☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
61-66
©Rabiatu sk msh
®NWA
www.babymsh.blogspot.com
A falonta sukaci karo dasu Muhseen, suma suna shirin shigowa suga idanta tashi shiru bata fito ba, bayansu ta koma ta lafe.
"Hajna! Hajna ce, wlhy fatalwan Hajna ce bata mutu ba"
"kamarya bata mutu ba?"
"nidai bata mutu ba tananan"
Da dai suka lura a tsorace take, suka zaunar da ita suna mata addu'a harta ɗan samu barci sannan suka fita suka barta.
Maman Abdul
Saukan ruwan da taji jikinta ne ya farkar da ita ta tashi tana ihu sosae, sai da taga Khadija a kusa da ita ne sannan tayi shiru tana zazzare ido.
"Umma kinyi mafarkin ban tsoro bazaki farka da addu'a ba?"
"ina take addu'an? Ke kinga abunda na gani kuwa?"
"A'ah Umma, me kika gani?"
Shiru tayi tana tunana abunda ya faru a ɗakin, sannan ta fasa ihu,
"jarirai ne, da kukansu cike da ɗakinnan, Allah na gansu a mirrow"
Khadija shiru tayi tana tausayin maman tata, anya ba halin da Abdul ya shiga bane keson ruɗata? Don ita gani take maman ta damu da Abdul kawai dai don ba yacce zatayi ne.
"Umma ki kwantar da hankalinki, mafarkine kawai, ki dinga addu'a zaki samu natsuwa"
"tohh naji, naji" ta juya a hankali tana kallon mudubi, wata fuskace taci karo da ita marar kyaun gani, an yak'e hak'ora cako-cako ana mata dariya, da sauri ta k'ank'ame fuskanta.
"kin gani ko, ga mutun can ta mirrow"
Khadija ta kalla, "Umma babu komai fa, daman keda ke a tsorace kin kalla madubi?"
"tashi ki rufeshi"
Ta tashi ta ɗauka towel ta rufe.
"shikenan ko Umma?"
Bata nutsu ba tadai ci gaba da kalle-kalle.
A can wani gida, wata mata ce ta saka roban kaya a gabanta. Wata dake kusa da ita ta karkaɗa kai.
"lallai Hajia saratu, ina magana anma banda amsa ko?"
"kikace me?" ta faɗa cikin nuna rashin kulawa.
"sai yaushene zaki daina wannan harkar ta cutar da mutane?"
Ta gyatsina fuska ba tare da ta kalleta ba, "shikenan mu haɗu mu daina, in daina harkar da nake ke kuma ki daina samun ido da bak'in ciki"
"bak'in ciki ne ma nake miki?"
"tohm da miye? Shikenan tunda kikaga na fara samu kika bi kika sakamun ido, don kinga babu harkar da takai wannan samun kuɗi a yanzu"
"kuma babu wanda ta kaita halakar da mutane ba, ke kanki kinsan yana cutarwa anma kike siyarwa"
"oho akwai wanda nakema dole sai ya siya ne? Abunda sukeso kenan, ko an faɗa musu da illanshi ba daina siya zasui ba"
"shikenan ke kuma...."
Ta dakatar da ita, "kinga Hajia barira, idan ba cinikayya zata kawoki gidannan ba, don Allah na yafe zuwan naki"
"nikam Allah ya tsareni da siyen kayannan, nasan ciwon kaina"
"eeh sai kibar wanda basusan ciwon kansu ba suzo"
"Hajia saratu yau nice kike ma iyaka da gidanki?"
"eeh anyi miki, tunda ba son zaman lafiya kike ba"
"masha Allahu, kinga tafiyatah" ko magana bata k'ara mata ba har tabar gidan.
Tana fita wata matar na sako k'afa gidan,
"gafaranki dai Hajia saratu"
"A'aaah Hajjaju makkatun, sai yau nake ganinki?"
"Haba duka nayi sati da barin gidannan? Kinsan yanzu in nace zan fita anyita zuwa nemane, yanzu ma don naga na wurina sun kusa k'arewa ne na dawo sari"
"kinsan kuwa akwai wani na musanman nanan aka kawomun shekaranjia, na hana kowa ke nake ajje mawa"
"yauwah hajiata, ɗaukomun shi na gani"
Wata er k'aramar k'walbace ta ciro a kwali ta mik'a mata, ta ansa tana buɗewa kuma tayi baya.
"yadai hajjaju?"
"wannan ae tsutsotsi ne"
"tsutsa kuma? Yanzu fa na ajeshi da hannuna"
"gashi dai ki gani da kanki"
Ta mik'a mata, Hajjaju saratu ta kware ido ɗaya ta mak'ale ɗaya tana lek'en cikin kwalba, sai dai taji wani lafiyayyen naushi.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment