💕💕 *```HAKA SO YAKE```* 💕💕
💗💗💗💗💗
💕 *_1 - 2_* 💕
💗💗💗💗
*Na*
*_Rabee'at sk mash_*♥
```_And_```
*_Mr, smiles_*😃
"Uhim, Uhim" tayi gyaran murya sannan tace " Sunana SUWAIBA amma wasu mutane sunfi kirana da SUBEECOOL, wad'ansu kuwa suce SUBEEY Amma ni wadda nafiso shine SUBEEY, hakan yasa mutane kowa yake kirana da subeey, natasone a gidan kanwar mahaifina, Inada yayana mai suna ABDUL AZEEZ, ina matukar son yaya ABDUL a cikin zuciyata, yaya Abdul mutum ne mai son mutane da kuma son barkwanci, Inajin dad'in zama dashi sosai, uhimm.." ta kara yin gyaran murya sannan taci gaba dacewa "Wai na manta bangaya muku kaman ninaba, ni farace, doguwa, kirara fulani domin asalina ni'yar kyauyen yola ce,
Inada kyau amma saidai kash inada matsala d'ayah...."
"CUT " yafad'a yana dariya yad'an tsaya yana kallon wayarsa, kafin yad'ago kansa ya kalleta yace "video yayi kyau kinga yadda kika fito kuwa kamar wata ba'indiya, wannan ai zan iya d'aurashi a Instagram"
Subeey ta murgid'a masa baki tana hararansa cikin wasa tace "kagani koh yaya abdul gaskiya banaso, ni karka sakani a instrgrm kaifa kace zaka ajiye a wayar dan tarihi" takarasa maganar cike da shagwaba,
Abdul ya yayi dariya yace "to naji zan ajiye amma, gaskiya zan daura a instrgrm, kin sani koki sami mai sonki" yakara bushewa da dariya
A Lokaci d'aya naga yanayin fuskar subeey ya chanza, ta Tsuke fuska tana hararanshi taja mayafinta tanufi hanyar fita daga d'akin, abdul yayi saurin cewa " ina kuma zakije bamu gama video ba fah"
Subeey tajuyo edonta har yayi ja sosai murya a sanyaye tace " kajira harna samu mai sona sai muci gaba" Bata jira yayi maganaba tafita tabar d'akin,
Sunanta yarika kira yana dariya, amma taki ko juyosa da sauri taja kofar d'akin tafita,
Da fitarta d'akinta ta nufa, tunkafin ta karasa kuka ya kubuce mata, ai kuwa tana shiga d'akin ta fad'a kan gado tafashe dakuka, zuciyarta cike da haushin kalamin da Abdul yafad'a,
Kuka tayi sosai saida edonta yasoma kumbura, sannan tatashi tazo bakin mirror, tana kallon kanta, a hankali tasa hannu ta share hawayenta,
Sannan takara kai Hannu ta tab'a edonta d'aya da batada lafiya, tana murzata a hankali, nanfa kuka yasoma dawo mata, cikin shashshekar kuka tadafen edon tana cewa "Saboda kene yaya abdul baya sona, narasa wata darajar a cikin jikina.." Ta fashewa da kuka tana danna edon nata,
Cen kuma bayan wasu dakiku ta tsayar da kukata tana hawaye takara d'ago kanta tana kallon kanta ta jikin mirror tace " yaya abdul ina sonka, wlh ina sonka HAR cikin ZUCIYA ta, amma narasa yazanyi na fahimtar dakai MIYE SO, kayarda dani yaya abdul ..." Ita kad'ai take magana saikace wata zararriya, saikuma takara fashewa da kuka...
Via OHW📚📲
0 comments:
Post a Comment