agaji"
   Ita dai Hajia Saratu harta fara fita hayyacinta, sama-sama ma take jiyo Karime, ita kuma sai kuka take muryarta ma ta daina fita.
    Suna cikin haka sai dai suka ji an fara janye karime, tana kuka ta mik'a hannu zata rik'o Hajia saratu, anma bata da k'arfin daga ido ta kalleta ma.

©Rabiatu sk msh

HAKKIN KISA 61-66

☠HAK'K'IN KISA☠
      👽👽👽👽
            61-66

©Rabiatu sk msh
      ®NWA

www.babymsh.blogspot.com

  A falonta sukaci karo dasu Muhseen, suma suna shirin shigowa suga idanta tashi shiru bata fito ba, bayansu ta koma ta lafe.
    "Hajna! Hajna ce, wlhy fatalwan Hajna ce bata mutu ba"
    "kamarya bata mutu ba?"
    "nidai bata mutu ba tananan"
   Da dai suka lura a tsorace take, suka zaunar da ita suna mata addu'a harta ɗan samu barci sannan suka fita suka barta.

Maman Abdul
Saukan ruwan da taji jikinta ne ya farkar da ita ta tashi tana ihu sosae, sai da taga Khadija a kusa da ita ne sannan tayi shiru tana zazzare ido.
     "Umma kinyi mafarkin ban tsoro bazaki farka da addu'a ba?"
    "ina take addu'an? Ke kinga abunda na gani kuwa?"
     "A'ah Umma, me kika gani?"
   Shiru tayi tana tunana abunda ya faru a ɗakin, sannan ta fasa ihu,
    "jarirai ne, da kukansu cike da ɗakinnan, Allah na gansu a mirrow"
   Khadija shiru tayi tana tausayin maman tata, anya ba halin da Abdul ya shiga bane keson ruɗata? Don ita gani take maman ta damu da Abdul kawai dai don ba yacce zatayi ne.
      "Umma ki kwantar da hankalinki, mafarkine kawai, ki dinga addu'a zaki samu natsuwa"
    "tohh naji, naji" ta juya a hankali tana kallon mudubi, wata fuskace taci karo da ita marar kyaun gani, an yak'e hak'ora cako-cako ana mata dariya, da sauri ta k'ank'ame fuskanta.
     "kin gani ko, ga mutun can ta mirrow"
   Khadija ta kalla, "Umma babu komai fa, daman keda ke a tsorace kin kalla madubi?"
    "tashi ki rufeshi"
Ta tashi ta ɗauka towel ta rufe.
   "shikenan ko Umma?"
Bata nutsu ba tadai ci gaba da kalle-kalle.

A can wani gida, wata mata ce ta saka roban kaya a gabanta. Wata dake kusa da ita ta karkaɗa kai.
     "lallai Hajia saratu, ina magana anma banda amsa ko?"
    "kikace me?" ta faɗa cikin nuna rashin kulawa.
    "sai yaushene zaki daina wannan harkar ta cutar da mutane?"
    Ta gyatsina fuska ba tare da ta kalleta ba, "shikenan mu haɗu mu daina, in daina harkar da nake ke kuma ki daina samun ido da bak'in ciki"
     "bak'in ciki ne ma nake miki?"
   "tohm da miye? Shikenan tunda kikaga na fara samu  kika bi kika sakamun ido, don kinga babu harkar da takai wannan samun kuɗi a yanzu"
    "kuma babu wanda ta kaita halakar da mutane ba, ke kanki kinsan yana cutarwa anma kike siyarwa"
   "oho akwai wanda nakema dole sai ya siya ne? Abunda sukeso kenan, ko an faɗa musu da illanshi ba daina siya zasui ba"
     "shikenan ke kuma...."
Ta dakatar da ita, "kinga Hajia barira, idan ba cinikayya zata kawoki gidannan ba, don Allah na yafe zuwan naki"
     "nikam Allah ya tsareni da siyen kayannan, nasan ciwon kaina"
   "eeh sai kibar wanda basusan ciwon kansu ba suzo"
    "Hajia saratu yau nice kike ma iyaka da gidanki?"
    "eeh anyi miki, tunda ba son zaman lafiya kike ba"
    "masha Allahu, kinga tafiyatah" ko magana bata k'ara mata ba har tabar gidan.

    Tana fita wata matar na sako k'afa gidan,
     "gafaranki dai Hajia saratu"
   "A'aaah Hajjaju makkatun, sai yau nake ganinki?"
    "Haba duka nayi sati da barin gidannan? Kinsan yanzu in nace zan fita anyita zuwa nemane, yanzu ma don naga na wurina sun kusa k'arewa ne na dawo sari"
       "kinsan kuwa akwai wani na musanman nanan aka kawomun shekaranjia, na hana kowa ke nake ajje mawa"
    "yauwah hajiata, ɗaukomun shi na gani"
    Wata er k'aramar k'walbace ta ciro a kwali ta mik'a mata, ta ansa tana buɗewa kuma tayi baya.
    "yadai hajjaju?"
        "wannan ae tsutsotsi ne"
      "tsutsa kuma? Yanzu fa na ajeshi da hannuna"
    "gashi dai ki gani da kanki"
   Ta mik'a mata, Hajjaju saratu ta kware ido ɗaya ta mak'ale ɗaya tana lek'en cikin kwalba, sai dai taji wani lafiyayyen naushi.

©Rabiatu sk msh

Popular Posts

 
]]>All content on thisblog are copyright protected and cannot be reproduced on other websites without permission.