☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
56-60
©Rabiatu sk msh
®NWA
www.babymsh.blogspot.com
Umman Abdul, tare suke da Abbanshi a mota wurin komawa gida, sai dai yayi tagumi duk ya shiga damuwa.
"wai kinsan wani abu Hajia?"
"A'ah saika faɗa Abban yara"
"wallahi ni gaba ɗaya kunyar kaina nakeji, yaronnan yana kuka yana faɗa mana ba shine ya kasheta ba, anma muka kasa yarda"
"tohh yanzu an tabbatar da bashine ya kasheta ba? Ni naga kaman ka fara saukowa Alhaji"
"Haba Hajia, bakiji bayanan da likita yayi ba? Nifa daman can don kar ace na goya mishi bayane shiyasa kika ga ina haka"
"Hmm" kawai tace, shima da yaga kaman batason maganar sai yayi shiru kawai.
Wata mahaukaciyar dariya taji ta cika mata kunne, da sauri ta zabura ta juya inda yake "kaine kayi dariya?"
"na miki kama da yanayin dazan dariya ne?" juyawa kawai ta k'arayi, can kuma ta k'arajin an ɓarke da wata dariyar, da sauri da saka hannuwa ta toshe kunnuwanta.
Cikin dariyar kuma da wata razananniyar murya akace "HAKK'IN KISA, ninan zan ɗauka Hakkin kisan da kaina, tunda kuka kasa magana a gaban kotu"
Wata irin k'ara ta fasa ta rirrik'eshi, "wai lafiyanki Hajia? Tuk'i fa nake"
"nidai muyi sauri mubar wurinnan Aljanune hanyar"
"ai kece Aljanar"
Da shigarsu gidan ɗakinshi ya wuce,
"ki kawomun abincina tun safe banci komai ba"
"tohh Alhaji, kaima dai ne duk ka...." hannu ya saka ya dakatar da ita, "ki kawomun ɗaki" kaɗa kai tayi ta shige kitchen.
Saida ta buɗa ta tabbatar abincin akwai zafinshi sannan ta rufe daman khadija ce mai girka mishi, tana cikin harhaɗawa a tire taji abu ya faɗo mata akai, da sauri ta duk'a tana duba ko miye, gabanta ne ya faɗi taja ajiyar zuciya tayi baya.
K'ullin magani ne ta gani, sarai ta gane ko maganin miye anma ta ina yazo nan? ta duk'a hannunta na kyarma zata ɗauka, maganin taga kaman yana ja da baya, mamaki ya cikata haka ta dinga bin maganin zata ɗauka yana matsawa, kawai ta mik'a hannu da sauri zata cafkoshi, hannunta na dira k'asan ya bugu, take ta farajin kaman girgizan k'asa, komai na kitchen ɗin kaman zai faɗo mata idan ta ɗaga kanta sai taga kaman ana jujjuyawa da ita.
Tana dawo da kanta ta duba babu maganin, hankalinta ya tashi ta ringa ihu a kitchen ɗin, gashi ba daman ta gudu data mik'e za'a mayar da ita daɓas ta zauna, idan taja gwiwa kuma kaman ba tafiya take ba sai maidota ake, ta bala'in tsorata ga wata irin mahaukaciyar dariya data cika mata kunnuwa.
Saboda ihun da take da kuma tsabar tsorata bata kula da komai ya lafa ba, sai dai ta buɗa ido taga Abbansu Abdul tsaye jikin k'ofa.
"nikam Hajia don Allah yau menene yake damunki? Kinbi kin cika gida da ihu kaman wata yarinya"
Da sauri ta rarrafa inda yake, "Aljanune, wallahi Aljannune kitchen ɗinnan, na rantse akwai Aljanu"
"badai a gidana ba, Idanma Aljanun ne da ihu zaki koresu? Don Allah ki saba da addu'a a bakinki mana"
"Naji nidai, mubar wurinnan" duk ta rirrik'eshi ko kanta tak'i dagowa idanunta a runtse.
"muje kinma manta da yunwar da kika bar mijinki da ita?"
"ga abincin can"
Ya tafi zai ɗauka da kanshi, ta bishi tana rik'e dashi, tsoki yaja bayan ya buɗa abincin.
"yanzu wannan shine abincin?"
"eeh shine"
"wannan ne abincin da zanci? Haba hajia, nidai bansan meke damunki ba yau, anma don Allah kiyi k'ok'arin canjawa"
Da sauri ta ɗago tana duban abincin taga meye dalilin da yasa mijinta keta faɗa haka, abinda ta ganine yayi matuk'ar razanata, yanzunnan fa take kitchen ɗin anma har ya canja haka.
Ruɓaɓɓun Vegetables ne ta gani, cabbage, carrot, dasu tattasai, ga lakar kifi da aka yaɓa daga sama duk sun cakuɗe da ɗanyen cous-cous.
Sakinshi tayi ta ruga da gudu ɗakinta a tsorace, girgiza kai kawai yayi baima bi ta kanta ba yabar gidan kawai.
Har dare bai dawo gidan ba, ita kaɗai ga tsoron da takeji, daman Khadija tun bayan abunda ya faru da Abdul ta daina fira da kowa, ta daina zaman falo, data gama abunda take zata shige ɗaki kawai tayi kwanciyarta tana tunanin ɗan uwanta, inta gaji ta ɗora Alwala tana mishi Addu'an Allah ya fitar dashi.
Umman Abdul tunda ta shige ɗaki, ta rurrufe ko ina, sannan ta kunna wutace, ta kwanta daga baki-bakin gado tana raba idanu, gabanta sai faɗuwa yake, a haka har barci ya fara ɗaukarta.
Can cikin barcin barcin ta fara jiyo kukan jarirai a hankali, tama ɗauka duk mafarki ne saida taji kukan ya fara yawa ta farka a firgice, jariri kuma? Ina zasu samu jariri gidannan?
Muryoyin jariran sai k'ara yawa suke, kuma kaman yana matsowa inda take, sai dube dube take a ɗakin gabanta na faɗuwa tuni ta fara kuka.
Kukan na k'ara yawa gabanta na tsawaita faɗuwa, sai wurwurga ido take ko ina, idonta na kaiwa kan mirrow ta kusan haɗiyar zuciya, jarirai ne kwance ta ko ina, cikin ɗakin, har inda take tsakiyar jariraine sun baibayeta, ai data k'walla k'ara anan ta faɗi sume.
A gidansu Hajna kuwa.
Dukan k'ofar da ake ne ya tashe ta daga wahalallen barcin da baifi minti biyu da ɗaukanta ba, a ruɗe ta tashi ta ida yaye zanin gadon tana kakkaɓe fuskanta, Maryam ta tsaya tana kallonta da mamaki.
"Mama" ta ɗan saurara daga kakkaɓe kakkaɓen da take idanu a rufe take kallon k'ofa.
"buɗe idonki Mama kin farka, nice Maryam"
Sannan ta buɗe idonta tana kallonta cikin jin kunya tama rasa me zatace "lafiya yau baki fito ba? Har 11 tayi baki break fast ba, Gwaggo Hauwa tace ko a kawo miki nan?"
"A'ah ganinan fitowa, kar kuma a k'ara dawowa a dameni"
"tohh Mama" harta juya zata tafi.
"ke jirani mu tafi tare"
Ta dawo zata shigo ɗakin "ki jira nace ba kizo ki zauna ba"
Ta kwashi zanen gadon zata wuce toilet tana rufe bayanta, Maryam da bata gani ta k'yale tace "Mama duk kin jik'e a bayanki, kalla katifarki ma"
"ke baki ganine? Bakiga zufar da nake ba? Mummunan mafarki nayi"
Ta zaro ido "Mafarkin ban tsoro?"
"kin isheni da surutu"
"nayi shiru Mama, da nice ko a mafarki addu'a zantayi, sai dai abun tsoran yayi zufa bani ba"
"shirun kenan? Don bake kikaga abunda na gani bane"
Ta shige kewaye tana magana ko addu'an shiga bayi batayi ba, zanen gadon ta fara wankewa, tana shirin cire kayanta ta hango shower na girgiza, ita kaɗai take girgizawanta, sai zare ido take tana jiran taji ta inda zata jiyo dariyan, anma bataji ba sai dai showern dake girgiza kaman zata ɓalle, gabanta na faɗuwa kamn ta fasa ihu take kallonta.
Can saiga ɓera ya fito daga ciki, yana fitowa ta daina motsi a hankali ta sauke ajiyar zuciyah, da taga kaman fita zaiyi ta tafi buɗe mishi k'ofa, yana kaima bango karo sai ya zama dunk'ulen magani bak'ik'irin, sannan aka kwashe da wata daria, ae batasan sanda ta buɗe k'ofan tayi waje da gudu ba, anan ta wuce Maryam ko kanta bata bi ba.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment