☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
26-30
©Rabiatu sk msh
®NWA
Tana shiga Falo ta iske duk k'annenta suna jiran shigowan ta, sai wannan ya kalla wannan suyi dariya, ta ɓata rai "ku kuma miye kuke ma daria"
Alhassan yace "kawai muna taya Ya Abdul murna ne, yau ya cira tuta har auntie ta tsaya fira dashi"
Muhseen Yace "kinga kuwa yanda fira ke miki kyau auntie? Hakanan baki kula kowa duk farin jinin nan naki"
Alhassan ne ya sake bashi amsa, "ba firan ne ya mata kyau ba, kawai dacewa ne da sukayi"
Tsagal Maryam tace "Hakane fa Yaya"
Alhusein da son girma ya harareta, "ke rufe ma mutane baki manyanki na magana" taja baki ta lafe ta kwanta. Haka suka gama firansu cikin nishaɗi, kowa dai ya yaba da Abdul.
Koda ta shiga ɗakin Mama, tambayanta kawai tayi "waye mahaifinshi?"
Sanannan mutum ne indai ka kwana ka tashi zakasanshi a garin kano, yana da kuɗi sosae da kyauta, ga mutunci da halin taimako duk inda yaji ana buk'ata.
Cikin ɗan lokacin da Abdul yayi kafin ya koma makaranta sukayi sabo sosai da k'annen Hajna, ko da ya koma ma kullum suna gaisawa harma da mamanta, Ummanshi har gida ta turo da Khadija ta tafi mata da Hajna, tayi matuk'ar yabawa da halinta, yarinya mai kunya da nutsuwa dai dai matan da take ma Abdul ɗinta fatan samu. Zumunci sosae ya shiga tsakanin dangin biyu.
*** ***
Hayaniyar da yaji ne ta dawo dashi daga dogon tunanin daya tafi, muryar mace yakeji da mai tsaronshi, kaman yasan muryan anma ya kasa tuna ko na waye
"kiyi hak'uri hajia, doka ce babu wanda zai shiga ganinshi"
"ni kuma dolene na ganshi kota yaya, ko kwana ya kama inanan har saina ganshi"
"ki taimakeni Hajia karkimun silar aikina"
"nawane Albashin naka?" cikin gatse ya faɗa mata kuɗin da sunmafi albashin nashi, ta ajje mishi wanda suka ninka abinda ya faɗa.
"anma dai bazaki daɗe ba ko hajia?"
Ta ɗaga mishi kai, yana washe baki ya rakata har inda Abdul yake, daman idanunshi a hanya, da mamakinshi yake kallonta.
"Meerah?"
"Abdul kaine ka koma haka?"
Tuni hawaye ya gama wanke mishi Fuska, "Meerah k'awarki ta tafi, Hajna ta tafi ta barni"
Duk yanda taso danne zuciyarta saida ya sakata kuka,
"kayi hak'uri Abdul, kwatsam daga komawata sai naji wannan mummunan abu daya faru dkai, abinda ya maidoni garinnan kenan, ni kaina na yarda bazaka taɓa kashe Hajna ba, shiyasa ko nawa zan kashe saina nema maka lawyer, dole ne ma a gano waye yake da HAKKIN KISAN Hajna"
"wannan wata tatsuniyah ce da ni kaina na fito daga cikinta, bani buk'atan wani lawyer ko wnda zai kareni, a halin yanzu nafi son na mutu na tararda Hajna can mu sake wani zaman, bzan iya rayuwar da babu Hajna a ciki ba"
"kasan kuwa me mutane suke faɗa a kanka Abdul? Ka daure ka bani haɗin kai Abdul, karda abunda ya faru da Hajna ya sake faruwa da wasu matan, ka bari mu gano waye silan mutuwanta?"
"NINE!!" ya faɗa cikin k'araji, sannan ya sassauta murya, "babu wanda yayi silan mutuwan Hajna bayanni Meerah, ko baki fahimci labarin bane? Na daina jin haushin duk wanda zai dangantani da mutuwanta, Inajin ihun Hajna meerah, tana kuka anma na kasa k'yaleta, wlhy da nasan Hajna zata mutu bzan taɓa kusantarta ba, Allah kaɗai yasan dalilin mutuwan Hajna"
"kuma shine zai fitar dakai, nasan bazaka taɓa kashe Hajna ba, na yarda dakai Abdul koda kuwa kaine ka faɗamun da bakinka, kada ka saduda, karka taɓa amsa laifin da ba naka ba,"
"na gode da yardar da kikamun Meerah, kece mutum ta biyu data yarda da ban kashe Hajna ba, hatta iyayena sun juyamun baya, har sun saka na fara shakku akan kodai nine na kasheta"
"insha Allah ko waye yake da HAKK'IN KISAN Hajna sai ya bayyana kanshi"
"ta yaya?"
Ta saukar da numfashi, tana kallon Abdul duk ya koma kalan tausayi, tabbas abun a tausaya mishi ne, ita kanta shaidane akan son da yake ma Hajna, rashinta kaɗai ya isa ya saka rayuwanshi cikin ruɗu, ga kuma HAKKIN KISANTA da akeson ɗaurawa kanshi.
"Hajia lokacinki ya cika," ta jiyo muryanshi daga bayanta.
A raunane da k'ara kallon Abdul bayan ta mik'e, "na tafi Abdul, saina sake dawowa tare da lawyer" bai iya ce mata komai ba, saboda kukan da yaci k'arfinshi, itama tana kuka ta tafi.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment