💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
73-74
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
♠Naji Ra'ayoyinku da shawarwari, Nagode fa sosai😘
www.babymsh.blogspot.com
Sai da aka kira sallahr asubah ya lallaɓa ya sauketa daga jikinshi, yana tashi itama ta buɗe ido, da k'arfinta ta yunqura zata tashi, ya dawo zai rik'ota
"ina zakije?"
"wanka zanyi"
"tohh kwanta bara in haɗa miki ruwan"
"Zan iya fa"
"kedai ki kwanta nace"
"tohm ranka shi daɗe"
Ta koma ta kwanta ba don tanajin daɗin kwanciyar ba, don ko ina jikinta a ɓace yake, sai dai jinin ya daina zuba,
Shiya taimaka mata ya mata wankan, dak'yar ya barta ta gyara wurin duk da tace mishi ta warke, sannan ta koma ta kwanta bayan tayi sallah jinta take kamar bata taɓa ciwo ba,
"tashi fa zakiyi mu tafi asibiti"
"Ba buk'atar wani asibiti fa, na warke"
"kinason min wasa da baby ko? Da lafiyanki ma, jini kika zubar fa, na damu da sanin matsayin da babynmu yake ciki plz ki tashi mana" sai kuma yayi shiru muryarshi ta canja damuwa ne fal a ciki,
"Duk laifinane Majeeda, da nasan zaku cutu jiya duk buk'atar da nake da wlhy dana hak'ura, baki kyautamun ba da baki faɗamun ba tun wuri"
"Nima fa ban sani ba, anma fa tun kafinnan ne nakejin ciwon, karka zargi kanka shaheed, bara in shirya ɗin"
"tohm" ya faɗa kawai yayi zurfi cikin tunani, duk damuwah ce a ranshi,
Tare suka fito bayan sun shirya, karo sukaci da Maryam da kayan abinci a hannunta, ta tare su da murmushi,
"Yanzu nake shirin kawo muku break fast ashe harkun fito, bara in kai muku dinning" ta juya tana ci gaba da magana, wani irin farin ciki take ciki,
"inanan ina aiki, anma hankalina na wurinki, ya jikin naki?" sai da Majeeda tayi shiru cikin mamaki sannan ta bata amsa,
"Yayi sauk'i auntie, Kin tashi lafiya?"
"lafiya lau Majeeda," sannan ta juya wurin shaheed ta duk'a har k'asa cikin ladabi ta gaisheshi, ya amsa mata kamar shi yayi ciwon ba Majeeda ba, duk ya shiga damuwa,
Abincinma kaɗan yaci, ya tashi bayan yacema Majeeda ta sameshi a waje, harya juya zai tafi kuma ya dawo da kallonshi kan Maryam, cikin wani yanayin da har saida ta tsorata,
"Ya akai kikasan Majeeda bata lafiya?" kame-kame ta shiga yi, tama rasa amsar da zata bashi, Majeeda ce tayi murmushi,
"Ba daɗewa fa ka faɗa mata zamuje asibiti" da sauri Maryam ta ɗago tana yak'e,
"eeh mana, kaine ka faɗa"
Har lokacin kallonta yake, don yasan kishi babu abinda bai saka mata, kuma bai manta da maganin data kawo mata ba, don ranar ne kawai ta taɓa bata magani da kanta, shi yamayi tunanin k'wayar maganinne tunda a hannu tazo dashi,
"tunda muka fito bamui maganar asibiti ba,"
"Miye haka Shaheed?" majeeda ta tambayeshi, hannu ya ɗaga mata yana kallon Maryam, can dubara tazo mata,
"Wai Yau nice kake tsarewa da tambaya saboda na nuna kulawa a kan matarka? Jiya kukan data dinga yi tana wayyo cikina waye baiji ba? Ban taɓa tunanin hakan daga gareka ba Shaheed" sauke ajiyar zuciyah yayi sai kuma baiji daɗi ba,
"Kinsan na yarda dake da yawa Maryam, kiyi hak'uri, na fara tsorone kada ko kishi ya saka kin fara canja halaye, ina tsoran halin Matan yanzu"
"Duk k'ok'arin da nake akan matarka anma abunda zakamun kenan don yanzu ka samu ɗa? Ni kake zargi Shaheed? Ni....?" ta kasa magana ma saboda kuka,
"ba haka bane Maryam kiyi hak'uri don Allah" tashi tayi ta ruga da gudu ɗakinta, dak'yar take gudunma saboda kib'a, yabi bayanta, Majeeda ta samu wuri ta zauna duk taa damu itama,
Sun daɗe yana rarrashinta kafin su fito, tana dariya kamar ba itace ta gama kuka ba,
"Tohh Majeeda a dawo lafiya"
"Ameen Auntie, ban gajia kullum da gode miki, inama kowacce mace addu'ar samun kishiya kamarki, kici gaba da hak'uri damu plz"
"ba komi Majeeda, anma zai addu'arnan taki....,ba kowacce mace keson kishiya ba"
"indai irinki ce Auntie kowah ma zai so" murmushi Maryam tayi ita kaɗai tasan fassaranshi,
"Tohh shknan saikun dawo, Allah ya baki lafiya"
"Ameen"
Sannan ta koma ciki, su kuma suka tafi asibiti,
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment