New Post

Wednesday, 18 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 75-76

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  75-76

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    Tsadajjen Asibiti sukaje, ba ɓata lokaci sukaga likita, aka mata scanning da duk sauran abubuwa, likita ya tabbatar musu da babu wani abun daya samu cikinta, anma tana k'ara samun hutu sosae, (bed rest) saboda jinin data zubar, sunyi farin ciki sosae, ba kamar Shaheed saida yayi sujjadar godiya ga ubangiji, lallai Addu'ah bata faɗuwa k'asa banza,
    Sun fito tare suna tafiya taji yaro ya rirrik'e mata k'afafuwa,
    "Mamanah" muryar Abdallah taji da mamakinta, ta  juya shiɗin dai ne, ta ɗagoshi dak'yar zata ɗauka, Shaheed ya ansheshi,
   "Yanzunnan fa likita yace ki daina ɗaukar Abu mai nauyi"
     "Uncle"Abdallah ya faɗa, Shaheed ya harareshi da wasa,
   "bana hana Uncle ɗinnan ba" Abdallah yayi dariya,
   "Na daina Daddyna" Majeeda dai kallonshi kawai take baki buɗe,
     "kai dawa kukazo Asibiti?"
  "Nida Umma ne, ni kuma na fito" Majeeda ta kamo kunnenshi zata murɗe,
   "Yanzu yawonnan bazaka daina ba Abdallah?"
   "in zaki mishi faɗa kuma sai kinji mar ciwo? Zo muje kaji Abdallah Umma na can na nemanka" ya juya sukai gaba ta bishi a baya, duk nisan da yayi kau tsaf ya gane inda ya baro Umma, suka shiga batasan ma bainan ba,
   Suka gaisa da Umma, ashe Aisha ce batajin daɗi,
    "Umma Ashe Aisha bata lafiya kuma banji ba"
     "jikinne nata kullum ba daɗi Majeeda, Shiyasa ma bama faɗa"
   "Allah sarki, meke damunta"
  "har yau dai basu faɗa mana ba, anma jikin nata da sauk'i ma" 
     "Allah ya k'aro sauk'i Umma" ta k'ara kallonta, barcinta takesha, ita har manta kamanninta ma take, rabon data ganta tun tana gidan Majeed, hannunta ta duba,
    "Aikam na baro jikkata inda na zauna" Shaheed da keta shan surutu wurin Abdallah yace "bara in ɗauko miki tohh"
    "A'ah yi zamanka bara inje" ta fice da sauri tana tunano inda take ganin ta barota, cikin sa'a ta ganta, tana ɗauka ta juya zata tafi, ta jiyo maganarshi a kunnanta, bazata taɓa mantawa da muryarba, bazata taɓa manta yanayin da takeji idanta saurari muryar ba, shiru tayi ta kasa motsawa daga inda take, ko kallanshi ma batayi ba, wani irin yanayi da bazata iya fassarawa ba ta shiga, ganin haka ya canja akalar zancen,
      "ke haryau baki iya gaisuwa bane?" murmushi tayi jin ya tuno da lokacin da suke faɗa, kafin aurensu kenan,
   "Ayni banga Abinda zan gaisar ba anan"
       "lallaima yarinyar nan, yauma rashin kunyar zakimun?"
   "babu yarinya anan" ta bashi amsa,
   "idan nazo na murɗe wannan masifaffen bakin naki kinmu bayani"
   "Zan zauna ne ka murɗemun baki? Kaima kasan ba tsoranka...." sai kuma tayi shiru tana k'ok'arin maida hawayenta, su duka suka yi daria,
     "Gaskiya da munyi yarinta"  ta faɗa tana juyowa, shima dariyar yake, sai kuma yayi shiru, shima da damuwa a fuskarshi
    "lokacin da muka fara gane gaskiya kuma k'addara tayi halinta" sai yanzu ta ɗago suka haɗa ido, tun bayan rabuwarsu bata k'ara ganinshi ba, shekara kusan Uku, yayi fari ya k'ara kyau sosae, sai dai rama da yayi da alaman bai cikin kwanciyar hankali,
   "Yaya Majeed dukka rame" ita kanta batasan sanda ta faɗa ba,
   "kekam Matatah na kwance Asibiti, kullum ciwo, idan ban rame ba ya za'a gane nine mijin?" ya faɗa da zolaya, sosae ya bata daria,
    "Allah ya bata lafiya"
  "Ameen, kwana da yawa, faɗamun ya rayuwanki?"

"ba daɗi, tun bayan rabuwar mu, Munyi aure da shaheed, matsalan dangin miji, ga kishiya kullum saita zaneni, miji babu ruwanshi dani, babu ci babu sha, babu wanda zan faɗama matsalana, kaifa?" yaɗan murmusa, irin yanda yake idan taa gama burgeshi,
   "Munyi aure da Aisha, Masifa harta linka taki, safe daban rana daban, ba ruwanta damun girki, kullum tayi ficewarta bata tambayata, ta rainani batajin magana ta kuma..." yayi shiru yana tunani, suka k'arayin daria a tare,
   "ina cikin farin ciki yaya Majeed, bani da matsala da kowah"
   "nima haka Majeeda, Aisha macece ta gari, banda damuwa yanzu saita ciwonta kawai, sai muna tunanin taji sauk'i kuma abun ya dawo"
    "Insha Allahu zata samu lafia"
    "Ameen fa"
   "Yanzu dai mu manta da rayuwarmu ta baya, ko babu komai mu en uwanah ne, kina kallona a matsayin yayanki, komai ya wuce"
   "komai yaa wuce fa," ta faɗa tana share hawayenta cikin dubara, "bara inje yanzu zamu tafi"
     Ta juya ta tafi, shima bai iya ce mata komi ba, soyayyar gaskiya kenan, kowannensu k'ok'arin ɓoye damuwarshi yake da murmushi, anma a zuciyoyinsu sunajin ciwo sosae,
  Tana zuwa sallama sukayi da Umma, bayan ta k'ara duba Aisha, sosae ta bata tausayi,

©Rabiatu sk msh

Related Posts:

1 comment:

Popular Posts