New Post

Thursday, 5 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 57-58

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  57-58

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

```It is sad when the person who gave you the best memories become a memory.```

www.babymsh.blogspot.com

    Har sukaje gida Majeeda kuka take, babu wanda yayi k'ok'arin rarrashinta, kamar ranta zai fita haka take wannan kuka,
      Suna zuwa Aunty ta rakata tsohon ɗakinta, kayanta komi sunanan, ta kwance mata goyon Abdallah ta ajjeshi sannan ta juya ta barta nan,
  Jawoshi tayi ta ɗaura saman jinyarta ta tsura mishi ido, kowanne hali babanshi yake ciki? Shikenan fa kamar k'iftawar ido komai ya gama faruwa, rungumeshi tayi a jikinta taci gaban da kuka,

Bayan kwana biyu,
Majeeda babuci, babusha, saita kama dole, tayi wata uwar rama tayi bak'i sosae, kullum cikin kuka take, daga Momie har daddy babu wanda ya kula da halin da take ciki, Abdallah kanshi yayi ramar dole saboda bai samun isasshen abinci, sai dai da madara ake kaɗa mishi,
   Kullum cikin kiran layin Majeed take bai shiga, babbar damuwarta kenan da batasan halin da yake ciki ba, rayuwar gaba ɗaya taa burkice mata da babu Majeed a tare da ita,
    Sai a kwana na Uku ne Momie ta fara gajia da halin da take ciki, tunda ta shiga ɗakin bata fito ba, abinci yanda aka kai mata haka za'a ɗaukeshi, ruwa kawai take ɗura ma cikinta,

Tana kwance ta saka waya a gabanta tana kuka, bayan ta gama kiran layin Majeed,
   Momie tace "tashi Zaune" babu gardama ta mik'e zaune tana share hawaye, momie ta jawo kwanon Abinci ta ajje mata gabanta,
   "banson gardama, ki maza ki cinye abincinnan idan baso kike muci gaba da sanya miki ido ba" kuka ta fashe dashi sosai ta faɗa jikin momie,
    "Don Allah momie kuyi hak'uri"
   "naji tashi kici abinci nace" ta tallabota, sai da ta tabbatar taci mai yawa sannan ta k'yaleta bayan tasha ruwa, da kanta ta fita da kwanonin sannan ta dawo zauna tana fuskantar Majeeda,

    "Damuwar me kike?" tayi shiru ta kasa ɗago kanta, momie ta zare wayarta dake sak'ale a hannunta,
   "bamu isa mu rabaki dashi ba Majeeda? Yanzu kiran menene kike mishi?" shiru ba amsa,
   "ke ba k'aramar yarinya ba da basai an zauna ana miki faɗa ba, yanzu duk bayan wannan neman wata alak'a kike a tsakaninku? Ki zauna kiyi tunani kanki ne kike cuta, kece mace, daga inda ya samu wata macen zai manta dake, kekau kina nan kullum kina cutar zuciyarki da tunaninshi, kiyi tunani idan har yana sonki me yasa ya sakeki? Da yake kanki rashin hankali ya k'are kika zauna kikaci gaba da zama dashi, kullum kuna cikin saɓon ubangiji, kuna tara ma kanku zunubai, me zakuce da ɗanku idan ya girma ya gano ta hanyar da kuka sameshi? Ki godema Allah da abun ya tsaya a haka, damarkice da zaki zauna kita rok'ar yafiyar ubangiji, ki manta da Majeed da rayuwar da kukayi a baya,"

   "Momie wallahi na kasa ne, kullum ina k'ok'arin mantawa dashi, don Allah ki tayani da Addu'ah"
   "ki k'ara dagewa kam, don babu wani sauran zama a tsakaninku, babu inda kika taɓajin anyi saki Uku an koma, kema kina tashi kina addu'ah Allah ya yafe miki, ya kuma yaye miki sonshi, namiji ne da ba'asha mishi alwashi, duk yanda yakai da sonki wata rana shida kanshi zai goranta miki,......" nasiha dai sosae Momie ta shiga yi mata, gaba ɗata jikinta yayi sanyi, har momie ta barta tana zubar da hawaye,
   "Taya zan fara koyama kaina rayuwa babu Majeed?"

Majeed,
Shima tun daga ranar duk wani farin ciki ya k'aurace mishi, yana raye anma yafi kama da matacce, ko kukan ya kasa yi, idan ya fara kallon wuri ɗaya sai ya daɗe a haka, ko magana baiyi, tunsu Umma na ganin abun wasa harya fara damunsu, ada Zahra ce kawai ke kula dashi,
   Umma har sanyashi gaba take taita kukan kodai ya haukacene, gashinan dai har asibiti anje babu wani ci gaba, ko abinci aka ɗura sai anbi da ruwa zai haɗe,
  
Wata rana Zahra taje take bamasu Momie labarin halin da yake ciki, sai a sannanne majeeda na laɓe ta jiyo, taci kukanta harta gode ma Allah,
   Abdallah ne ta goya ta tafi dashi su Umma nata jajenshi, daga can ɗaki ya dinga jiyo kukanshi, takenan duk abubuwan da suka faru suka dunga dawo mishi, baisan sanda ya k'walla k'ara ba, sai a sannanne yayita kuka,
   Wani lokacinshi kanshi kukan yana maganin damuwa, sukaita murna jin ya dawo hankalinshi,

Aisha tana yawan zuwa ganinshi, duk da ba wata fira ke shiga tsakaninsu ba, anma tana k'ok'arin debe mishi kewa

A gurguje plz

©Rabiatu sk msh

Related Posts:

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts