☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
1-5
©Rabiatu sk msh
®NWA
www.babymsh.blogspot.com
Wani babban gidane na hango ɗan madaidaici, cike da mutane har waje, masu kuɗi harda masu k'aramin k'arfi shiga kawai suke suna fita, ga motocinan birjik har basu gajiya da tsayawa, lallai da alama gidannan bikine ake, biki na er gatah ma kuwa, bazan iya wucewa ban bawa idona abinci ba har in samu labarin kawowah Masoya.
Kai tsaye na kutsa cikin gidan, lallai na zaune baiga gari ba, manyan mata ne a wurin masu ji da kansu, ga Uwar Amarya da keta tarban bak'i, ni kaina na samu karramawa, dana zauna kwasar girki ma saina manta da abunda ya kaini, sai dai naji ana hayaniyar kai amarya, da hanzari na na mik'e, don dolene ma inje gidan amaryarnan.
*****
Ankai Amarya tsantsareren gidanta, sai da kowa ya gama tafiya ya rage ita da k'awayenta, Ango da abokanshi sukazo, saida suka gama tsokana, da suka tashi tafiya suka musu nasiha sosai mai ratsa jiki, basu daɗe ba suka tafi, don Ango kamar ya korasu saboda zumuɗi.
Saida ya rakasu ya dawo yana gyara babban riga, sai washe baki yake irinna angwaye,
"Amaryata, bayan kuɗin siyan bakinma baza'a buɗen fuska ba?"
Hannu tasa zata yaye mayafin, ya ɗaura hannunta saman nashi suka buɗe a tare, "wao! Masha Allah, Godia ga Ubangiji daya mallakamun wannan kyakkyawar mace a matsayin Matatah"
Murmushi tayi har kyawawan hak'oranta suka fito, "Gaskia nayi dace Hajna, taya zan bayyana miki farin cikin da nakeji yau gani tare dake a matsayin Matah da miji?"
"bakai kaɗai ba Masoyi, burinmu ne mu duka ya cika, yanzu sai mu fara mik'a godiyarmu wurin Allah (S.W.T) daya bamu ikon ganin wannan rana"
"Yanda kikace Amaryatah" ya rigata mik'ewa, tabi bayanshi da kallo, harya shige toilet, wani soyayyarshi na k'ara shigarta, zuciyarta tanason Abdul da yawa, kyakkyawan saurayine da kowacce mace zatayi mafarkin samu, tananan tana sak'ar zuci harya fito, sannan ta mik'e tayo Alwalan itama.
Gado ta haye kawai ta juya baya ta kwanta bayan sun gama, "Nifa ban yarda da k'oshinnan ba, nasan hidima bazaki samu lokacin da zakici komi ba, plz indai baso kike in ɗura miki ba"
"Allah da gaske na k'oshi," ita tsakaninta da Allah ta k'oshi, shima bai wani ci kazar da yawa ba ya ajje, kayan jikinshi ya rage sannan ya haye gadon shima.
"bazaki rage kayannan ba?"
"um-um sanyi ake"
Jawota yayi ta faɗa jikinshi, "sai in rufeki anan" ɗan tureshi tayi zata juya, ya matseta gam, a hankali yake mata magana a kunne cikin raɗa, "karki barni plz, ki tsaya a haka" cikin sexy voice, gaba ɗaya ya kashe mata jiki, tunnan numfashinta ya canja, ta k'ara shigewa jikinshi.
"kayannan ya miki nauyi" ya k'ara raɗa mata a kunne, jin ko motsi batayi ba ya fara rabata dasu, sannan ya jawo bargo ya rufesu, tana manne a jikinshi sai shafa bayanta yake ita kuma tana k'ara manne mishi. A hankali duk ya rabata da kayan jikinta.
Rikicewa yayi ya fara wasa da jikinta, tun tana mak'alewa har itama ta saki jikinta, wani salo mai k'ara rikitarwa yake zo mata dashi, duk da hakan dak'yar ya shigeta, batasan sanda ta fasa wani uwar k'ara ba, sannan ma ya jishi a wani sabuwar duniyar, ya k'ara k'aimi ihu kawai take, tun tana toshe baki harta farayi da k'arfi tana jin wani azababben ciwo, inaa Abdul baimasan tana yi ba.
K'arshema kasa ihun tayi, koda yaga jini a jikinta bai ɗauka wani abu bane, kowacce cikakkiyar mace ance hakanne a daren farkonta, wani k'arfima yakeji yana k'arazo mishi, a tak'aice dai bai k'yale Hajna ba sai ana kiran Sallahr Asuba, ya kwanta samanta yana maida numfashi.
Ko kaɗan bai kula da numfashinda ta dainayi ba saida ya dawo hankalinshi, ya mik'e yana dubata jinine kaca-kaca a jikinta, gadon ya ɓaci sosai, a ruɗe yake kallon jini, sannan ya fara taɓata ko motsi batayi.
Cikin k'arfin hali ya ruga fridge ya ɗauko robar ruwan faro mai sanyi sosai, ya juye mata anma ko motsi batayi, duk kallon abun yake kamar a mafarki, ya ɗan kwantar da kanshi a k'irjinta anma babu alamun numfashi?
Hannuwanshi ya ɗaura saman kai ya fasa ihu, jikinshi har kyarma yake yana hawaye, TA MUTU NE KO SUMA TAYI?? ya tambaya kanshi.
Bai hak'ura ba ya sauka ya fara jijjigata da hannu, kaman yana jijjiga filo ne ba wani motsin kirki, kaman zautacce ya fara zagayen gidan, duk wani taimakon gaggawa da yake tunanin zai saka Hajnarshi ta tashi yaa bata anma shiru, duk inda tashin hankali yakai yaa wucenan.
Tunani ya fara yi, ya kira likita ne ko kuma ya kira sauran dangi? Da yake baima da lokacin tunanin bai tsaya shawara ba gaba ɗayansu ya kirasu, yana ganin kiran mahaifinshi da sauran dangin amarya, bai iya ɗaga na kowa ba tunda ya samu ya faɗa musu suzo ba lafiya.
Kusan tare suka iso, mahaifanshi da nata, da kuma likitan daya ma waya, ya sakata a gaba hannuwanshi saman kai, zufa kawai yake gaba ɗaya babu k'walla a idanunsa.
Turus sukai suna kallonshi zaune ya tasa Hajna a gaba, "lafiya meya faru?" mahaifinshi ne ya watso mishi tambayar.
Shi kanshi baisan meya faru ba, ballantana yasan amsar dazai basu, da hannu kawai ya nuna musu Hajnar dake gabanshi.
Ummanshi tace "Hajna ba? Munga Hajna ce, dalilin kiran daka mana duk ka tada mana hankali mukeson ji"
Maman Hajna ce ta saki jikkarta tana ihu bayan hango jini malala jikin Hajna, sannan ta lura da shima jinin yanda duk ya ɓata shi, "Na shiga Uku, wannan jinin ko ai ya wuce lafiya? Meka ma 'yata?"
Sannan duk suka k'arasa saman kanta yanda ta kakkahe babu alamun numfashi a jikinta.
Yanda Mamanta ta cika gidan da ihu tana maganganu, duk ya k'ara ɓata ma Abbanshi rai, ya kalla likitan, "Me kake jira? Ka dubata musan meke faruwa da ita"
"tohm Alhaji" da sauri ya k'arasa inda take, en gwaje-gwaje kawai ya mata sannan ya ɗago duk yana kallonsu, duk ya haɗa zufa.
"kai muke saurare, ka faɗa mana meya sameta?"
"bazan iya ganewa ba Alhaji, abunda dai na sani, AMARYA HAJNA TA RIGAMU GIDAN GASKIA"
take ɗakin suka ɗauka salati gaba ɗaya, banda Abdul~azeezu da k'afafuwanshi suka kasa ɗaukansa, ya tafi luuu zai faɗi, Maman Hajna ta cakumoshi.
"k'arya kake wallahi, kai baka isa ka kashe mun y'ata ba, wallahi baka isa ba, y'atah bzata mutu ba"
Duk da Abbanshi shima cikin tashin hankalin yake, saida yace "Hajia kudai iya kalaminku"
"kalamim banza da wofi, naqi in iya kalamin, a gabanka fa, jiya da dare aka kawo mishi y'ata, daga shi sai ita, yau sai gawarta zai nunamin? Wallahi baka isa ba saika faɗamun abunda ka yima y'atah"
"Magana ake maka, ka barmu cikin duhu me kayiwa matarka? Meyasa ka kasheta?"
Da sauri ya ɗaga kai yana kallon Abban nashi cikin mamaki ne ko firgici,
Mamanta tace "mefa zata mishi, kawai jininta ya bayar, ni daman nasan kuɗinnan da yayi da wuri ba banza ba, wallahi jinin ɗiyata bazai tafi a banza ba"
A hankali yake furta, "Hajna ta mutu? Shikenan kin tafi kin barni? Daman kin shigo rayuwatah ne dan ki barni cikin k'unci da kaɗaicin rashinki?"
Don tsabar haushi Abbanshi ya ɗauka kwalban humranta ya mishi jifa samankai duk ta tarwatse, take shima fuskarshi ta fara zubar da jini.
"Mu zaka maida sakarkarun banza? Tambayarka ake a ina ka bayarda jininta?"
"Jininta kuma? Wallahi tallahi ni badan yankan kai bane, na rantse da Allah Abba nima bansan komai game da mutuwar Hajna ba"
Wayanshi ya ɗauka yana kiran police, "idan kaje zaka musu bayani ne"
Yama rasa mezai faɗa ya kare kanshi, kallonsu kawai, Ummanshi kam duk zuwanta batace komai ba, suna gani aka tafi dashi police station, ita kuma aka wuce da gawarta asibiti donyin binciken musabbabin mutuwanta.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment