☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
71-75
©Rabiatu sk msh
®NWA
www.babymsh.blogspot.com
Wattpad
@Rerbeeart_sk
Abubuwan Maman Hajna sun fara munana, ko ita kaɗai take zaune kaman mai shirin zaucewa, ta ringa ihu tana faɗin Hajna ta dawo a fatalwa zata kasheta. Sai su Muhseen sun ringa rufe mata baki, buge hannun take.
"ku barni in faɗa, Hajna ce ta dawo ba kowa ba"
Sai dai suyi shiru kawai suna kaɗa kai.
A daren Ranar da za'a koma kotu, tana zaune Umman Hajna da k'aton carbi tana ja, batasan ma me take faɗa ba tunda hankalinta ba wurin yake ba.
Giftawan mutun take gani, ta k'ara zare ido tana ci gaba da jan cazbahanta da sauri, nan da nan zufa ta fara karyo mata, ta buɗe baki da k'arfi tana karatun da batasan ma me take faɗa ba, sai dai taga tsayuwan mutum a gabanta, ta kasa ɗago kanta, sai dai taji kaman an ɗago da kanta.
Kallon mummunan fuskan take jikinta na kyarma ko ina, har ya suɓuce a hannunta.
"Kin shirya zuwa kotun kiyi bayani kuwa"
"don Allah kimun rai, wallahi na tuba na daina"
"karma ki tuba ɗin, Gobene zaman k'arshe a kotu, babu wanda yasan gaskia saike, don haka idanma baki je kinyi bayani ba..."
"Hmm nice nan zan ɗauka hukunci da kaina"
"zanje, zanje wallahi...."
Kafin ta gama rufe baki fatalwan ta ɓace.
Umman Abdul na kwance gefen Abbanshi, tuni yayi barci ya shareta, yanzu kwata-kwata barcinta bai wuce na minti biyar, sama-sama tanayi tana tashi dube-dube.
Can idonta yakai kan madubi, rubutu ne da jan pen an rubuta.
"Idan har kinason ci gaba da rayuwa, ki faɗi gaskia a gaban kotu gobe"
Jikinta na kyarma ta fara tattaɓa Abban Abdul, yana jinta ya mata banza, don ya riga da yasan halinta haka zasu kwana fana firgita sai ya tashi babu komai, tun tana tadashi a hankali harta fara dukanshi tana kuka.
Tashi yayi a harzuk'e, "miye kuma? Meya faru?"
Hannunta na kyarma take nuna mishi mirrow, kaman yanda ya zata, babu komai.
"miye a jikin mirrown?"
"Gashinan, rubutu ne, wlhy kasheni zatayi?"
"wacece? Ni banga rubutun komai ba"
Ta juya tana nuna mishi, itama bata ga komai ba, ta rirrik'eshi tana kuka kawai. Shareta yayi ya tashi ya shiga toilet ɗauro Alwala.
Daren ranar dukkansu kwana sukayi saman sallaya, Meerah, Khadija, Abban Abdul, da kuma Abdul ɗin, kowannensu Addu'an neman nasara yake mishi akan shari'ar da zasuyi gobe.
Banda Abdul daya gama fidda rai daga fita zargi, kullum addu'anshi Allah yakai haske a kabarin Hajna, mantawa yake da kanshi a addu'anma, addu'anshi kawai Hajna yake mawa, saiya tuna halin daya shigane hankalinshi yake tashi.
Tuna maganarshi yake da Meerah marecen ranar, tana son kwantar mishi da hankali anma ta kasa ɓoye kukanta.
"ka kwantar da hankalinka Abdul, koda mun rasa Hujja, Addu'an da muke bazata taɓa faɗuwa a banza ba, insha Allah, Allah zai kawo mana mafita"
"yanzu shikenan duniya zata ci gaba da kallona a matsayin wanda ya kashe matarshi?"
"koda duk duniya zata yarda da hakan, ni bazan taɓa yarda ba Abdul...."
Kukane ya hanata k'arasawa, ta juya zata bar inda yake a rufe.
"meeerah!!" ya k'wala mata kira, tsayawa tayi ba tare data waigo ba.
"Nagode Meerah, ngde da taimakon da kikamun, ko bayan raina bazan manta da abunda kikamun ba, inama ace Hajna tana raye? Na tabbata zatayi Alfahri fiye da wanda take na samunki a matsayin k'awarta"
Bata iya cewa komai ba saboda kukan da take, sai dai ta juya kawai tabar wurin.
Share hawayenshi yayi ya jingina da bango, inda hawaye na k'arewa shikam da tuni ya daɗe da manta yana dasu, shikenan gobe za'a yake mar hukuncin kisa?
Baradai muje mezai faru goben, matsoratan masoyana😜😄😄
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment