💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
65-66
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Da safe tana kunna wayarta kiranshi ne ya fara shigowa, ba tare data duba bama ta ɗauka,
"Assalamu Alaiki" ya faɗa da daddaɗar muryarshi cikin nutsuwa,
"Wa'alaikas salam," ta amsa mishi,
"Hajja Majeeda ina fatan kin tashi lafiya" mamaki ne ya kamata sosae yanda har yasan sunanta,
"Yi hak'uri don Allah ban gane mai magana ba"
"wanda kike tsammanin kiranshi ne, ko kuma nace wanda kike tunani a halin yanzu"
"Banfa gane mai magana ba"
"kina neman k'arin bayani dai, anma daɗewarmu a jiya, bai kamata ki sauri mantawa dani haka ba, kamar yanda nima na kasa daina ganin kyakkyawar fuskarki"
"Shine kuma akace dole sai nayi tunaninka? Don Allah malam na faɗa maka fa ni matar aurece" ta faɗa da alama ya fara ɓata mata rai
"Ajiyan fa kamar naa yarda, kafin in gano gaskia, don Allah majeeda mu duka ba k'ananun yara bane, ki bani dama in faɗa miki abinda ke tafe dani" shiru ta mishi, hakan ya bashi damar ci gaba da magana,
"Sunana Shaheed, anma family namu sunfi kirana da sarki"
"sarki?" ta maimaita, ba tare da taa sani bama,
Yayi er dariya "da ina yaro kuka ne dani, shine mama na ta samun sarkin kuka"
Dariya ya bata, ta rik'a abinta ciki-ciki tana saurarenshi,
"ina rik'e da kamfanin mahaifina ne a halin yanzu, bana aikin gomnati, naayi karatun gaba da secondry har zuwa master's, sannan kuma kamar yanda na faɗa miki ina da Mata shekararmu biyar kenan da aure, Allah bai bamu haihuwa ba, ban taɓa tunanin auren MATA BIYU ba, sai jiya da na ganki, kallo ɗaya kika kwanta min a rai, Allah ya jarabceni da soyayyarki, don Allah Majeeda ki bani dama, ki shigo rayuwarmu nida iyalina, ina matuk'ar k'aunarki,
Shiru tayi kamar mai nazari, hakanan taji hawaye nason zubo mata,
"Don Allah kice wani abu Majeed, kice kin yarda, a shirye nake dana miye miki gurbin tsohon mijinki, na zame ma Abdallah tamkar mahaifinshi, ki amince dani, ni masoyinki ne na gaskia"
Kasa rik'e kukanta tayi, ta kashe wayar kawai ta jefar da ita, taci gaba da kukanta da ita kanta bata san dalilinshi ba, sai da tayi mai isarta, sannan ta shiga toilet ta wanke fuskarta, ta fita daga ɗakin tana jinshi yana sake kira ko kallon wayar batayi ba,
Kamar mai tsoron wayar ta kasa komawa ɗakin duk da taa gama abinda take, ta nemi wuri a falo ta fara kallon dole har marece yayi, sannan ta koma ɗakin,
Miss calls ɗinshi 99, ta kashe ta gaba ɗaya ta tura ta jikka ta ajje, wani irin nauyinshi takeji, don yaa wuce saurayi tunda harda Mata, zai kai irin 35 haka, wani irin yanayi takeji a kanshi, anma ta rasa ta yanda zata fassara yanayin, bata ɗauka bayan Majeed ba akwai namijin dazai iya tsaya mata a rai haka, ita tayaya ma zata fara soyayya,
Kwananta biyu bata kunna wayar ba, sai ana uku, gobe kenan lokacin da Daddy ya bata zai cika, tana gyara ma Abdallah kayanshi ya shigo da gudu,
"Auntie, Momie na kiya" ya koma da gudu yana faɗa mata, tana tambayarshi 'ina Momien' ko tsayawa baiyi ba,
Tana zuwa momie ta faɗa mata bak'one tayi, ta koma ta sako mayafi sannan ta fita,
Can ta hangoshi da Abdallah saman cinya sai surutu yake zuba mishi, hannunshi choculate har babu hannun rik'ewa, yana hango ta ya kasa daina kallonta, har tana harɗewa ta samu dai ta k'arasa, taja kujera ta zauna, sannan ta ɗan zamo ta gaidashi,
Ya amsa yana ta fara'a, har lokacin idonshi na kanta,
"ke kuma kalan naki salon horan kenan Majeeda?" ta k'ara k'asa da kanta tana wasa da yatsunta,
"Anan ɗinma babu amsa? Yau kwana nawa kin kashe waya da sai dai ki jini asibiti, kasa daure wa nayi yau nazo da k'afafuna sauraren Amsa"
"hhm" tace da alama duk ta takura da zaman, haka amsarta ta kasance, sai kuma "eeh" da "A'ah" shi kaɗai yake zuba surutunshi harya lura da yanayinta,
"Da alama yau baki cikin yanayin kodai sai a waya zaki bani amsar" da sauri tace, "toh shiknan" sai da ya murmusa, "in kuma naji a kashe gobe ki k'ara ganina" murmushi kawai tayi, ta mik'e ta tafi,
"ba bankwana?" ta kasa juyowa,
"Allah ya kiyaye hanya"
"Ameen" ya faɗa yana sauke Abdallah, bayan ya cika mashi aljihu da kuɗi,
Ya juya zai shiga motarshi saiga Daddy ya shigo, ya tsaya harya fito sannan yaje ya gaisheshi har k'asa cikin ladabi, ya tashi zai tafi ya tsayar dashi,
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment