New Post

Sunday, 22 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 79-80

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  79-80

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

Bayan shekara Uku...
Majeeda ta kwantar da hankalinta, Yanzu ta zama lecturer a makarantar Umyu katsina, tsakaninta da Majeed sai dai mutunci kawai na en uwah, gida ma ganin halin da take ciki ya saka ko maganar aure basu mata, kullum dai suka mata Addu'ar zaɓi mafi Alkhairi,
    Aisha ne da Majeed kwance ya juya mata baya, ba barci yake ba, anma kuma yayi shiru kamar mai barcin,
    "Kayi shiru hniee inata magana ni kaɗai, kuma nasan ba barci kake ba" shirun ya k'ara mata,
    "kana jina fa" baice komi ba, ta kamo k'afarshi ta fara mishi susar k'adangaruwa,ba shiri ya fara dariya, ya kamota ya rungume, tureshi tayi suka fuskanci juna,
    "Wai hniee Meyasa kullum nake maka maganar dawo da Majeeda kake shareni? Wlhy na faɗa maka banda Matsala da hakan, kuma kunason junanku, ga Abdallah kullum k'ara girma yake, zaiso ya ganshi a tsakiyar iyayenshi"
   "ke ba mahaifiyarshi bace?"
   "Duk da haka nidai ka dawo da ita don Allah"
    Fuskarta ya jawo ya haɗa da tashi suna shak'ar numfashin juna "Hakan kikeso" ta ɗaga mishi kai,
    "Zanyi komai saboda farin cikinki, Anma nidai ki dainamun maganar zanyi tunani akan hakan"
   "naji anma baza'a ɗauka lokaci ba?" ya gyaɗa mata kai, duk wannan maganar da take k'arfin hali ne kawai, yana rungume da ita, ɗagotan da zaiyi yaga jinine ke fita ta hancinta, ta tafi luuu ta faɗa gefe, cikin tashin hankali ya rink'a jijjigata, ciwon nata nayau yafi na kullum ɗaga mishi rai, doguwar riga kawai ya ɗaura mata saman kayan barcin jikinta, ya ɗauketa a ruɗe ya saka mota, dak'yar ya iya driving zuwa asibiti,
      Har gari ya waye bata dawo hayyacinta ba, likitoci na iyakar k'ok'arinsu a kanta, en uwanta cike a asibitin, wata nurse ta lek'o tace "Waye Majeed?" da sauri ya matsa inda take yana cewa shine, yabi bayanta suka shiga Maryam na kwance ta farka, idanunya tsaye kanshi tana murmushi, ta mik'a mishi hannunta ya rik'e yana hawaye, ta ɗan ɓata rai da wasa,
    "Miye na kuka kuma hniee? Ka kwantar da hankalinka kaci gaba damun addu'a kamar yanda ka saba, wlhy koda mutuwa nayi ina cikin farin ciki sosae, burinah ya cika, na rayu na wani lokaci kuma zan mutu a matsayin matarka, kada ka manta da maganar da mukayi jiya da dare, kada ka manta dani Majeed" k'ara rirrik'e hannunta yayi,
    "bazaki barni ba Aisha, zamu rayu a tare insha Allah"
   Girgiza kai tayi "ban taɓajin ciwon da nakeji ba a yau, ni nasan wannan ciwon shine ajali na" ta k'ara lumshe ido dak'yar take magana, tashi yayi yana k'wala ma likita kira,  tak'i sakin hannunshi, ya juyo yana kallonta, murmushi ta k'ara mishi,
    "kada ka manta da alk'awarinmu na dawo da Majeeda" sannan ta sakeshi, ya tafi duk jikinshi yayi sanyi, suna dawowa da likita har rai yayi halinshi, anan Majeed ya faɗi sumamme, yasha jinya sosae Asibiti kafin ya ɗan samu,

Bayan shekara ɗaya,
Da mutuwar Aisha, Abdallah yanada shekara 10, ya zama ɗan saurayi, Maryam nada shekara 4, Majeeda ta zama babbar mace, 'yar gayu da ita, kullum k'ara kyau take, idan ka ganta bazaka ce tayi shekarunta ba, har Gida Maryam ɗin Shaheed tazo neman yafiyarta, Shaheed ma har kuka yayi na zafin rabuwa da ita, bata rik'esu da komai ba ta yafe musu, sannan ta barma Maryam, Maryam k'arama don har lokacin Allah bai bata haihuwa ba,

   Majeeda ce tafe cikin Mota, tana tuk'i cikin natsuwa, duk da saurin da take zuwa gidansu Umman shaheed saboda kiran gaggawar da aka mata, mintoci kaɗan ta isa gidan, mai gadi ya wangale mata gate ta shiga, daga makaranta take duk ta shawo gajia, kai tsaye falon bak'i ta wuce,
   Kamar yanda suka saba idan zasuyi meeting, kowa ya hallara, zahra ce kawai babu, ta gaishesu sannan ta samu wuri ta zauna, kallo ɗaya data ma Majeed ta k'ara hango ramar da yayi sosae,

Kuyi hak'uri plz da yanda nakeyinshi a gurguje plz👏🏻

©Rabiatu sk msh

Related Posts:

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts