♠SANADIN K'IYAYYA♠
(︶︿︶)
1-2
©Rabiatu sk msh
NWA
Dedicated to Mrs Umar and Maman Adnan
Tsaye suke bakin titi sai faman chatn take, Ummie ta mik'a hannu zata anshe wayar tayi saurin janye wa, ta buga tsoki,
"Haba Aleesa sai kace bak'uwar chatn? A hanyar ma bazaki saurara ba?"
"kindai jira na gama reply ko? Kinsan dai bada wani k'ato nakeyi ba"
Bata tsaya maida mata amsa ba, ta faɗaɗa fara'arta, "wow! ɗago idonki kiga wata haɗaɗɗiyar mota"
"Miye sunanta?" Aleesa ta tambayeta ba tare data ɗago ba,
"benz ce fa" Aleesa ta kwashe da dariya, "benz ɗin zan ɗago gani, kinsan dai nama tsani motar?"
"Na sani, kece fa kike cewa ba'a cika samun mota yellow colour ba" inji ummie
"ke nifa ba son ganinta nake ba, kinsan yanda nakejin haushin colour ɗin,"
Shiru tayi ta k'yaleta, ta rii
ga da tasan halin Aleesa idanta kafe kan Abu, sai data ajiye wayar don kanta, har lokacin basu samu abun hawa ba,
"kinga motar nan bansan inda ta shige ba?" Aleesa banza ta mata don taa fara bata haushi,
"Mota kamar babu gidanku Ummie?"
"ta burgeni ne sosae, kalan ba'a cika samunta ba"
"yauwah kin ganta nanma ta taho, don Allah ki kalla"
"ke wlhy bazan kalla ba" Aleesa ta faɗa don Ummie ta fara k'ureta,
"Munfa kusan Makara Ummie, anya zamu samu lecture nan?"
"nima tunanin da nake kenan, anya bazamu hau mashina ba?"
"A'ah ni bazan hau ba"
K'aran buɗe mota sukaji, Ummie ta dinga taɓo Aleesa anma tak'i waigawa,
"kefa banza ce, mai motarnan ne ya tsaya"
"don Allah ki daina, karma yace mun damu dashi..." maganarta ta rik'e saboda ganin mai motar ya buɗe hardasu fitowa, ya nufo inda suke yana washe baki kamar gonar auduga,
Daga nesa hasken hak'oran kawai nake hangowa, bak'ine sosae, da sajenshi da yafi gashin gemun tsayi, sai kanshi yasha rantali ko hula babu, sannan kuma idonshi ɗaya nada er matsala, ba wani babba bane sosae, irin 30yrs haka, yana sanye cikin bugaggiyar shadda yellow, ta mishi kyau sosae a jiki, a fuska ne kawai baida k'oshin kyau,
Aleesa da ganinshi ta fara dariya harda duk'ewa, bata damu da a bakin titi suke bama, Ummie kamar ta nutse don kunya, ta fara taɓota anma kamar batasan tanayi da ita ba, har ya k'araso inda suke,
A hankali cikin sanyin murya yace "Sannunku en matah"
"Yauwah, ina wuni" inji Ummie,
"lafiya lau," ya amsa yana kallon Aleesa da har lokacin dariyarta kawai take,
"da alama yau abun hawa yayi wuya, kuma bai kamata en matah kamarku sunashan ranarnan ba, idan kun yarda zan kaiku har inda kukeso"
"Ba komi ai bamu daɗe da fitowa ba, zamu samu insha Allah"
Aleesa ta kalleshi shek'ek'e, ta k'ara tuntsurewa da dariya,
"Anma dai ba donmu shiga ka tambayemu ba ko?"
"Idan na rasa k'warin gwiwa ai bazanma tsaya ba"
"A'atoh, don koda mun rasa abun hawa bazamu shiga motarka ba, kai don Allah ko kunya bakaji ba ka tsaya wurinmu?" Ummie ta ɓata rai tana kallonta
"Haba Aleesa ba haka akema mutane ba, don Allah ki daina?"
"Dole ne sai nayi abunda kowa keyi? Wannan ma ai cin mutunci ne ace kamarshi ya rage mana hanya, jibarshi fa abun tsoroma dashi"
"Haba Aleesa, wai miye haka?"
"kaga malam zaka kama hanya koko?"
"hak'uri zaki hajia, naga alaman kamar kina cikin ɓacin rai"
Harararshi tayi son ranta, sannan ta tsaida mai napep ɗin da taga ya taho, ko saurarar Ummie batayi ba ta wuce ta shiga,
"kayi hak'uri fa, ba halinta bane...."
"ba komi na fahimceta, daman ya za'ai kyakkyawa kamarta tayi faɗa haka, anma gida zakuje ne?"
"A'ah makaranta dai, daga gidan muke"
"owk, ban sani ba ko zaki taimakamun da kwatancen gidansu? don daga ganinta nema zuciyatah ta tilastamun tsayawa "
"Malama zakije ne, ko saikin gama kallon bak'in Akuyar nan?" yaji ciwo sosae anma ya kanne, da hannu Ummie ta nuna mishi gidansu Aleesa,
"Yauwah nagode, don Allah ki k'ara bama k'awarki hak'uri," ta ɗaga mishi kai sannan taje ta shiga napep ɗin,
A makaranta mai napep na saukesu, ta fito da sauri ta baro Ummie na sallamarshi, sai sauri take taje hall ɗin da suke lecture don lokaci ya kusan cika, bata ankara ba taji ta kusa karo da abu, tayi baya da sauri sannan ta ɗago kanta, take sauran fara'ar dake fuskarta ta ɓace,
"Kai wani irin dabba ne, da bakajin kunyar shiga hanyar mutum?"
"Dabba kuma Aleesa? Yanzu cin mutuncin har yakai haka?"
"Yamafi haka idan har bazaka daina shiga rayuwatah ba"
"bazan taɓa dainawa ba kuwa, don Soyayyar da nake miki a shirye nake dana karɓi duk wani cin mutunci naki, don nasan dole wata rana zaki soni"
"Allah ya sauwak'emin, don kana da kyau da kuɗi, banga dalilin da zaisa in soka ba, en matan dake kulaka ma na tausaya musu"
"ki fara tausaya ma kanki kema" ya faɗa yana wani shu'umin murmushi,
Ta wuceshi zata tafi, yasha gabanta, "ya zaki tafi bamu gama magana ba?"
"banson iskanci Hadid ka matsamun a hanya"
"idan nak'i fa?" kafin ya rufe baki yanata wani murmushi ta ɗaukeshi da zazzafan mari, abinda bai taɓa tunani ba daga gareta,
Ɗagowa yayi dafe da kuncinshi, idanunshi sunyi jajir da ɓacin rai, ya waiga ko ina, ba laifi mutane sun taru, kuma duk hankalinsu na wurinsu suna daria ciki-ciki,
Ummie taja hannunta "Menene kika yi Aleesa? Kina manta halin hadid ko"
"Ke Malama naga duk kin wani ruɗe, ke kin manta nawa halin ne?"
"ba mantawa nayi ba, anma gaskiya baki kyauta ba"
"ban taɓa dana sanin abunda nayi dana sani ba Ummie, wata k'ila wannan zai sanya ya fita hanyata"
"Allah yasa tohh"
A haka suka k'arasa hall ɗin, suna fira, sunyi sa'a saida suka shiga lecturer n ya shigo,
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment