New Post

Wednesday, 18 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 67-68

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  67-68

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

A gurguje,,,,,,,,,

    Daddy yace "sai dai ban ganeka bane" cikin ladabi yace,
   "Sunana Shaheed ibraheem imamu Abba, nazo wurin Majeeda"
    "tohhhh, Alhaji ibraheem dai wanda na sani?"
    "eeh Abba"
"tohh masha Allah, idan ka koma gida saika turo iyayen naka, nan da wani ɗan lokaci sai a...."
    Don tsabar jin daɗi ma baisan sanda ya katse Daddy ba,  "Da gaske Abba" wani irin kallo ya mishi na rashin ganewa sannan ya gane bai kyauta ba, daya saka k'ok'onto a maganar, yaci gaba da washe baki ba kunya Shaheed kema Daddy godia,

   Washe gari lokacin daya ɗibarma Majeeda ya cika, tunda safe data shigo gaisheshi ya tsayar da ita,
    "kina sane da yau ne lokacin dana ɗibar miki ya cika"
    "eeh Abba, bani da wani zaɓi, Insha Allah zanyi biyayya ga duk mijin daka zaɓamun"
    "Tohh tashi kije, Allah ya miki Albarka, daga yau ki fara shirye-shiryen bikinki nan da wani ɗan lokaci" wani irin faɗuwar gaba taji,
    "Ameen Daddy" ta mik'e jiki ba k'wari tabar ɗakin, tohh anma meyasa bata faɗa ma Daddy Shaheed ne zaɓinta ba? Kuma dai gani take kamar yaa fasa don tun bayan tafiyarshi, bai nemeta a waya ba, koba wannan ma yanzu tafiso Daddy ya sake mata wani zaɓin da kanshi, don ta samu ta mishi biyayyar data kasa a baya,

•••   •••   •••
   An kusa bikin Zahra, sai aka saka lokaci ɗaya, Duka bangarorin sai shirye-shiryen biki suke, su Majeed anzo biki, shi yanzu hankalinshi kwance, soyayya da kulawa babu wanda bai samu a wurin Aisha, tuni ya manta da komai ya rungumo matarshi don ba k'aramin so take mishi ba,
   Majeeda ma tunda hidimar bikin ta kama, ta kwantar da hankalinta, bama kamar da taasan Shaheed ne zata aura, ta kasa yarda ne, anma wani ɓangare na zuciyarta faɗa mata yake ta fara kamuwa da soyayyar Shaheed,

     Ansha shagalin biki, garin Mashi aka kawo mana Zahra😉, Majeeda kuma Aka ajeta Katsina Layout, taci kuka sosai, kamar shine aurenta na farko,
    Da dare ya kirasu ita da uwargida domin musu nasihar zaman lafiya, tana zaune kafin uwar gidan ta fito taa tsura ma wani hotanta dashi ido, sunyi kyau sosae tana tsaye ya rungumota daga baya suna dariya, kyakkyawahce anma bata da haske sosae da ɗan k'aramin jikinta mai kyau,
    Jin tafiyarta ne yasa Majeeda ta daina kallon hotan ta maida kanta k'ansa, ta zauna kujera mai kallon wacce suke sai k'amshi take zubawa, da yake Maryam akwai tsafta,
     Sai da ta ɗago ta kalleta ne, kamar ba itace a hotonnan ba, tayi wata uwar k'iba sosae, irin hajiyoyinnan, cif ta cika kujera mai zaman mutum ɗaya, babbar mace mai halin dattako, bai ɗauki wani lokaci yana musu bayani ba, ya sallamesu kowa ta koma ɗakinta,

    Zaman su da Maryam sosai takejin daɗinshi, tana janta a jiki, har dangin shaheed take janta kasancewarta mace mai zumunci, da fahimta, ɓangaren Shaheed ma bata da wata matsala, yana bata kulawa sosai yakeji da iyalanshi, bata da wata damuwa yanzu,
    Sai dai kewar Abdallah da yanzu yake hannun Umma, kowa yaso a bar mishi shi, sai daga k'arshe suka hak'ura aka barma Umma,

    Watansu Uku da aure Allah ya albarkaceta da juna biyu, ba k'aramin farin ciki Shaheed da Maryam sukayi ba, kusan ma Maryam duk ta fisu Murna, tun daga lokacin ta ɗaukema Majeeda duk wata hidimar gida, ita take kula da ita, sai abinda takeso za'a girka, Maryam mace ta gari ce sosae, kusan tare suke rainon cikin,
   Har mamakin Maryam take, mace mai kawaici da k'ok'arin danne kishi, irinsu kaɗanne a duniyar nan, ko godiya take mata sai dai tace
    "banson haka fa Majeeda, ni ban taɓa kallonki a matsayin kishiya ba sai dai er uwa, abinda muka daɗe muna Addu'ar nema ne da Shaheed, Allah bai bamu ba, kuma yaa nufeki da samu, ina tayashi son duk abunda yakeso, wallahi ji nake duk ɗayane"
     "Gaskiyarki Auntyna, ina yima kowacce mace Addu'ar samun kishiya ta gari kamarki" Maryam tayi daria,
    "da kuma macce ta gari kamar ki ba" sukai dariya gaba ɗaya, kamar ba kishiyoyi ba,

©Rabiatu sk msh

Related Posts:

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts