♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
72
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
A daidai wannan gab'an kam Saude baza ta iya wa momie k'ariya ba kamar yanda zuciyar ta ke zuga ta, amma toh Idan tayi na'am da wannan tambayar me ze biyo baya, wani irin kallo momie zata yi Mata? kallon maci Amana ko kuma mak'aryaciya? "Amsar ki nake jira kuma kinyi shiru Saudat" Momie ta katse mata tunanin da take. Tuni hawaye sun wake mata fuska, ta watsa wa yasseer wani kallo zuciyar ta na tsananin bugawa, Sannan cikin raunannan murya ta ce "Gskia ne momie, yasseer ya Kasan ce miji na a da can baya but not any more! ta karashe maganar da d'an k'arfi tana kallon yasseer da tuni idanun sa suka dawo jaa da jin kalaman ta na k'arshe.
Kafafuwan Najib ne suka kasa d'aukan sa, wani nauyi yaji kan sa na masa kamar ze fad'i yyi saurin zama dirshan akan rug carpet din dake d'akin, ya tallafo kan sa da hannayen sa biyu a hnki bakin sa na furta "innadillahi wa'inna ilaihir rajiun". Wannan shine Kalmar da momie ma ke furta wa, hankalin ta yayi dubu ya tashi ta shiga safa da marwa acikin d'akin.
"Har Yanzu ke MATATA CE Saude! matsayin ki bazai tab'a chanja wa ba agurina, Dan Allah kiyi hakuri Kar kiyi min hukunci me tsauri haka, I know I deserve even more than this but pls kiyi min aikin gafara ko Dan albarkacin 'yar mu da muka Haifa tare".
"Wace 'ya??" ta wurga masa tambayar
"Hafsat mana, ko kina nufin hafsat ba 'ya ta bace?"
"Ae hafsat bata da wani uba daya wuce wannan" ta nuna najib dake zube agurin
"Saboda shi ta sani kuma shine ya yi Mata rik'on mahaifi kuma ya dawo da mahaifiyar ta cikakkiyyar mutum alokacin da kaii ka guje mu"
Yasser ze yi magana momie ta dagatar dashi cikin b'acin rae tace "Duk ku dakata! wannan bashi bane, meyasa kika boye mana wanan BOYAYYEN AL'AMARI Saudat?"
K'afan momie tazo ta Kama tana durkushe cikin muryan kuka tace "Dan Allah momie kiyi hkri, nayi gudun fad'a muku ne kuyi tunanin wani mugun halin gareni yasa miji na ya gudu ya barni, naji tsoron Kar kuki k'arba ta alokacin da bani da wani inda Zan je, shi ya......"
Najib ya katse ta "Sam! wannan ba hujja bace Saudat! I cnt bliv abunda kunne na suka jiyo min" ya Kai hannu ya d'ago ta daga durkushen da tayi suna fuskanta juna kowannen su da rinanne ido
"Idan zaki iya b'oye wa momie then why me! I tout ni dake ayanxu mun zama d'aya da zaki iya fad'amin duk wani Abu naki tunda I'm ur soon to be husband"
"Ya yasseer ba miji na bane ayanxu, yana da matar sa me kaunar sa haka nan nima wallahi Kai nake so ya Najib, Dan Allah karka gujeni masoyi nasan..."
"Ni wallahi duk kun rud'a ni yaran nan, Yanzu ya kuke so mu b'ullo wa wannan sabon Al'amarin, da wani ido zamu kalli mutane kuma me kuke so nayi adaidai wannan lokaci da bai fi awa guda ba a daura aure."
Cewar momie...
"A dakatar da auren nan momie, Dan wallahi Saudat MATATA CE, da aure na akanta har Yanzu"
Najib juyawa kawai yayi zai bar ɗakin, Momie na kiran shi amma ko ya saurareta, sai da Saudat ta sha gaban shi Sannan ya tsaya yana sauke ajiyan zuciya "Pls Kar ka barni masoyi! wallahi ni kai nakeso kuma Kai Zan aure"
wani zafi yasseer yaji azuciyar sa, se alokacin yake k'ara gani wautar sa da yyi abaya.
"Ta yaya Zan aure ki bayan kuma da auren dan'uwa na akan ki, yaya ma Zan yi tunanin rayuwar aure da matar da ta Kasan ce tayi tarayya da dan'uwa na a matsayin matar sa, noo I can't! yana Kai wa nan yasa Kai ya fita momie bata Hana shi ba, ta ma rasa ta inda zata fara tackling problem d'in.
Sai ma tashi tayi itama ta fita zuciyar ta Sam Babu dadi, tana tunanin yanda zata Fara warware wannan matsala data kunno Kai a kurarren lokaci.
Tana fita yasseer ya zube akan gwuiwoyin sa yana ba wa Saudat hakuri data yafe mishi akan kuskuren da tafka a baya, ko kallon shi bata yi ba ta cigaba da rera kukan ta yana taya ta. Gaba ɗaya jin haushin zamanshi gabanta take.
"Ka yi min raunin da bazai tab'a warkewa ba Yasseer, na jima ina jiran dawowar ka garemu ni da 'yar Dana haifan maka but u kept me waiting all dis years, Idan nace a baya ban son ka toh nayi wa zuciya ta k'arya amma wallahi tunda zuciyata ta amshi soyayyar Najib na shafe duk wani Abu da nake ji akan ka wannan yasa nayi pretending kamar ban gane ka ba tun ranar da idona ya sauk'a akan ka"
"Plx Kar kice haka Saude nasan kina fushi Dani ne har yanzu, I know ni ki ke so ba Najib ba Dan nine Mijin ki"
"Baka so na, kama san meye so Ya Yasseer? In har kana ma mutum soyayyan gaskia bazakaji kunyan nunashi koma a ina bane, da kana sona baza ka ji tsoron gabatar Dani ga iyayen ka ba har ka gudu ka barni kaje can ka auri wata ba"
"Wallahi ina son ki, ina kaunar ki Saudat! ya Kai hannu ze rik'e ta, tayi saurin juya wa ta bar d'akin, Kai tsaye ta bi back door ta fita ta can wani b'angare na bayan gidan inda Bbu mutane nan ta had'a Kai da gwuiwa ta kuka na sosae...
Tana fita shima ya fice zuciyar sa na tafarfasa kamar zai fito daga k'irjin shi, Kai tsaye yyi motar sa dake can wani side na parking space d'in gidan, nan ya shiga ya fice daga harabar gidan daya cika da mutane. Ko kad'an Yasseer bai San inda ya nufa ba shi dae kawae yana zuba gudu akan titi kmr ze tashi sama, titin by pass ya dauka wato can ta bayan gari zuciyar sa na tsananin yi masa ciwo, idon sa ya chanja sosae har kamar baya gani sosae, a hnkli ya rufe idon ya sake bud'ewa Bbu abunda yake tunano wa kamar yanda Sauden shi ta chanja, ta murje zuwa had'ad'd'iyar mace me suna Saudat. Tuni yayi nisa da fad'a wa duniyar tunani, wannan yasa bae ga motar da ta sako Kai ba alokacin da yayi over taking....
Momie ba k'aramin ruɗewa tayi da jin labarin accident ɗin Yasseer ba, gaba ɗaya kanta ya ɗaure batasanma me take faɗama taron mutanenta ba, kawai dai tace "an fasa ɗaurin auren, babban ɗanta yayi accident" mayafinta a hannu tabi driver zuwa Asibitin da aka kwantar dashi, tare da wasu en ɗaurin auren, gaba ɗaya gidan yaa rikice.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment