New Post

Tuesday, 15 August 2017

HAKKIN KISA 81-100

☠HAK'K'IN KISA☠
      👽👽👽👽
             81-100

©Rabiatu sk msh
      ®NWA
Wattpad @Rerbeeart_sk

www.babymsh.blogspot.com

🔚🔚🔚

  Maman Hajna tayi gyaran murya cikin damuwa ta fara magana.
    "Nice nan na haifa Hajna, kuma babu wanda yake da Hakkin Kisanta saini, nasan kowa zaiyi mamaki dajin hakan, anma ba abun mamaki bane idan kunji bayanin dazai fito bakina, fatana kawai sauran mutane zasu ɗauka darasi karsu aikata irin aikin wautar da nayi"
     "tun lokacin da likita yayi bayani kan mutuwan Hajna, na shiga k'ok'onto, domin bansan wanne irin hukunci za'a yankemun ba, shiya hanani magana"
    "na kasance tun kafin haihuwar Hajna, nakejin mutane na magana kan indai kana da yarinya ɗiya mace, kamata yayi tun kafin ta girma ka fara gyarata da magungunan mata ba saita girma an mata aure ba, da wannan burin nayi aure harna samu cikin Hajna, kuma cikin sa'a Allah ya bani rabo da ɗiya mace, tana da shekara 7 muka haɗu da Hajia karime mai bada magani, tun daganan take kawomun magungunan da bansan asalinsu ba, nake ɗurama Hajna, kullum cikin bata magungunan tsumi nake, hardana tsarki dana matsi, da kaina nasan Hajna badon tanaso ba take amsar magungunan nan, anma ko a fuska bata taɓa nunamun ba, da yake yarinya ce mai biyayya"
      Alk'ali ya nisa sannan yace "kenan magungunan da kike batane silar cutar data sameta?"
    Hajia Saratu tayi karaf tace "k'waraima kuwa, domin nima mutane da yawa na kokamun akan wannan matsalar"
     "kenan kunsan yana cutarwa kuma kuke saidawa?"
    "Itama ae mun faɗa mata yana cutarwa"
   Kallonsu kawai yake da mamaki, gaba ɗaya kotun jikinsu yayi sanyi, ya kalli maman Abdul,
    "menene abunda zaki faɗama kotu kan mutuwar Hajna?"

    "tabbas ni nake da abun faɗa, duk da bayanin da tayi yayi kama da nawa, ta faɗi silar cutan Hajna, anma nice nan nayi Silar mutuwarta, domin kuwa tunda aka saka ranar auren Abdul da Hajna, na fara amsar magunguna a hannun wannan mutumin da yake tare dani, shine yake kawomun magungunan k'ara ma maza k'arfi, ni kuma nake ba Abdul ba tare da saninshi ba, duk da baisan ko miye ba, anma a dole nake matsa mishi yasha, bayanin da zanyi kenan yamai shari'ah"

   Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abunda wasu daga cikin mutane kotun ke ambata, gaba ɗaya Meerah a firgice take dajin wannan bayanin, ballantana Abdul da yake jin maganar kaman saukar aradu.
    Alk'ali ya ringa girgiza kai cikin mamakin wannan iyaye, gaba ɗaya abun ya ɗaure mishi kai.
     "wannan wanne irin iyayene nake gani a gabana? Iyayen da zasu bama yaransu abu bayan kuma sunsan zai cutar dasu kawai da sunan gyara? Gyaran da ɓacinshi yafi amfaninshi yawa, yau wa gari ya waya? Abunda kika daɗe kina mata gyaran kanshi ya k'are a daren farko? Wallahi wannan kuskurene babba, gareku iyaye da kuma ku masu saida magungunan da bakusan asalinsu ba da sunan gyara, abun kunya ma wasu matan ne da kansu keshan abunsu"
    Ya kalla Hajia salame, "kina da aure? Yaranki nawa?"
      girgiza kai tayi cikin jin kunya, "bani da aure a yanzu, ban taɓa haihuwa ba sanadiyyan shan magungunan matan da nake"
      "kefa?" ya tambaya Hajia karime "aurena huɗu anma babu ko ɗaya"
     "kun gani ba? Wallahi magungunan nan ba k'aramin illa sukewa mutane ba, gaba ɗayama kun sanya ɓacin rai na manta abunda ke gabana"

     Duk'awa yayi yana en rubuce-rubuce, sannan ya ɗago kai kowa yayi shiru yana jiran yaji mezai faɗa,          
    "Bayan nazari da dogon bincike akan wannan shari'a, mun gane cewa Abdul bashi da laifi ko kaɗan akan mutuwan Hajna, domin kuwa gasha magungunannan ne a bisa rashin sani, sannan kuma abunda ya faru dashi a ranar aurensu da Hajna ba laifinshi bane, ya faru ne akan Maganin da yasha cikin rashin sani, don haka kotu ta wankeshi daga zargin da ake mishi"
    "Sannan kuma gaba ɗaya mutanen nan, babu wanda HAKKIN KISAN Hajna bai rataya a kansu ba, don haka kotu ta yanke musu hukuncin shekaru goma a gidan yari, Maman Hajna, Umman Abdul, da kuma sauran masu maganin nan guda Uku"
   Kotu.....!!!  

Umman Abdul anan wurin ta duk'e tana kuka, Umman Hajna kam Ɗaura hannu tayi akai tana ta ihu kaman wacce ake zarema rai, Hajia karime ta rungume Hajia saratu,
    "kaicon mu, kaicon duk wata macen dake bama er uwarta mace maganin dake cutarwa akan gyara, kaicon wannan hali namu yanzu gashi abunda ya jawo mana"

    Tsananin farin ciki Meerah batasan sanda ta taso ta rungume Abdul ba tana dariya, anan inda yake tsaye yana ma mahaifiyarshi wani irin kallo na tausayawa, ganin Abbanshi na zuwa inda yakene, cikin dubara ya cire Meerah daga jikinshi.
    Yana ɗaga ido ya hango Hajna tsaye cikin farare kaya, tana murmushinta mai kyau, kallon Meerah tayi tana mishi alama cikin murmushi, a haka harta ɓace gaba ɗaya.

Alhamdulillah
Anan na kawo k'arshen wannan gajeran labari nawa, kuskuren dake cikin Allah ya yafemun, Allah kuma ya bamu ikon amfani da darasin dake ciki.

SADAUKARWAR Takice Auntie Sis, Allah ya k'ara girma, tabbas babu wanda yasan halin karamcinta sai wanda ya zauna da ita.

Godia Mai yawa ABDULAZEEZ ILILEE, Allah ya k'ara basira da ɗaukaka, muna tare dakai a littafin BARE

Jinjina ta musanman ga k'ungiya mai Albarka, NAGARTA WRITERS ASSOCIATION, Allah ya k'arama mana haɗin kai, Ameen.

RAZ nawa, banda kamanku Amrah A msh, ZahraBB, Alah yabar k'auna.

Gaisuwa ga dukkan makaranta littafinnan, dama masoyana gaba ɗaya, Allah yabar k'auna, kuci gaba da kasancewa dani a littafin ZAMAN AURE, wani zaman ma yanzu za'a fara.

Domin gyara da shawarwarinku +2348032133670

©Rabiatu sk msh

Related Posts:

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts