New Post

Wednesday, 18 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 63-64

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  63-64

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    "hajia ki rok'eni kawai in kai miki yaronki gida" bata saurareshi ba taci gaba da lallashin Abdallah yazo su tafi, anma yak'i yama maida ita kamar k'awar wasanshi,
   "Abdallah bazaka je gida ba?", ya tambayeshi, shikau harda saurin ɗaga kai,
   "Meyasa?" yayi shiru da yake maganarshi ba k'wari tayi ba,
   "mu tafi can muyi wasan ko"
  "eeh janje didan"
     "Yauwah tohh mu tafi yaron kirki" ya ɗaurashi a kafaɗa sukai gaba don yaga hanyar da Majeeda ta biyo,
   "Auntie mu tafi ko? Nima zan wuce gidane yanzu, ko an barmun shi?" batace mishi komi ba dai tabi bayanshi, suka tafi, sai da sukaje dai-dai gidan tace "tohh sauke minshi anan" ana saukeshi kau yayi cikin gidan da gudu,
   "na gode" tace mishi kawai, sannan tabi bayan Abdallah, yayi tsaye a k'ofar yana kallonta harta shige,

   Mai gadin ya taso rufe k'ofa ya ganshi nan tsaye, ya fasa rufewar bayan ya lek'o da kanshi,
    "Barka dai yallaɓai"
  "Yauwah baba, sannu da aiki" ya juya zai bar wurin,
   "Aiki da godia, wurin Alhaji kazo ne?"
  "A'ah yaron Matar gidan dai na maido"
   "matar gidan kuma? Ɗiyar Alhaji dai" harya fara tafiya ya dawo jin haka, baba mai gadi harda gyara tsayuwa zai fara tsegumi,
   "Shifa yaron?"
  "ɗanta ne, anma yanzu shekara ɗaya kenan da en watanni basu tare da mijin"
  Gaskiya mai gadinnan akwai surutu, mutumin ya faɗa a ranshi,
   "Allah sarki, nagode sosai baba" ya zaro dubu biyu ya mik'a mishi, ya amsa yana washe baki, don akwaishi da son kuɗi
   "ni keda godia yaro," sai kuma ya kasa tafiya, yayi shiru yana so yayi ma baba magana,
  "numberta zan baka?" da sauri ya ɗaga kai,
  "yauwah baba za'a samu ko"

  "eeh yaro, anma ka k'aro dubu biyar", yana kallon tudun Aljihunshi, ikon Allah wannan wanne irin mai gadi ne? Gashi dai tsoho sai tsurku da son gulma, ga shegen son kuɗi,
   Ya kwaso duk kuɗin Aljihunshu dubu uku,
  "gashi baba, daman su kaɗai suka rage"
  "tohh shknan yaro nima rabi zan baka tunda rabi ka bada" baza'ayi haka ba baba ina zuwa,
   Ya koma inda ya aje motarshi, ya jawota k'ofar gidan, ya dawo ya mik'a mishi dubu biyar cas sannan yace yana zuwa, ya shiga ɗakin da yake ya ɗauko wayar bala driver daya bari chaji ya kawo mishi,
   "Gashinan Alhaji duba, ko hajia Majeeda, ko Majeeda, ko er gatan Alhaji duk yanda kaga an rubuta"
   "Sunanta majeeda kenan" ya faɗa yana murmushi, "suna mai daɗi, kuma ya dace da ita,
  Ya maida mishi wayar yana godia bayan ya ɗauka number,

   Abdallah da gudu ya shige gidan, Majeeda na mishi magana bai tsaya ba saida yaje inda momie take ya faɗa jikinta yana daria, sannan taja ta tsaya tana kallonshi,
  "Abdallah ina ka tafine muna ta nemanka?"
   "wuyin uncle" ya fara lallaben Aljihunshi ya ciro chocolates yana bata,
   "shine ya baka wannan" ya ɗaga mata kai,
   "ka daina fita yawo kaji" nanma ɗaga kan yayi, sannan ya sauko kuma ya tafi wurin Majeeda ta ɗaukeshi, suka tafi ɗaki,
   Faɗa sosae ta mishi harya fara kuka, ta rungumeshi don batason ɓacin ranshi, ta share hawayen daya zubo mata,
   "ka daina rashin ji kaaji yaro nah"
   "baran kala fita ba"
  "yauwah nima naa daina maka faɗa" taci gaba da lallashinshi har yayi barci,

  Da dare harta kwanta, taji wayarta na ringing, ta jawo da duba bata gane number ba ta maida ta aje, mai kiran dai ya nace da kira gashi barci takeson yi, ta ɗauka kawai batayi magana ba,
   Ɗayan bangarenma shirun akayi, harta gaji da saurare ta kashe ta maida ta ajje, aka sake kira ta kashe wayar ma gaba ɗaya,

©Rabiatu sk msh

Related Posts:

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts