☠HAK'K'IN KISA☠
👽👽👽👽
16-20
©Rabiatu sk msh
®NWA
www.babymsh.blogspot.com
ASALIN LABARIN.
Bayero University Kano
Tafe take a hankali cikin takunta na nutsuwa, bak'ace anma ba can ba, fatarta mai kyau da shek'i, tana da dogon hanci da dara-daran idanu masu k'ara ma fuskarta kyau, ɗan k'aramin bakinta da ko kaɗan ta motsashi sai dimple nata ya fito, bata da k'iba jikinta dai dai, sai dai bata da rama ko ina a cike take.
Wuri ta samu ta zauna ta fito da wayanta tana shirin kiran k'awarta, kawai sai dai taga mutum a gabanta. Ba k'aramin faɗuwa gabanta yayi ba, bama kaman da ta ɗaga kai sukai ido huɗu dashi, kodai Aljanine? Don kyan nashi har yayi yawa, batasan sanda ta tsurama kyawawan idanunshi kallo ba, a yayinda shima yake kallon nata.
Yaɗan kalla wayan hannunta, sannan ya koma kallanta "Plz wayan hannunki zaki aramun?" wani daddaɗan sauti ya sauka a kunnanta da tunda take bata taɓa sauraren kamansa ba.
Ta ɗauke idanunta "amfani nake da ita" ta faɗa da sanyayyan muryanta
"nima bzan gudar miki da ita bane, anan zanyi waya kawai na baki"
"ina taka?"
"na barta a gidane ina sauri zan fita lecture, plz karki tsaya tambya wayan da zanyi tana buqatan sauri ne"
Mik'a mishi wayan tayi, kafin ya amsa tace "ka tabbatar ba layinka zaka kira donka samu numbana ba?"
Ya girgiza kai "o'oh"
Saida ya tabbatar ya rik'e wayan a hannunsa, sannan yace "Idan kuma numbana kikeso ki faɗa na miki saving"
Harara ta aika mishi sannan ta mik'e zata anshe wayanta, ya cillata ɗayan hannun tare da kashe mata ido "soriyo"
Bayan ya kanga wayan a kunne ya sake cewa "naga en mata da yawa suna tambayana numbane, wasu suna aikomun da nasu, kekam a kyauta zan miki saving"
"niba kaman wasu en matan bane ai, kamasan waye saurayina? Ko kaɗan bzaka haɗa kanka dashi ba....."
"Shhhht" ya ɗaura hannunsa saman leɓe yana nuna wayan alaman ta shiga, ta harareshi cikin k'ulewa.
"wa'alaikis salam Ummana" ya faɗa, anma bata jiyo me ake cewa ɗayan ɓangaren.
"Abdul ɗinkine, kira nayi na miki albishir"
"abunda kika daɗe kinaso, ynzu haka gani tare da surukarki"
"Da gaske Ummana, na samu Matan aure wacce hankalina ya kwanta da ita, da layinta ne ma na kira ki"
"Ameen Umma, Ameen, Ameen Ummana" tunda ya fara magana ta buɗe baki tana kallonshi, mamakinshi sosae take, wannan wanne irin mutum ne?
Ji tayi ya ajje mata waya a gabanta, "ngde sosae Hajna"
Ina yasan sunana kuma? Qila a wayan zai gani, ta kalleshi ya sakar mata murmushi, "sai mun sake haɗuwa"
Kasa ɗauke kai tayi tabi bayanshi da kallo, yanda yake tafiya cikin aji, ya haɗu ta ko ina, kyakkyawane na ƙarshe anma da alama bai ɗauka rayuwarshi da zafi ba, ta taɓe baki.
Ji tayi an taɓota ta baya "wow Hajna, wannan guy ɗin fa?"
"ohon mishi, aron waya yazo, yayi shiriritanshi ya k'ara gaba"
"watau ke duk namijin da yake sonki mashiririci ne ko? Jifa yanda ya haɗu, ga kyau ga gayu"
Ta girgiza kai "meerah! Idan ya miki ki aureshi mana"
"da ni yake so kam dana more, muje ko?"
Ta mik'e ba tare data k'ara cewa komai ba.
Kafin ta isa gida ta manta da batunshi, ɗakin mamanta ta wuce.
"Sannu da gida mama"
"yauwah sannu da hanya"
Taɗan kwanta jikinta "wallahi na gaji da yawa Mama"
"kici abinci saiki huta mana, wannan son jiki naki har yayi yawa"
"Maryam bata dawo ba?"
"an tafi ɗaukota, su muhseen ma yanzu suka tafi exam"
"shysa naji gidan shiru, nima na tafi inɗan runtsa kafin lokacin sallah"
Ruwa ta watsa, sannan ta canja kaya mararsa nauyi, ta haye gado ta jawo wayanta, whatsapp ta shiga bayan ta buɗa Data.
Tana cikin reply taci karo da bak'uwan numba, batasan numbanba, anma da yake sallama aka mata saita amsa kawai.
"yauwa daman ke kaɗai nake online ina jira"
Mamaki ya cikata da taga sak'on, "ban gane ba, waye yake magana?"
"wanda kike tunani a ranki mana"
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment