☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
76-80
©Rabiatu sk msh
®NWA
www.babymsh.blogspot.com
Rerbeeart_sk @wattpad
Kotu....!
Ta cika ta tumbatsa, ko ina mutanene ba masaka tsinke, a can na iske en RAZ novella sun riga kowa zuwa, su Maryam tapeeda, dr meenert, murjar baba, umman sayyida, da marymaama kam suna gaba baba, en KHADIJA CANDY novels gayya guda sukayo, ASHNUR ma naa hangota da tawagarta, PHERTY zahra exam take anma ta ajje sai da tazo kotu jin yanda zata kaya, en MU FARKA MATA daman a can gari ya waye musu, en ILILEE novels kowa yazo sai hange nake ina zan hangoshi? Ga UMMU ABRAR ma tazo da Abrar ɗinta a gaba (if u knw wat i mean😆).
Wasu en mata dake kusa dani naji suna maganan wata mata da miji, ae ba k'aramin burgesu suke ba, mijin sai ririta matan yake kaman ita kaɗaice er gata a dunia, jin yanda suke zuzuta couples din ya sakani waiwayawa ba shiri, "wazan gani haka?" abunda nace kenan.
Dariya yayi yana nunata "MATATAH CE"
"kaikam Najib har yanzu baka daina faɗin matarka bace?"
"ina ae har a Aljannah na ringa faɗa kenan Saudat Matatah ce"
Sama-sama muka k'arasa gaisawa da Sauden Najib, saboda hango best couple ɗina da nayi, Majeeda da Majeeda rik'e da kyawawan yaransu, sai mita yake mata shifa baison zuwa irin wurin hayaniyarnan ta kawoshi, kusa dasu HAFSATUL KIRAM ne da Ya Umar ɗinta.
Shigowan Alk'ali ne yasa kotun tayi tsit, kowa ya nutsu, shari'arsu ce ta farko, aka gabatar da ita, barrister Ahmad ya fara mik'ewa, shima da ganinshi yana cikin yanayi. Idan ya kalla Abdul da yanayin da yake duk sai yaji ya k'ara sarewa, don yaune ranarsu ta k'arshe.
"Shaidar da nake da ita a yau, itace cikakken bayanin likita akan cutan data kashe Hajna, wanda suka k'ara zurfafa bincike suka gano"
Likitan ya fara bayani, da takardar report a hannunshi.
"wannan report ɗin mun nemo bayani ne a wurin likitan dake duba Hajna lokacin da take raye kan Matsalar infection da take fama da ita. Report din ya nuna cewa tana yawan fama da infection wanda hakan kesa tana zuwa asibiti don duba lfyrta. Likitan yace duk zuwa ana mata HVS/MSC( High viginal swab/microscopic, culture and sensitivity) don ganin kalar microorganisms din dake cikin gabanta da neman maganin da zai kashe kwayar cutar Dan da nan.
Wani lokacin ma idan abun yayi kamari sai anyi mata ECS/MCS(endo cervical swab/microscopic, culture and sensitivity) Wanda idan ta dace magani tana dadewa abun bai tasar mata ba. Amma kuma mun dauki hakan ne a makaranta take kwaso infection din sbd kwamacala ta bayin makaranta da kuma fitsari inda bai kamata ba.
A binciken da mukayi kan vigina din Hajna mun gano wani tsuro wanda haduwar wasu abubuwa da bamu san ko miye ba suka dunkule waje daya duka tsuro sai ya zama kamar tumour. Sai ya tsiro mata daidai idan an wuce labia majora, labia minora wajen vulva dinta kafin a kai cervix. Shine abinda ya fashe a gaban Hajna har ya kawo wannan jinin mai yawa da muka gani faca faca a jikinta da gadonta.
Tambayarmu a kan Abdul itace shin yana shan wani abu ne da ke kara karfin maza kafin yayi aure ko kuma kasha kwaya ne ranar da aka kawo maka Hajnah
Sbd yadda yaje ma Hajna abun tambayane,babu yadda zaayi namiji ya sadu da mace na tsawon wannan lokacin tun wajen 11 na dare har asuba) alhalin lfyrshi lau bai sha komai ba.
Dadewar da yayi yana saduwa da ita ne ya kawo fashewar wannan abun
Amma da ya sadu da ita na kankanin lokaci ta kuma hanyar hankali da ko tsautsayin zai faru zai zo ne da sauki sosai."
Barrister Ahmad yayi gyaran Murya bayan an mik'a ma alƙali takardan,
"wannan shine bayanin ɓoyayyar cutan da Hajna ta daɗe tana fama da ita, Ya mai girma mai shari'ah, ina fatan wannan hujjar zata zama gamsarshiya wurin wanke Abdul daga laifin da ake zarginshi dashi"
"ina da ja Ya mai shari'ah" inji barrister Alqaseem.
"bai kamata shari'arnan ta k'are a haka ba, idan mukai nazari akan bayanin likita na k'arshe, mun yarda da batunshi na cewar Hajna nada cutan Infection wanda har iyayenta basusan da tana zuwa wurin likita yana dubata ba, anma shida kanshi likitan yayi bayani kan cewan inda Abdul baisha wani abu dazai k'ara mishi k'arfi ba abun zaizo da sauk'i, kenan har yanzu HAKK'IN KISAN hajna yana kan Abdul"
Ya maida kallonshi akan Abdul, "Malam Abdul, tunda har anzonan, bai kamata kaci gaba da wahalan da shari'ah ba, wanne irin magani ne kasha ka jema Hajna a daren data rasu?"
Girgiza kai kawai yake, "babu abunda nasha, wallahi tunda nake da idona ba ban taɓa ganin maganin k'arama maza k'arfi ba, ban taɓa sha ba, mezai sakani shan abunda zai cutar da Hajna ma?"
Barrister Alqaseem ya juya kan Alk'ali, "ina ganin duk hujjojin da kotu take buk'ata kan dalilin mutuwan Hajna sun kammala, Abdul yayi amfani da matarshi Hajna tun daga k'arfe 11 na dare har zuwa Asuba, wanda wannan ba k'aramin cutarwa bane a gareta, bayannan kuma bai tashi je mata ba saida yayi amfani da maganin daya k'ara mishi k'arfi, bisa duba da wannan hujjojin nake rok'on kotu da tayi gaggawan yankewa Abdul hukunci, domin babu wanda yake da HAKK'IN KISAN hajna bayanshi"
Barrister Ahmad dafe kai yayi kawai ya koma ya zauna domin kuwa yama rasa da wanne kalamin zai k'ara kare Abdul, Alƙali ya duk'a yana en rubuce-rubucenshi, gaba ɗaya kotun tayi tsit kowa da abunda yake sak'awa a ranshi, k'aran kukan Meerah kawai ake jiyowa, Abban Abdul ma duk da k'arfin halinshi saida ya zubda hawaye, Umman Abdul daman baizo da ita ba saboda Halin da take ciki na tsorata.
Anan wurin Abdul ya duk'ar da kanshi yana hawaye, kanshi na matuƙar sara mishi, tunanin Hajna na dawo mishi sabo, ɗaga kanshi yayi yana kallon Meerah, yanda take kuka da alama tama fishi shiga tashin hankali, Allah sarki khadija, yasan tana can gida tana ta mishi Addu'a.
Maman Hajna ce Zaune, idonta rufe tamak'i buɗewa saboda wani abubuwa dake mata yawo saman kai, tana jin hayaniya anma tayaya zata iya buɗa baki ta faɗi gsky gaban wannan jama'ar? Buɗe ido tayi da niyyar ta k'ara k'are musu kallo, wani k'aton kai ne mai ban tsoro, babu tsoka ko kaɗan sai k'ashi ya taho baki buɗe ya kusan kaima fuskarta karo, ta fasa wani uban ihu ta rufe ido.
Cikin kunnanta ake mata wani irin tsawa, "Bazaki faɗa ba? Ki buɗe baki kiyi bayani, ki faɗi gaskia nace"
A ruɗe ta mik'e, "zan faɗa! Wallahi zan fafa" kowa ya juya kallo ya koma kanta, harta alƙali tsawa yayi da rubuce-rubucenshi.
Saiga Umman Abdul tare da wani mutum irin en k'auyennan, kaman an jefosu sun dira gaban kotu,
Umman Abdul tace "a dakata, ba shine ya kasheta ba"
Maman Hajna tace "eeh bashi bane, nice nan nayi silar mutuwar y'ata"
Umman Abdul tace "A'ah nice dai, nice nayi silar mutuwarta" ta kalla mutumin da sukazo tare,
"gaskia mukazo mu faɗa ko?"
Shikam Abdul kallonsu kawai yake da mamaki, Ummanshi kuma? Meya haɗasu da mutuwan Hajna?
Mutumin yace "k'warai ma kuwa, babu mai HAKKIN KISAn baiwar Allahn nan Ya mai shari'a sai mu, domin kuwa ni naga abunda na gani, sati guda kenan HAKKIn ta ya hanani runtsawa, idan na kwanta na ringa ganin kawuna kenan, kai ido buɗe ma cikin tsorata nake"
Daga can baya suka jiyo murya na cewa "muma haka, Mune nan Mukai silar mutuwan Hajna, gaba ɗaya mutuwanta ta hana mana sukuni" su Hajia karime ne, hango Maman Hajna da sukai a tsaye ne ya saka har suna rige-rigen K'arasawa inda take.
Hajia saratu tace "kiyi hak'uri Hajia, anma dole mu faɗi komai a gaban kotu yanzunnan, domin kuwa rayuwanmu na cikin hatsari indai bamu faɗi gaskia ba"
"k'warai ma kuwa, duk kwanakinnan cikin tashin hankali muke, hak'uri zakiyi kawai Hajia mu muka ga abunda muka gani"
Gaba ɗaya kotun ta hargitse, kowa da abunda yake faɗa, mamaki faal a zuciyoyin mutane, sai da Alk'ali ya tsawata sannan kowa yayi tsit.
"ya isa haka, kotu ba wurin sauraren hayaniya bane, idan da maganar da zakuyi a gaban kotu zaku fito ku faɗeta" su duka kamar walk'iya sai gasu sun wuntsilo gaban kotu.
Alk'ali yama Maman Hajna Umarni akan ita za'a fara saurara.
Kumin Uzuri, wallahi hannuna ya gaji naso kuji komai a yau, anma ku k'ara hak'uri zuwa next page plz
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment