New Post

ABUBUWA BAKWAI (7) ABIN KULA GA DAN'ADAM

1. Duniyar da za a barta, me ya kawo hadama? 2. Dukiyar da za a lissafa daya bayan daya, me ya kawo tarata? 3. Rayuwar da zata kare, ina wani farin ciki? 4. Yarintar da tsufa zai zo mzta, me ya kawo takama? 5. Ana sauraren mutuwa, ina wata walwala? 6. Jikin da zai zama gawa, me ya jawo dagawa? 7. Karshe dai makomarsa kabari, me zai sa alfahari? Wanda ya manta da wadannan a ina ya bar hankalinsa? Allah yasa mu dace, yayi mana kyakkaywan karshe. Ameen!

KADA KA RAMA CUTA GA WANDA YA CUCEKA!

Kar kayi wani abu mummuna don ka cutama wani, amma idan wani ya munana maka, kai kayi hakuri. Zaka samu abu biyu sakamakon hakan; * Na farko zaka samu ladan hakuri a wurin Allah. * Sannan zaka samu kwarjini a wurin wanda ya cuta ta maka.

KADA KA BARI ZUCIYARKA TA ZALUNCEKA!

Kada ka sale zuciyarka ta zalunceka, tabbas zaluncin zuciya ga gangar jiki yake komawa, idan akayi wasa ya zamanto ya shafi rayuwa. Assasa bak'in tunani, yawan zargi da rashin tabbas akan wani aiki, zato, shakku ko kokwanto akan wani al'amari batare da tantance gaskiyarsa ba, shine zaluncinzuciya akan dan Adam. Maza ka hana zuciyarka don akwai hadurra dubu akan hakan.

MAHAKURCI MAWADACI

Tabbas ba kowane dandanon magani ne ke da dadi ba, amma babu shakka shine abu mafi dacewa ga dukkan mara lafiya. A lokuta da dama rayuwa takan dakeka da guduma ta jefaka acikin wani mawuyacin hali, kayi ta fama amma tayi maka tutsu. Amma idan kayi hakuri sannu ahankali zata kwaranye. Hakika ba duk abinda rai yake so yakan samu ba, amma bukata bata taba sauyawa ba kuma bata taba karewa ba. Don haka ka shirya bukatunka da kyau ka bisu daya bayan daya sannu a hankali, kayi gwa- gwarmaya, sannan kayi juriya. Tabbas mafarkinka zai zama gaskiya.

KO KA SAN?

Rayuwa bakin alqalami ce tana bukatar kaifi sannan tana son tsini. Kaifin don ka yanki magauta, tsinin kuwa don ka soki makiya. Haka zalika rayuwa kamar randar ruwan sanyi ce ta kasa tana bukatar tanaji da adani, kodn wata rana ka shayar da masoyanka. Da kyau ka lura da abu biyu a rayuwa; 1. Ka lura da mai zaginka mai aibantaka wata kila wata rana zai iya zama masoyinka mai yabonka 2. Ka lura da masoyinka na kusa mai yawan ambaton alkhairinka, wata kila wata rana zai iya zama makiyinka mai zaginka.

Sunday, 22 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 81-82

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  81-82

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

Qarshe🤗

www.babymsh.blogspot.com

   Bayan ta samu wuri taa zauna, Abban Majeed yayi gyaran murya ya fara Magana,
      "Wannan karon ba Umarni bane muke baku, shawara ce muka yanke kuma duk saida amincewarku, abinda ya faru mu ɗauka k'addara ne, yanzu kuma dama ce garemu, mu cika Alk'awarin da mukai ma mahaifinmu, muna fatan wannan karan bazaku bamu kunya ba"
   Momie ce ta nisa, tun kafin kowah ya fara magana "Gaskia ni ban yarda da wannan hukuncin ba" su duka suka juyo suna kallonta, taci gaba da magana cikin fahimta,
      "Su duka yanzu ba k'ananun yara bane, kun manta abunda wancan haɗin ya haifar? Shiyasa ni ban cika magana ba, anma gaskia wannan lokacin bazan yarda a k'ara musu dole ba,  su koma halin da suka shiga wancan lokacin ba" Daddy ya katseta
    "Waye yace dole za'a musu? Suna da damar da zasu faɗi ra'ayoyinsu, karki manta da Alk'awari ne muka ma Mahaifinmu, ba don haka ba koda kansu suke so bazamu taɓa k'ara amincewa ba, kuma yanzunma idan har basu so bazamu k'ara tilasta su ba" shiru tayi bata k'ara magana ba,
   Abbah yace "ku muke saurare", Majeeda kanta a k'asa tun tana kuka a hankali harta fara shesshek'a, Majeed ma sai dai tashi yayi ya fita, fuskokin iyayen nasu duk ta nuna rashin jin daɗi, sunyi jugum kowa ya kasa motsawa, message ya shigo wayar Aunty zainabu, ta ciro ta tana ganin daga Majeed ne ta buɗe da sauri, da k'arfi ta karanta yanda kowah zaiji,
    "Ki tayani godia Auntynmu, kunyarsu ta hanani furta komai, sun nuna mana soyayyar da babu abinda zamu biyasu da ita, Allah ya saka musu da mafificin Alkhairi, ya k'ara musu tsawon kwana" kowa a ɗakin saida ya murmusa, sunyi farin ciki sosae, Majeeda ma murmushin jin daɗi take, ta mik'e da gudu ta fita, kunya bata barta ta jira kowah ba, ta shige motarta ta wuce gida,
   Cikin lokaci kaɗan aka fara hidimar biki, shagali sosae akayi wanda ko bikinsu na farko ba'ayi ba, cikin sati biyu aka gama komai aka kai Amarya ɗakinta,

   Bayan en rakiyarta sun gama tafiya, ta shek'a wankanta, tayi kwalliya ta fitar hankali, ko ina jikinta k'anshi yake, ga wata doguwar riga data saka ta daifi babu, irin shigarda tasan Majeed yafiso, sai dai ta ɗaura zani daga sama,
     Yana shigowa tsaye yayi a k'ofa yana kallonta, duk'arda kanta tayi sannan wata irin kunya ta saukar mata, ya ware mata hannuwa alaman tazo ya rungumeta, cikin zolaya tace "yau kuma ina laidan da za'a jefeni da ita?" daria yayi,
    "rufamun asiri zaki jamun ɗauri," itama tayi dariya,
   "nayi alwala fa, kai kawai nake jira"
    "tohm ranki shi daɗe"
  Ya shiga yayo alwala, ya fito, Sallah sukayi raka'a biyu kamar yanda manzon Allah ya koyar damu, ya daɗe yana kwararo musu addu'ar zaman lafiya, sannan sukai godia ga ubangiji,
    Ya rausayar da kanshi yana kallonta, rayuwarsu ta bayace ta dinga dawo mishi, wata irin soyayyarta na k'ara ratsashi, itama kamar hakan takeji, ta hure mishi idanu,
    "ka faɗa mana"
  "na rasa mezan faɗa ne, kullum k'ara kyau kike, bazaki taɓa tsufa ba"
   "kaima hakanne, babu wanda zaice kana da kaman Abdallah"
   "bazan iya bayyana miki farin cikin da nakeji ba da dawowarki gareni, wallahi ban taɓa sanin ina sonki da yawa haka ba saida na rasa ki, HARAMTACCEN ZAMA, ya k'are, Allah ya bamu ikon farantama juna har k'arshen rayuwarmu"
     "Ameen" ta faɗa

GODIYA
   Ta tabbata Ga Allah daya bani ikon kammala littafinnan lafiya, tsira da Aminci su k'ara tabbata ga annabinmu Muhammad (S.A.W), kuraren da suke ciki Allah ya yafe mana, Ameen,

Bani da bakin godia gareku Masoyana nesa da kusa, inajin daɗin yanda kuke nuna soyayyarku ma littafinnan, Allah yabar k'auna, sai kunjini a sabon littafina K'IYAYYA, anma bayan na dawo daga jigawa wurin kishia😊 labarin A HANYAR JIGAWA, yananan tafe ba daɗewa domin nishaɗinku,
   domin gyara ko shawarwari
      +2348032133670

SADAUKARWA
   wannan littafin sadaukarwa ne ga dukkan jikokin Alhaji sani katibu, duk sunayensu ne a ciki
     Manyan gobe, Allah ya raya mana ku ta farkin addinin musulunci, ya zaɓa muku abokan zama na gari, Ameen

IYAYENA
Allah yaji k'anshi mahaifinmu da rahma ya gafarta mishi, Allah ya k'ara tsawon kwana momienah, Allah ya saka miki da gidan Aljannah, hak'ik'a Uwah ce ta gari, ina sonta fiye da rayuwatah!

   NAGARTA WRITERS ASSOCIATION
    Ina Alfahri daku, Allah ya k'ara ɗaukaka, ya k'ara mana haɗin kai,

Godiya ta musanman,
   Da taimakonka ne na fara littafinnan harna k'areshi, ILILEE, nama rasa ta yanda zan gode maka, Allah ya k'ara basira, Ameen

AMINAN JUNA
   K'awaye na gari, babu kamarku a zuciyatah, RAZ, k'aunarku dabance a cikin zuciyatah, kalmomi bazasu iya bayyana farin cikin da nakeji kasancewarku cikin rayuwatah ba, Amrah A msh and Zahra bb, Allah ya bar tare.

   Beelybadaru, kina raina a koda yaushe😊

  En uwanah writer, gaisuwa mai yawa a gareku, Allah ya k'ara basira ya k'ara mana haɗin kai baki ɗaya,

    Duk group ɗin da nake ciki da wanda suke samun littafina, ina mik'a gaisuwa mai yawa gareku, Ma'assalam

Taku har kullum
    Rabiatu sani katibu mashi🙋🏻

HARAMTACCEN ZAMA 79-80

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  79-80

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

Bayan shekara Uku...
Majeeda ta kwantar da hankalinta, Yanzu ta zama lecturer a makarantar Umyu katsina, tsakaninta da Majeed sai dai mutunci kawai na en uwah, gida ma ganin halin da take ciki ya saka ko maganar aure basu mata, kullum dai suka mata Addu'ar zaɓi mafi Alkhairi,
    Aisha ne da Majeed kwance ya juya mata baya, ba barci yake ba, anma kuma yayi shiru kamar mai barcin,
    "Kayi shiru hniee inata magana ni kaɗai, kuma nasan ba barci kake ba" shirun ya k'ara mata,
    "kana jina fa" baice komi ba, ta kamo k'afarshi ta fara mishi susar k'adangaruwa,ba shiri ya fara dariya, ya kamota ya rungume, tureshi tayi suka fuskanci juna,
    "Wai hniee Meyasa kullum nake maka maganar dawo da Majeeda kake shareni? Wlhy na faɗa maka banda Matsala da hakan, kuma kunason junanku, ga Abdallah kullum k'ara girma yake, zaiso ya ganshi a tsakiyar iyayenshi"
   "ke ba mahaifiyarshi bace?"
   "Duk da haka nidai ka dawo da ita don Allah"
    Fuskarta ya jawo ya haɗa da tashi suna shak'ar numfashin juna "Hakan kikeso" ta ɗaga mishi kai,
    "Zanyi komai saboda farin cikinki, Anma nidai ki dainamun maganar zanyi tunani akan hakan"
   "naji anma baza'a ɗauka lokaci ba?" ya gyaɗa mata kai, duk wannan maganar da take k'arfin hali ne kawai, yana rungume da ita, ɗagotan da zaiyi yaga jinine ke fita ta hancinta, ta tafi luuu ta faɗa gefe, cikin tashin hankali ya rink'a jijjigata, ciwon nata nayau yafi na kullum ɗaga mishi rai, doguwar riga kawai ya ɗaura mata saman kayan barcin jikinta, ya ɗauketa a ruɗe ya saka mota, dak'yar ya iya driving zuwa asibiti,
      Har gari ya waye bata dawo hayyacinta ba, likitoci na iyakar k'ok'arinsu a kanta, en uwanta cike a asibitin, wata nurse ta lek'o tace "Waye Majeed?" da sauri ya matsa inda take yana cewa shine, yabi bayanta suka shiga Maryam na kwance ta farka, idanunya tsaye kanshi tana murmushi, ta mik'a mishi hannunta ya rik'e yana hawaye, ta ɗan ɓata rai da wasa,
    "Miye na kuka kuma hniee? Ka kwantar da hankalinka kaci gaba damun addu'a kamar yanda ka saba, wlhy koda mutuwa nayi ina cikin farin ciki sosae, burinah ya cika, na rayu na wani lokaci kuma zan mutu a matsayin matarka, kada ka manta da maganar da mukayi jiya da dare, kada ka manta dani Majeed" k'ara rirrik'e hannunta yayi,
    "bazaki barni ba Aisha, zamu rayu a tare insha Allah"
   Girgiza kai tayi "ban taɓajin ciwon da nakeji ba a yau, ni nasan wannan ciwon shine ajali na" ta k'ara lumshe ido dak'yar take magana, tashi yayi yana k'wala ma likita kira,  tak'i sakin hannunshi, ya juyo yana kallonta, murmushi ta k'ara mishi,
    "kada ka manta da alk'awarinmu na dawo da Majeeda" sannan ta sakeshi, ya tafi duk jikinshi yayi sanyi, suna dawowa da likita har rai yayi halinshi, anan Majeed ya faɗi sumamme, yasha jinya sosae Asibiti kafin ya ɗan samu,

Bayan shekara ɗaya,
Da mutuwar Aisha, Abdallah yanada shekara 10, ya zama ɗan saurayi, Maryam nada shekara 4, Majeeda ta zama babbar mace, 'yar gayu da ita, kullum k'ara kyau take, idan ka ganta bazaka ce tayi shekarunta ba, har Gida Maryam ɗin Shaheed tazo neman yafiyarta, Shaheed ma har kuka yayi na zafin rabuwa da ita, bata rik'esu da komai ba ta yafe musu, sannan ta barma Maryam, Maryam k'arama don har lokacin Allah bai bata haihuwa ba,

   Majeeda ce tafe cikin Mota, tana tuk'i cikin natsuwa, duk da saurin da take zuwa gidansu Umman shaheed saboda kiran gaggawar da aka mata, mintoci kaɗan ta isa gidan, mai gadi ya wangale mata gate ta shiga, daga makaranta take duk ta shawo gajia, kai tsaye falon bak'i ta wuce,
   Kamar yanda suka saba idan zasuyi meeting, kowa ya hallara, zahra ce kawai babu, ta gaishesu sannan ta samu wuri ta zauna, kallo ɗaya data ma Majeed ta k'ara hango ramar da yayi sosae,

Kuyi hak'uri plz da yanda nakeyinshi a gurguje plz👏🏻

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 79-80

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  79-80

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

Bayan shekara Uku...
Majeeda ta kwantar da hankalinta, Yanzu ta zama lecturer a makarantar Umyu katsina, tsakaninta da Majeed sai dai mutunci kawai na en uwah, gida ma ganin halin da take ciki ya saka ko maganar aure basu mata, kullum dai suka mata Addu'ar zaɓi mafi Alkhairi,
    Aisha ne da Majeed kwance ya juya mata baya, ba barci yake ba, anma kuma yayi shiru kamar mai barcin,
    "Kayi shiru hniee inata magana ni kaɗai, kuma nasan ba barci kake ba" shirun ya k'ara mata,
    "kana jina fa" baice komi ba, ta kamo k'afarshi ta fara mishi susar k'adangaruwa,ba shiri ya fara dariya, ya kamota ya rungume, tureshi tayi suka fuskanci juna,
    "Wai hniee Meyasa kullum nake maka maganar dawo da Majeeda kake shareni? Wlhy na faɗa maka banda Matsala da hakan, kuma kunason junanku, ga Abdallah kullum k'ara girma yake, zaiso ya ganshi a tsakiyar iyayenshi"
   "ke ba mahaifiyarshi bace?"
   "Duk da haka nidai ka dawo da ita don Allah"
    Fuskarta ya jawo ya haɗa da tashi suna shak'ar numfashin juna "Hakan kikeso" ta ɗaga mishi kai,
    "Zanyi komai saboda farin cikinki, Anma nidai ki dainamun maganar zanyi tunani akan hakan"
   "naji anma baza'a ɗauka lokaci ba?" ya gyaɗa mata kai, duk wannan maganar da take k'arfin hali ne kawai, yana rungume da ita, ɗagotan da zaiyi yaga jinine ke fita ta hancinta, ta tafi luuu ta faɗa gefe, cikin tashin hankali ya rink'a jijjigata, ciwon nata nayau yafi na kullum ɗaga mishi rai, doguwar riga kawai ya ɗaura mata saman kayan barcin jikinta, ya ɗauketa a ruɗe ya saka mota, dak'yar ya iya driving zuwa asibiti,
      Har gari ya waye bata dawo hayyacinta ba, likitoci na iyakar k'ok'arinsu a kanta, en uwanta cike a asibitin, wata nurse ta lek'o tace "Waye Majeed?" da sauri ya matsa inda take yana cewa shine, yabi bayanta suka shiga Maryam na kwance ta farka, idanunya tsaye kanshi tana murmushi, ta mik'a mishi hannunta ya rik'e yana hawaye, ta ɗan ɓata rai da wasa,
    "Miye na kuka kuma hniee? Ka kwantar da hankalinka kaci gaba damun addu'a kamar yanda ka saba, wlhy koda mutuwa nayi ina cikin farin ciki sosae, burinah ya cika, na rayu na wani lokaci kuma zan mutu a matsayin matarka, kada ka manta da maganar da mukayi jiya da dare, kada ka manta dani Majeed" k'ara rirrik'e hannunta yayi,
    "bazaki barni ba Aisha, zamu rayu a tare insha Allah"
   Girgiza kai tayi "ban taɓajin ciwon da nakeji ba a yau, ni nasan wannan ciwon shine ajali na" ta k'ara lumshe ido dak'yar take magana, tashi yayi yana k'wala ma likita kira,  tak'i sakin hannunshi, ya juyo yana kallonta, murmushi ta k'ara mishi,
    "kada ka manta da alk'awarinmu na dawo da Majeeda" sannan ta sakeshi, ya tafi duk jikinshi yayi sanyi, suna dawowa da likita har rai yayi halinshi, anan Majeed ya faɗi sumamme, yasha jinya sosae Asibiti kafin ya ɗan samu,

Bayan shekara ɗaya,
Da mutuwar Aisha, Abdallah yanada shekara 10, ya zama ɗan saurayi, Maryam nada shekara 4, Majeeda ta zama babbar mace, 'yar gayu da ita, kullum k'ara kyau take, idan ka ganta bazaka ce tayi shekarunta ba, har Gida Maryam ɗin Shaheed tazo neman yafiyarta, Shaheed ma har kuka yayi na zafin rabuwa da ita, bata rik'esu da komai ba ta yafe musu, sannan ta barma Maryam, Maryam k'arama don har lokacin Allah bai bata haihuwa ba,

   Majeeda ce tafe cikin Mota, tana tuk'i cikin natsuwa, duk da saurin da take zuwa gidansu Umman shaheed saboda kiran gaggawar da aka mata, mintoci kaɗan ta isa gidan, mai gadi ya wangale mata gate ta shiga, daga makaranta take duk ta shawo gajia, kai tsaye falon bak'i ta wuce,
   Kamar yanda suka saba idan zasuyi meeting, kowa ya hallara, zahra ce kawai babu, ta gaishesu sannan ta samu wuri ta zauna, kallo ɗaya data ma Majeed ta k'ara hango ramar da yayi sosae,

Kuyi hak'uri plz da yanda nakeyinshi a gurguje plz👏🏻

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 77-78

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  77-78

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    Lokacinda Maryam ta fahimci cikin Majeeda nanan bai fita ba, ba k'aramin kad'uwa tayi ba, ba shiri ta nemo Asiyah har ita suka koma wurin Malam, sai dai sunyi rashin sa'a ya tabbatar musu babu makawa sai an haife cikin, sai dai daga baya zaisan yanda yayi da yaron harma ita Majeedar tabar gidan,
   Bayan wata biyar Majeeda ta haifo santaleliyar yarinyarta Mace, ko ban fad'a ba kunsan ba k'aramin farin ciki iyalannan sukayi ba, har Maryam taji dad'in zuwan yarinyar, tun haihuwarta ita take hidima da ita, wani irin soyayyarta take ji,
    Ranar suna yarinya taci suna Maryam, shawarar Majeeda kenan, ta dage sai anyima Maryam takwara, ansha shagali sosae, tun ranar haihuwarta har washe garin suna, babu wanda bai shaida da haihuwar Maryam ba, harta da Aisha matar Majeed kullum tana gidan, don yanzu sun zama kamar en uwah,
   Kullum Maryam k'arama tana wurin Maryam, tsakaninta da Mamanta sai in tana rigimar yunwa, Shaheed ma acan ya tare b'angarenta wurin d'iyarshi, ita dai Majeeda ta zama er kallo,
    Tun tana da shekara guda suka yayeta, sai dai madara, ganin haka Maryam ta koma wurin Malam, da maganarsu ta baya kar Majeeda ta samu wuri tayita haifa ma Shaheed yara, ita kuma ta zama hoto, shima  abu ya bada da zata zuba mishi a abinsha, tace "shi yafi komai sauk'i malam" sannan tayi godia ta tafi,

    Majeeda na kwance, Shaheed ya shigo d'akin da Marece ne, tayi mamaki sosae don da wuya ya shigo idan ba dare ne ba,
    "Sannu da dawowa" baice komai ba yaci gaba da k'are ma d'akin kallo, duk da daman yanzu yaa daina kulata, sannan ya zura hannu Aljihu ya ciro takarda, ta kalleshi da mamaki,
   "takardar miye?" cikin yanayin da bai tab'a mata magana ba yace "in faɗa miki da baki mana, idan ni yaronki ne, Ansa ki duba" jikinta ba k'wari ta mik'a hannu ta amsa ta buɗa, Saki Uku ne reras, tana ganin haka ta kulle takardar idanunta cike da hawaye, ita kuma k'addarar da Allah ya ɗaura mata kenan,
      "Mena maka shaheed?"
   "kawai na gaji da zama dake, babu laifin da kikamun, ki tattara kawai ki tafi, sannan kuma karma ki sakaran tafiya da Maryam, tuntuni na barma Maryam ita" wani irin takaicine ya taso ma zuciyarta, wani irin kallon tsana take mishi,
     "Sai yanzu ne na fahimceka, lallai yau na yarda ka cika namiji, watau aurena kayi in haifa maka ɗiya ka cimun mutunci? Lallai idan ance maza DUK HAKA SUKE (littafina mai zuwa), bazanyi gardama ba, saika zauna dasu halayensu da baka taɓa tunani ba zasuna bayyana, ka  rusa duk wata yardar dana maka Shaheed, kaci amanatah, bazan taɓa yafe ma cutar dani da kayi ba, kuma Maryam nina haifeta babu inda zan tafi in barta"
    "Da ita kikazo? Zaifi miki ma daki manta da ita, don keda ita har abada, kuma kici gaba da zama har in dawo in sameki" ya fita fuuu yabar ɗakin, anan ta zube k'asa tasha kuka sosae kamar ranta zai fita, da kanta kuma ta rarrashi zuciyarta tayi shiru, jikkarta kawai ta ɗauka tabar gidan,
     Mai napep ya ajeta k'ofar gidansu, ta fito dak'yar take haɗa hanya ta shiga gida,
   Momie da Umma ne a ɗakin tazo gidan, Abdallah ma ya koma gidan babanshi a can ya sakashi makaranta, dak'yar har tana ganin jiri ta faɗa falon, wurin zama a kujera harta kusa faɗuwa, ta jinginar da kanta kawai tana dafe kanta dake mata ciwo sosae, duk suka taso sukayo inda take,
    Kasa basu amsoshin tambayoyinsu tayi, sai dai ta mik'a musu takardar dake hannunta, duk tare suka saki salati, sunyi matuk'ar tausaya mata, Umma kamar karta bar gidan don tausayin Majeeda, babu wanda zaiga halin da take ciki bai tausaya mata ba,

A gurguje dai....

©Rabiatu sk msh

Wednesday, 18 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 75-76

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  75-76

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    Tsadajjen Asibiti sukaje, ba ɓata lokaci sukaga likita, aka mata scanning da duk sauran abubuwa, likita ya tabbatar musu da babu wani abun daya samu cikinta, anma tana k'ara samun hutu sosae, (bed rest) saboda jinin data zubar, sunyi farin ciki sosae, ba kamar Shaheed saida yayi sujjadar godiya ga ubangiji, lallai Addu'ah bata faɗuwa k'asa banza,
    Sun fito tare suna tafiya taji yaro ya rirrik'e mata k'afafuwa,
    "Mamanah" muryar Abdallah taji da mamakinta, ta  juya shiɗin dai ne, ta ɗagoshi dak'yar zata ɗauka, Shaheed ya ansheshi,
   "Yanzunnan fa likita yace ki daina ɗaukar Abu mai nauyi"
     "Uncle"Abdallah ya faɗa, Shaheed ya harareshi da wasa,
   "bana hana Uncle ɗinnan ba" Abdallah yayi dariya,
   "Na daina Daddyna" Majeeda dai kallonshi kawai take baki buɗe,
     "kai dawa kukazo Asibiti?"
  "Nida Umma ne, ni kuma na fito" Majeeda ta kamo kunnenshi zata murɗe,
   "Yanzu yawonnan bazaka daina ba Abdallah?"
   "in zaki mishi faɗa kuma sai kinji mar ciwo? Zo muje kaji Abdallah Umma na can na nemanka" ya juya sukai gaba ta bishi a baya, duk nisan da yayi kau tsaf ya gane inda ya baro Umma, suka shiga batasan ma bainan ba,
   Suka gaisa da Umma, ashe Aisha ce batajin daɗi,
    "Umma Ashe Aisha bata lafiya kuma banji ba"
     "jikinne nata kullum ba daɗi Majeeda, Shiyasa ma bama faɗa"
   "Allah sarki, meke damunta"
  "har yau dai basu faɗa mana ba, anma jikin nata da sauk'i ma" 
     "Allah ya k'aro sauk'i Umma" ta k'ara kallonta, barcinta takesha, ita har manta kamanninta ma take, rabon data ganta tun tana gidan Majeed, hannunta ta duba,
    "Aikam na baro jikkata inda na zauna" Shaheed da keta shan surutu wurin Abdallah yace "bara in ɗauko miki tohh"
    "A'ah yi zamanka bara inje" ta fice da sauri tana tunano inda take ganin ta barota, cikin sa'a ta ganta, tana ɗauka ta juya zata tafi, ta jiyo maganarshi a kunnanta, bazata taɓa mantawa da muryarba, bazata taɓa manta yanayin da takeji idanta saurari muryar ba, shiru tayi ta kasa motsawa daga inda take, ko kallanshi ma batayi ba, wani irin yanayi da bazata iya fassarawa ba ta shiga, ganin haka ya canja akalar zancen,
      "ke haryau baki iya gaisuwa bane?" murmushi tayi jin ya tuno da lokacin da suke faɗa, kafin aurensu kenan,
   "Ayni banga Abinda zan gaisar ba anan"
       "lallaima yarinyar nan, yauma rashin kunyar zakimun?"
   "babu yarinya anan" ta bashi amsa,
   "idan nazo na murɗe wannan masifaffen bakin naki kinmu bayani"
   "Zan zauna ne ka murɗemun baki? Kaima kasan ba tsoranka...." sai kuma tayi shiru tana k'ok'arin maida hawayenta, su duka suka yi daria,
     "Gaskiya da munyi yarinta"  ta faɗa tana juyowa, shima dariyar yake, sai kuma yayi shiru, shima da damuwa a fuskarshi
    "lokacin da muka fara gane gaskiya kuma k'addara tayi halinta" sai yanzu ta ɗago suka haɗa ido, tun bayan rabuwarsu bata k'ara ganinshi ba, shekara kusan Uku, yayi fari ya k'ara kyau sosae, sai dai rama da yayi da alaman bai cikin kwanciyar hankali,
   "Yaya Majeed dukka rame" ita kanta batasan sanda ta faɗa ba,
   "kekam Matatah na kwance Asibiti, kullum ciwo, idan ban rame ba ya za'a gane nine mijin?" ya faɗa da zolaya, sosae ya bata daria,
    "Allah ya bata lafiya"
  "Ameen, kwana da yawa, faɗamun ya rayuwanki?"

"ba daɗi, tun bayan rabuwar mu, Munyi aure da shaheed, matsalan dangin miji, ga kishiya kullum saita zaneni, miji babu ruwanshi dani, babu ci babu sha, babu wanda zan faɗama matsalana, kaifa?" yaɗan murmusa, irin yanda yake idan taa gama burgeshi,
   "Munyi aure da Aisha, Masifa harta linka taki, safe daban rana daban, ba ruwanta damun girki, kullum tayi ficewarta bata tambayata, ta rainani batajin magana ta kuma..." yayi shiru yana tunani, suka k'arayin daria a tare,
   "ina cikin farin ciki yaya Majeed, bani da matsala da kowah"
   "nima haka Majeeda, Aisha macece ta gari, banda damuwa yanzu saita ciwonta kawai, sai muna tunanin taji sauk'i kuma abun ya dawo"
    "Insha Allahu zata samu lafia"
    "Ameen fa"
   "Yanzu dai mu manta da rayuwarmu ta baya, ko babu komai mu en uwanah ne, kina kallona a matsayin yayanki, komai ya wuce"
   "komai yaa wuce fa," ta faɗa tana share hawayenta cikin dubara, "bara inje yanzu zamu tafi"
     Ta juya ta tafi, shima bai iya ce mata komi ba, soyayyar gaskiya kenan, kowannensu k'ok'arin ɓoye damuwarshi yake da murmushi, anma a zuciyoyinsu sunajin ciwo sosae,
  Tana zuwa sallama sukayi da Umma, bayan ta k'ara duba Aisha, sosae ta bata tausayi,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 73-74

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  73-74

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

♠Naji Ra'ayoyinku da shawarwari, Nagode fa sosai😘

www.babymsh.blogspot.com

   Sai da aka kira sallahr asubah ya lallaɓa ya sauketa daga jikinshi, yana tashi itama ta buɗe ido, da k'arfinta ta yunqura zata tashi, ya dawo zai rik'ota
     "ina zakije?"
   "wanka zanyi"
       "tohh kwanta bara in haɗa miki ruwan"
   "Zan iya fa"
  "kedai ki kwanta nace"
     "tohm ranka shi daɗe"
  Ta koma ta kwanta ba don tanajin daɗin kwanciyar ba, don ko ina jikinta a ɓace yake, sai dai jinin ya daina zuba,
    Shiya taimaka mata ya mata wankan, dak'yar ya barta ta gyara wurin duk da tace mishi ta warke, sannan ta koma ta kwanta bayan tayi sallah jinta take kamar bata taɓa ciwo ba,
   "tashi fa zakiyi mu tafi asibiti"
   "Ba buk'atar wani asibiti fa, na warke"
 

"kinason min wasa da baby ko? Da lafiyanki ma, jini kika zubar fa, na damu da sanin matsayin da babynmu yake ciki plz ki tashi mana" sai kuma yayi shiru muryarshi ta canja damuwa ne fal a ciki,
   "Duk laifinane Majeeda, da nasan zaku cutu jiya duk buk'atar da nake da wlhy dana hak'ura, baki kyautamun ba da baki faɗamun ba tun wuri"
   "Nima fa ban sani ba, anma fa tun kafinnan ne nakejin ciwon, karka zargi kanka shaheed, bara in shirya ɗin"
    "tohm" ya faɗa kawai yayi zurfi cikin tunani, duk damuwah ce a ranshi,

   Tare suka fito bayan sun shirya, karo sukaci da Maryam da kayan abinci a hannunta, ta tare su da murmushi,
    "Yanzu nake shirin kawo muku break fast ashe harkun fito, bara in kai muku dinning" ta juya tana ci gaba da magana, wani irin farin ciki take ciki,
    "inanan ina aiki, anma hankalina na wurinki, ya jikin naki?" sai da Majeeda tayi shiru cikin mamaki sannan ta bata amsa,
    "Yayi sauk'i auntie, Kin tashi lafiya?"
  "lafiya lau Majeeda," sannan ta juya wurin shaheed ta duk'a har k'asa cikin ladabi ta gaisheshi, ya amsa mata kamar shi yayi ciwon ba Majeeda ba, duk ya shiga damuwa,
    Abincinma kaɗan yaci, ya tashi bayan yacema Majeeda ta sameshi a waje, harya juya zai tafi kuma ya dawo da kallonshi kan Maryam, cikin wani yanayin da har saida ta tsorata,
    "Ya akai kikasan Majeeda bata lafiya?" kame-kame ta shiga yi, tama rasa amsar da zata bashi, Majeeda ce tayi murmushi,
    "Ba daɗewa fa ka faɗa mata zamuje asibiti" da sauri Maryam ta ɗago tana yak'e,
   "eeh mana, kaine ka faɗa"
   Har lokacin kallonta yake, don yasan kishi babu abinda bai saka mata, kuma bai manta da maganin data kawo mata ba, don ranar ne kawai ta taɓa bata magani da kanta, shi yamayi tunanin k'wayar maganinne tunda a hannu tazo dashi,
   "tunda muka fito bamui maganar asibiti ba,"

    "Miye haka Shaheed?" majeeda ta tambayeshi, hannu ya ɗaga mata yana kallon Maryam, can dubara tazo mata,
    "Wai Yau nice kake tsarewa da tambaya saboda na nuna kulawa a kan matarka? Jiya kukan data dinga yi tana wayyo cikina waye baiji ba? Ban taɓa tunanin hakan daga gareka ba Shaheed" sauke ajiyar zuciyah yayi sai kuma baiji daɗi ba,
     "Kinsan na yarda dake da yawa Maryam, kiyi hak'uri, na fara tsorone kada ko kishi ya saka kin fara canja halaye, ina tsoran halin Matan yanzu"
   "Duk k'ok'arin da nake akan matarka anma abunda zakamun kenan don yanzu ka samu ɗa? Ni kake zargi Shaheed? Ni....?" ta kasa magana ma saboda kuka,
    "ba haka bane Maryam kiyi hak'uri don Allah" tashi tayi ta ruga da gudu ɗakinta, dak'yar take gudunma saboda kib'a, yabi bayanta, Majeeda ta samu wuri ta zauna duk taa damu itama,
    Sun daɗe yana rarrashinta kafin su fito, tana dariya kamar ba itace ta gama kuka ba,
   "Tohh Majeeda a dawo lafiya"
   "Ameen Auntie, ban gajia kullum da gode miki, inama kowacce mace addu'ar samun kishiya kamarki, kici gaba da hak'uri damu plz"
    "ba komi Majeeda, anma zai addu'arnan taki....,ba kowacce mace keson kishiya ba"
  "indai irinki ce Auntie kowah ma zai so" murmushi Maryam tayi ita kaɗai tasan fassaranshi,
    "Tohh shknan saikun dawo, Allah ya baki lafiya"
   "Ameen"
  Sannan ta koma ciki, su kuma suka tafi asibiti,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 71-72

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  71-72

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

Ta juyo wurin Majeed tana mishi murmushi,
    "Auntynah tana ji dani sosai"
     "gaskia ne, nayi sa'a sosai da samun mata na gari"
   "Muma munyi sa'a da samun miji na gari, da kowacce mace zatayi alfahrin samu"
  Ya jawota bayan ta gama saka rigar barcinta,
   "hajia nifa na gaji da wannan jan lokacin" ya kashe musu fitila, saboda yau cikin tsananin buk'atarta yake,

   Tun lokacin daya fara da shasshafa jikinta ta fara jin wani yanayi a jikinta, can cikinta takejin kamar wani abu na motsi anma ba sosae ba yana ɗan tsira, bata ɗauka wani abune daban ba, anma ciwon har tsakiyar kanta take ji, kasa taɓuka komi tayi, wani irin azaba ta dingaji bayan ya tashi ya shiga wanka, kamar tafiyar tsutsotsi haka ta dinga ji a cikinta duk yaa yamutse kamar ana cin kayan cikinta, ga wani irin zafi kamar ana dahuwa a ciki,
   A haka ya dawo ya iske majeeda,
     "wankan fa dear?" shaheed ya tambayeta,
  Dak'yar ta iya buɗa baki tana cije leɓe,
      "zan tashi inyi" baima lura da yanayin da take ciki ba, yaja bargo ya kwanta,

  Haka ta dinga juye-juye, hannuwanta biyu ta dinga sawa tana matse cikin ko zataji sassauci, kamar ruɓaɓɓen abu haka takejin cikin, ta sauko qasa komai ta samu ɗaura ma cikin take ta dinga juye-juye, da taji dai abun bamai k'arewa bane, ko nak'udar Abdallah bataji azaba haka ba, a kwance ta dinga jan jiki har inda Shaheed yake, ta dinga tashinshi, baimasan tanayi ba barcinshi yayi nisa,
    Hawaye ta dinga zubarwa masu zafi, ko ina jikinta ciwo yake kamar ba nata ba, ko hannunta bata son motsawa maganar ma ciwon buɗa baki takeji, haka ta dinga daurewa tana kiranshi, ta saka hannu tana bubbugashi, wani masifaffen ciwon nema idan jikinta ya haɗu da nashi,
   Jinta tayi taa jik'e kamar wacce tayi fitsari, a ruɗe ta saka hannu ta shafa k'asanta, jinine ta gani a malale, ba k'aramin ruɗewa tayi ba, ta fara wani irin kuka,
   "Na shiga Uku, ya Allah ka taimakeni kar in rasa wannan farin cikin na shaheed, don Allah ka tashi shaheed, karmu  rasa abunnan da muke matuk'ar so, ka tashi shaheed karka rasa mu" haka ta dinga kuka, tana sambatun da azabarma bata bari tasan tana yi ba,
    Maryam na jiyota daga inda take laɓe, ta koma ɗaki cikin farin ciki bama kamar da taji Shaheed baisan tanayi ba, anma kuma a yanda take jin tana magana dak'yar tausayinta take ji sosae, da kuma tausayin shaheed idan ya rasa wannan cikin na Majeeda daya k'wallafa rai a kanshi,

    Sai da ta galabaita sosae, harta suma a wuri sannan shaheed ya farka, da sauri ya buɗe idanunshi ganin halin da Majeeda take ciki kwance a gabanshi bata ko motsi, cikin tashin hankali ya shiga girgizata anma ko motsi ba tayi, ga jini malale a jikinta daya qara tayar mishi da hankali,
    Fridge ya ɗauko robar ruwa ya dawo inda take ya fara kwara mata, ta saki wata doguwar ajiyar zuciyar, idanunta sun k'ank'ance saboda azaba ta shiga hawaye,
    "Cikina Shaheed, mutuwa zanyi, mutuwa zamuyi nida babynmu"
   "bazaki mutu ba Majeeda, rayuwatah tana buk'atarki, don Allah kicemun babu abinda ya samu babynmu" girgiza kan zafin ciwo kawai take, tana hawaye, duk ya fita hayyacinshi,
   Ganin yanda take dafe da cikinta, da alama tana cikin azabar ciwo, ya ɗauko robar ruwan ya shiga tofa mata addu'ah, wadda RAZ suka kawo a littafin dodon jatau, da kuma ayatul kursiyyu, suratul ikhlas, falaq da nas, kowanne sau Uku, ya dawo fuskarta ya bata tasha, sannan ya kwantar da ita, ya shafe mata fuskarta da cikin, da hannuwanta da k'afafuwanta, ta kwantar da kanta kawai jikinshi, tayi shiru tanajin ciwon na lafawa kaɗan-kaɗan,
   A haka barci ya ɗauketa jikinshi, ya gyara mata kwanciyar, bai koma barci ba, sai dai ya ɗauko Al-Qur'ani yana karanta mata har aka kira sallah, kallon tausayi kawai yake mata, kamar ya cire ciwon ya maida a jikinshi, rok'on Allah ya shiga yi daya kare mishi abunda ke cikinta, yasa babu abinda ya sameshi

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 69-70

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  69-70

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Cikin Majeeda nada wata hudu, k'awar Maryam tazo ta iskesu suna fira da Majeeda, sai dariya suke bazaka taɓa cewa kishiyoyi bane, ko gaisuwar Majeeda dak'yar ta amsa taja Maryam suka shige ɗakinta, tun kafinsu zauna tayi k'asa da Murya,
    "Me nake faɗa miki Maryam? Ke har yanzu kin kasa gane inda ke miki ciwo"
   "ko kuma kece kika kasa fahimtata Asiya, nifa babu abunda yarinyarnan ta tsaremun"
    "Aikam baki shirya ganin aibun kishiya ba, wallahi karki ga yanzu da cikinnan yana miki kawaici, tana ajje ɗa a cikin gidannan keda babu duk ɗaya, a hakan ma ya aka k'are? Wallahi duk yanda kikeson Shaheed tana haihuwa zata rabaki dashi"
  Anzo wurin, don babu abinda Maryam tafi tsana a rayuwarta kamar ace zata rasa Shaheed, "Tohh anma Asiya, nima fa inason inga yaro a cikin gidannan, shekara nawa bamu samu ba?
   "Zaki ga yaro a cikin gidannan, anma kina da iko dashi? Wata da tazo cikin ɗan lokaci zata rabaki da gidanki, idan kuma so kike sai lokaci yayi ki bani labari tohh in saka miki ido"
    "inaaa zan zauna? Nidai yanzu ya za'ayi?"
   "kuɗi kaɗan zaki bada, yanzu daganan wurin wani malamin zaure zanje a lalata abinda ke cikinta, daganan kema in anso miki maganin haihuwan"

   "da gaske nima zan samu haihuwan?"
  "indai kinyi yanda akace, kuma saikin yarda da malamin sannan zaki ga aiki",
   "gaskia wannan ba k'aramin Albishir bane, anma don Allah kar ayma Majeeda wani mugun abu" tsoki Asiyah taja,
   "hajia idan kinason aiki, ki tashi ki ɗauko yanzu in dawo miki da magani, da zafi-zafi ake dukan k'arfe"
   "inaso mana, yanzu kuwa"
Ta tashi ta lalubo mata kuɗi ta bata, har bakin gate ta raka ta sannan ta dawo,

   Ranar Majeeda keda Shaheed, Anma Maryam ita tayi komai kamar yanda ta saba, babu wani canji a tare da ita, bayan sunyi dinner yaja matarshi suka wuce ɗaki,
    Ta fito daga wanka tana ɗaure da towel, ta isa gaban mirrow ta zauna zata fara shafe-shafe, suka haɗa ido ta cikin madubin yana kwance ya k'ura mata ido, suka sakar ma juna murmushi,
   "banson kallo fa"
   "laifine don mutum ya kalla matarshi? kawai tunani nake"
   "tunanin me kuma?"
  "Da wanne irin farin ciki zan kasance a ciki? Idan ya kasance dake na fara rayuwa"
  "hhm zaka fara ko"
  "wallahi da gaske nake Majeeda, ban taɓa farin ciki ba kamar ranar dana fara ganinki, kowanne dak'ik'a ɗaya da nayi tare dake, ina alfahri dasu, ji nake kamar donke kaɗai akayi zuciyatah, kece farin cikina"
    "nima ina farin ciki dakai sosae, inajin daɗin kasancewa dakai, ina sonka fiye da kowacce halitta dake doron k'asa" ita kanta batasan sanda maganar ta fito mata ba, anma tasan tabbas k'aryane ta faɗa,bata da kamar Majeed a zuciyarta,
  Cikin farin ciki ya tashi ya tare ta zata saka kaya,
    "da gaske kike kina sona fiye da kowa" cikin son subar maganar tace "da gaske mana, har kana k'ok'onton soyayyar da nake maka?"
   "A'ah wlhy, kina nufin har daddyn Abdallah kenan?"
    "wake Maganar daddyn Abdallah kuma yanzu?"
   "nidai inason sani plz, nasan kinso Majeed sosae Majeeda, kina nufin son da kikemun yanzu yafi nashi?"

   Rasa yanda zatayi tayi, duk ya tsareta da tambaya, gashi batason ɓata mishi rai,
     "Soyayyar Majeed daban take a zuciyatah, ban taɓa tunanin zan iya koda kallon wani namiji a matsayin namiji ba bayanshi, anma a yanzu da nake tare dakai, banama tunawa dashi, nikam soyayyar da kake nunamin ma ta isa, ban buk'atar sanin tsakanin Ni da Aunty Maryam wakafi so, wannan sirrin zuciyarka ne"
   "ke ta dabance Majeeda, kalamanki suna matuk'ar tasiri a zuciyatah, kece wannan sirrin na zuciyatah, kinason sanin wa nafi so?....."

Girgiza mishi kai tayi, ba magana, ya jawota ya haɗa da jikinshi, ya fara aika mata da sak'onni cikin wani irin yanayi, m sai da aka turo k'ofa sannan sukai sauri suka saki juna,
   Maryam ce saida ta shigo tsakiyar ɗakin sannan ta fahimci halin da suke ciki, sai da ranta ya sosu, anma ta kanne kawai,
   "kuyi hak'uri na shigo muku kawai, bansan oga na ciki ba"
   "haba, Aunty keda ɗakinki kuma"
   "uhm, maganinki na kawo miki, nasanki da wasa dasha"
  Ta mik'a mata ruwa a cup da maganin, ko kaɗan bata kula da yanayin canjawar ruwanba, sai da ta kwankwaɗeshi tass, sannan ta mik'a mata cup ɗin,
    "nagode sosae Aunty"
  Ta ɓata rai "banson haka fa, sai da safenku" ta fita ta rufo musu k'ofa

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 67-68

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  67-68

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

A gurguje,,,,,,,,,

    Daddy yace "sai dai ban ganeka bane" cikin ladabi yace,
   "Sunana Shaheed ibraheem imamu Abba, nazo wurin Majeeda"
    "tohhhh, Alhaji ibraheem dai wanda na sani?"
    "eeh Abba"
"tohh masha Allah, idan ka koma gida saika turo iyayen naka, nan da wani ɗan lokaci sai a...."
    Don tsabar jin daɗi ma baisan sanda ya katse Daddy ba,  "Da gaske Abba" wani irin kallo ya mishi na rashin ganewa sannan ya gane bai kyauta ba, daya saka k'ok'onto a maganar, yaci gaba da washe baki ba kunya Shaheed kema Daddy godia,

   Washe gari lokacin daya ɗibarma Majeeda ya cika, tunda safe data shigo gaisheshi ya tsayar da ita,
    "kina sane da yau ne lokacin dana ɗibar miki ya cika"
    "eeh Abba, bani da wani zaɓi, Insha Allah zanyi biyayya ga duk mijin daka zaɓamun"
    "Tohh tashi kije, Allah ya miki Albarka, daga yau ki fara shirye-shiryen bikinki nan da wani ɗan lokaci" wani irin faɗuwar gaba taji,
    "Ameen Daddy" ta mik'e jiki ba k'wari tabar ɗakin, tohh anma meyasa bata faɗa ma Daddy Shaheed ne zaɓinta ba? Kuma dai gani take kamar yaa fasa don tun bayan tafiyarshi, bai nemeta a waya ba, koba wannan ma yanzu tafiso Daddy ya sake mata wani zaɓin da kanshi, don ta samu ta mishi biyayyar data kasa a baya,

•••   •••   •••
   An kusa bikin Zahra, sai aka saka lokaci ɗaya, Duka bangarorin sai shirye-shiryen biki suke, su Majeed anzo biki, shi yanzu hankalinshi kwance, soyayya da kulawa babu wanda bai samu a wurin Aisha, tuni ya manta da komai ya rungumo matarshi don ba k'aramin so take mishi ba,
   Majeeda ma tunda hidimar bikin ta kama, ta kwantar da hankalinta, bama kamar da taasan Shaheed ne zata aura, ta kasa yarda ne, anma wani ɓangare na zuciyarta faɗa mata yake ta fara kamuwa da soyayyar Shaheed,

     Ansha shagalin biki, garin Mashi aka kawo mana Zahra😉, Majeeda kuma Aka ajeta Katsina Layout, taci kuka sosai, kamar shine aurenta na farko,
    Da dare ya kirasu ita da uwargida domin musu nasihar zaman lafiya, tana zaune kafin uwar gidan ta fito taa tsura ma wani hotanta dashi ido, sunyi kyau sosae tana tsaye ya rungumota daga baya suna dariya, kyakkyawahce anma bata da haske sosae da ɗan k'aramin jikinta mai kyau,
    Jin tafiyarta ne yasa Majeeda ta daina kallon hotan ta maida kanta k'ansa, ta zauna kujera mai kallon wacce suke sai k'amshi take zubawa, da yake Maryam akwai tsafta,
     Sai da ta ɗago ta kalleta ne, kamar ba itace a hotonnan ba, tayi wata uwar k'iba sosae, irin hajiyoyinnan, cif ta cika kujera mai zaman mutum ɗaya, babbar mace mai halin dattako, bai ɗauki wani lokaci yana musu bayani ba, ya sallamesu kowa ta koma ɗakinta,

    Zaman su da Maryam sosai takejin daɗinshi, tana janta a jiki, har dangin shaheed take janta kasancewarta mace mai zumunci, da fahimta, ɓangaren Shaheed ma bata da wata matsala, yana bata kulawa sosai yakeji da iyalanshi, bata da wata damuwa yanzu,
    Sai dai kewar Abdallah da yanzu yake hannun Umma, kowa yaso a bar mishi shi, sai daga k'arshe suka hak'ura aka barma Umma,

    Watansu Uku da aure Allah ya albarkaceta da juna biyu, ba k'aramin farin ciki Shaheed da Maryam sukayi ba, kusan ma Maryam duk ta fisu Murna, tun daga lokacin ta ɗaukema Majeeda duk wata hidimar gida, ita take kula da ita, sai abinda takeso za'a girka, Maryam mace ta gari ce sosae, kusan tare suke rainon cikin,
   Har mamakin Maryam take, mace mai kawaici da k'ok'arin danne kishi, irinsu kaɗanne a duniyar nan, ko godiya take mata sai dai tace
    "banson haka fa Majeeda, ni ban taɓa kallonki a matsayin kishiya ba sai dai er uwa, abinda muka daɗe muna Addu'ar nema ne da Shaheed, Allah bai bamu ba, kuma yaa nufeki da samu, ina tayashi son duk abunda yakeso, wallahi ji nake duk ɗayane"
     "Gaskiyarki Auntyna, ina yima kowacce mace Addu'ar samun kishiya ta gari kamarki" Maryam tayi daria,
    "da kuma macce ta gari kamar ki ba" sukai dariya gaba ɗaya, kamar ba kishiyoyi ba,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 65-66

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  65-66

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Da safe tana kunna wayarta kiranshi ne ya fara shigowa, ba tare data duba bama ta ɗauka,
   "Assalamu Alaiki" ya faɗa da daddaɗar muryarshi cikin nutsuwa,
   "Wa'alaikas salam," ta amsa mishi,
   "Hajja Majeeda ina fatan kin tashi lafiya" mamaki ne ya kamata sosae yanda har yasan sunanta,
   "Yi hak'uri don Allah ban gane mai magana ba"
   "wanda kike tsammanin kiranshi ne, ko kuma nace wanda kike tunani a halin yanzu"
   "Banfa gane mai magana ba"
  "kina neman k'arin bayani dai, anma daɗewarmu a jiya, bai kamata ki sauri mantawa dani haka ba, kamar yanda nima na kasa daina ganin kyakkyawar fuskarki"
     "Shine kuma akace dole sai nayi tunaninka? Don Allah malam na faɗa maka fa ni matar aurece" ta faɗa da alama ya fara ɓata mata rai
   "Ajiyan fa kamar naa yarda, kafin in gano gaskia, don Allah majeeda mu duka ba k'ananun yara bane, ki bani dama in faɗa miki abinda ke tafe dani" shiru ta mishi, hakan ya bashi damar ci gaba da magana,
   "Sunana Shaheed, anma family namu sunfi kirana da sarki"
   "sarki?" ta maimaita, ba tare da taa sani bama,
  Yayi er dariya "da ina yaro kuka ne dani, shine mama na ta samun sarkin kuka"
   Dariya ya bata, ta rik'a abinta ciki-ciki tana saurarenshi,

   "ina rik'e da kamfanin mahaifina ne a halin yanzu, bana aikin gomnati, naayi karatun gaba da secondry har zuwa master's, sannan kuma kamar yanda na faɗa miki ina da Mata shekararmu biyar kenan da aure, Allah bai bamu haihuwa ba, ban taɓa tunanin auren MATA BIYU ba, sai jiya da na ganki, kallo ɗaya kika kwanta min a rai, Allah ya jarabceni da soyayyarki, don Allah Majeeda ki bani dama, ki shigo rayuwarmu nida iyalina, ina matuk'ar k'aunarki,

   Shiru tayi kamar mai nazari, hakanan taji hawaye nason zubo mata,
   "Don Allah kice wani abu Majeed, kice kin yarda, a shirye nake dana miye miki gurbin tsohon mijinki, na zame ma Abdallah tamkar mahaifinshi, ki amince dani, ni masoyinki ne na gaskia"
    Kasa rik'e kukanta tayi, ta kashe wayar kawai ta jefar da ita, taci gaba da kukanta da ita kanta bata san dalilinshi ba, sai da tayi mai isarta, sannan ta shiga toilet ta wanke fuskarta, ta fita daga ɗakin tana jinshi yana sake kira ko kallon wayar batayi ba,

   Kamar mai tsoron wayar ta kasa komawa ɗakin duk da taa gama abinda take, ta nemi wuri a falo ta fara kallon dole har marece yayi, sannan ta koma ɗakin,
   Miss calls ɗinshi 99, ta kashe ta gaba ɗaya ta tura ta jikka ta ajje, wani irin nauyinshi takeji, don yaa wuce saurayi tunda harda Mata, zai kai irin 35 haka, wani irin yanayi takeji a kanshi, anma ta rasa ta yanda zata fassara yanayin, bata ɗauka bayan Majeed ba akwai namijin dazai iya tsaya mata a rai haka, ita tayaya ma zata fara soyayya,
       Kwananta biyu bata kunna wayar ba, sai ana uku, gobe kenan lokacin da Daddy ya bata zai cika, tana gyara ma Abdallah kayanshi ya shigo da gudu,
    "Auntie, Momie na kiya" ya koma da gudu yana faɗa mata, tana tambayarshi 'ina Momien' ko tsayawa baiyi ba,
  Tana zuwa momie ta faɗa mata bak'one tayi, ta koma ta sako mayafi sannan ta fita,

     Can ta hangoshi da Abdallah saman cinya sai surutu yake zuba mishi, hannunshi choculate har babu hannun rik'ewa, yana hango ta ya kasa daina kallonta, har tana harɗewa ta samu dai ta k'arasa, taja kujera ta zauna, sannan ta ɗan zamo ta gaidashi,
    Ya amsa yana ta fara'a, har lokacin idonshi na kanta,
   "ke kuma kalan naki salon horan kenan Majeeda?" ta k'ara k'asa da kanta tana wasa da yatsunta,
  "Anan ɗinma babu amsa? Yau kwana nawa kin kashe waya da sai dai ki jini asibiti, kasa daure wa nayi yau nazo da k'afafuna sauraren Amsa"
   "hhm" tace da alama duk ta takura da zaman, haka amsarta ta kasance, sai kuma "eeh" da "A'ah" shi kaɗai yake zuba surutunshi harya lura da yanayinta,
    "Da alama yau baki cikin yanayin kodai sai a waya zaki bani amsar" da sauri tace, "toh shiknan" sai da ya murmusa, "in kuma naji a kashe gobe ki k'ara ganina" murmushi kawai tayi, ta mik'e ta tafi,
   "ba bankwana?" ta kasa juyowa,
   "Allah ya kiyaye hanya"
       "Ameen" ya faɗa yana sauke Abdallah, bayan ya cika mashi aljihu da kuɗi,

   Ya juya zai shiga motarshi saiga Daddy ya shigo, ya tsaya harya fito sannan yaje ya gaisheshi har k'asa cikin ladabi, ya tashi zai tafi ya tsayar dashi,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 63-64

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  63-64

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

    "hajia ki rok'eni kawai in kai miki yaronki gida" bata saurareshi ba taci gaba da lallashin Abdallah yazo su tafi, anma yak'i yama maida ita kamar k'awar wasanshi,
   "Abdallah bazaka je gida ba?", ya tambayeshi, shikau harda saurin ɗaga kai,
   "Meyasa?" yayi shiru da yake maganarshi ba k'wari tayi ba,
   "mu tafi can muyi wasan ko"
  "eeh janje didan"
     "Yauwah tohh mu tafi yaron kirki" ya ɗaurashi a kafaɗa sukai gaba don yaga hanyar da Majeeda ta biyo,
   "Auntie mu tafi ko? Nima zan wuce gidane yanzu, ko an barmun shi?" batace mishi komi ba dai tabi bayanshi, suka tafi, sai da sukaje dai-dai gidan tace "tohh sauke minshi anan" ana saukeshi kau yayi cikin gidan da gudu,
   "na gode" tace mishi kawai, sannan tabi bayan Abdallah, yayi tsaye a k'ofar yana kallonta harta shige,

   Mai gadin ya taso rufe k'ofa ya ganshi nan tsaye, ya fasa rufewar bayan ya lek'o da kanshi,
    "Barka dai yallaɓai"
  "Yauwah baba, sannu da aiki" ya juya zai bar wurin,
   "Aiki da godia, wurin Alhaji kazo ne?"
  "A'ah yaron Matar gidan dai na maido"
   "matar gidan kuma? Ɗiyar Alhaji dai" harya fara tafiya ya dawo jin haka, baba mai gadi harda gyara tsayuwa zai fara tsegumi,
   "Shifa yaron?"
  "ɗanta ne, anma yanzu shekara ɗaya kenan da en watanni basu tare da mijin"
  Gaskiya mai gadinnan akwai surutu, mutumin ya faɗa a ranshi,
   "Allah sarki, nagode sosai baba" ya zaro dubu biyu ya mik'a mishi, ya amsa yana washe baki, don akwaishi da son kuɗi
   "ni keda godia yaro," sai kuma ya kasa tafiya, yayi shiru yana so yayi ma baba magana,
  "numberta zan baka?" da sauri ya ɗaga kai,
  "yauwah baba za'a samu ko"

  "eeh yaro, anma ka k'aro dubu biyar", yana kallon tudun Aljihunshi, ikon Allah wannan wanne irin mai gadi ne? Gashi dai tsoho sai tsurku da son gulma, ga shegen son kuɗi,
   Ya kwaso duk kuɗin Aljihunshu dubu uku,
  "gashi baba, daman su kaɗai suka rage"
  "tohh shknan yaro nima rabi zan baka tunda rabi ka bada" baza'ayi haka ba baba ina zuwa,
   Ya koma inda ya aje motarshi, ya jawota k'ofar gidan, ya dawo ya mik'a mishi dubu biyar cas sannan yace yana zuwa, ya shiga ɗakin da yake ya ɗauko wayar bala driver daya bari chaji ya kawo mishi,
   "Gashinan Alhaji duba, ko hajia Majeeda, ko Majeeda, ko er gatan Alhaji duk yanda kaga an rubuta"
   "Sunanta majeeda kenan" ya faɗa yana murmushi, "suna mai daɗi, kuma ya dace da ita,
  Ya maida mishi wayar yana godia bayan ya ɗauka number,

   Abdallah da gudu ya shige gidan, Majeeda na mishi magana bai tsaya ba saida yaje inda momie take ya faɗa jikinta yana daria, sannan taja ta tsaya tana kallonshi,
  "Abdallah ina ka tafine muna ta nemanka?"
   "wuyin uncle" ya fara lallaben Aljihunshi ya ciro chocolates yana bata,
   "shine ya baka wannan" ya ɗaga mata kai,
   "ka daina fita yawo kaji" nanma ɗaga kan yayi, sannan ya sauko kuma ya tafi wurin Majeeda ta ɗaukeshi, suka tafi ɗaki,
   Faɗa sosae ta mishi harya fara kuka, ta rungumeshi don batason ɓacin ranshi, ta share hawayen daya zubo mata,
   "ka daina rashin ji kaaji yaro nah"
   "baran kala fita ba"
  "yauwah nima naa daina maka faɗa" taci gaba da lallashinshi har yayi barci,

  Da dare harta kwanta, taji wayarta na ringing, ta jawo da duba bata gane number ba ta maida ta aje, mai kiran dai ya nace da kira gashi barci takeson yi, ta ɗauka kawai batayi magana ba,
   Ɗayan bangarenma shirun akayi, harta gaji da saurare ta kashe ta maida ta ajje, aka sake kira ta kashe wayar ma gaba ɗaya,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 61-62

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  61-62

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Kwana Uku da bikin Majeed har lokacin bata da wani natsuwa a tare da ita, zata fito dai ta taya Momie en aikace-aikacen da suka kamata, sai Momie tana janta da fira duk don taga hankalinta ya kwanta, anma data koma ɗaki sai wata sabuwar damuwar kuma,
   Yauma kamar kullum ta gama duk abinda take, ta shiga da Abdallah toilet ta sake mishi wanka, tun kafin ta shiryashi yaketa son ya fita, tana saka mishi kaya kam yabar ɗakin,
   Ta ɗauka ɗakin Momie ya tafi, ta shareshi tayi kwanciyarta har barci ya fara ɗaukarta ta jiyo muryar Momie tana tambayarta "Ina Abdallah" da ta ɗauka cikin barci ne, sai kuma ta tashi firgigit,
   "Momie ba wurinku yaje ba?"
   "A'ah tunda ya biyoki rabona dashi" ba shiri Majeeda ta sauko daga kan gadon,
   "ni wannan hegen yawon na Abdallah, yanzu haka yana can yana ɓarna"
   "Aikam k'ara ki nemoshi, don yau yaimun ɓarna kujera zanyi dashi"  tana dariya ta zira hijabinta,
   "Momie ana zauna mai gida?"
  "ni bani miji da wannan maɓarnacin, na barma Umma dai" dariya kawai tayi ta wuce, kullum cikin bata dariya suke, Momie da Abdallah,

Gidan ta shiga zagayewa, lunguna da sak'o da duk inda take tunanin Abdallah babushi, duk faɗin gidan babu inda bata duba ba, harta fito tsakar gida, inda ake ajje motoci ma taa dudduba babu shi, ta k'arasa tana tambayar mai gadi ko yaa ganshi,
   "wallahi hajia da yake na zagaya bayan gida ban lura ba koya fice, kuma saina manta da gidan a buɗe, duk an duba gidan bainan?" bata tsaya bashi amsa ba ta saka k'afa zata fice, kuma saita tuna bata da nik'ab ɗin, da gudu-gudu, sauri-sauri ta koma ciki sannan ta ɗauko ta dawo,
   Momie cikin tashin hankali take tambayarta,
   "Momie ban ganshi ba bari in duba cikin unguwa"

Abinka da unguwarda babu mutane, yaransu ma basu cika fita ba, sai en tsararun mutanen data gani take tambaya, anma kowa amsar ɗaya ce bai ganshi ba, tsananin tashin hankali harta fara hawaye ta cikin nik'abinta,
  Harta yanke shawarar komawa gida ta fasa, tasha kwanar layin bayansu, tana shiga ta hangoshi hannun wani handsome zaune saman bayan mota yana mishi wasa, sai dariya yake abinshi,
   Saida ta saukar da ajiyar zuciya, sannan ta k'arasa inda suke,
   "Ina wuni" ta gaishe dashi, cikin rashin fahimta yake dudduba kusa dashi, sannan ya dawo da kallonshi gareta ya tsura mata ido cikin nik'abin data rufe fuska dashi, yana son garin fuskar mamallakiyar zazzak'ar muryarnan, shikau Abdallah sai wasanshi yake a jikinshi,
    "Yaron dake hannunka nawa ne, ya fito daga gida" majeeda ta faɗa cikin k'osawa da kallon da yake mata,
  "ta yaya zan gane ba satarshi zaki ba, kina cikin wannan bak'in Abun"
   "na maka kama da mai sata ne? K'ila dai kaike shirin hakan" ta mik'a hannu zata ɗaukoshi aiko ya k'ara mak'alk'ale mutumin,
   "Abdallah" ta k'wala mishi kira cikin ɓacin rai,
  "Ayam" ya amsa da gwarancinshi,
   "Zo muje gida Momie na kira"
  "um-um, uncle" ya faɗa yana k'ara rik'e mutumin, takai hannu zata ɗaukeshi da tsiya, ya rirrik'eshi gashi bataso ta haɗa jiki dashi,
   "Don Allah ka bani yarona in tafi"
   "kingama tsoranki yake, alamar bai sanki ba, ki buɗe fuskarki idan da gaske kin sanshi" ganin tana k'ara ɓata ma kanta lokaci ya sanyata ɗaga nik'ab din, tsaida komi yayi ya tsaya yana kallonta, duk yanda yake hasaso kyawunta a zuciyarshi ta wuce nan,
   Abdallah na haɗa ido da ita ya k'ara lafewa jikin mutumin yana daria,
   "Auntieee, wannan ne"
"wannan ne me? Kazo muje nace" ta jawoshi ya koma da baya yana dariya,
   "Don Allah malam ni Matar aure ce ka bani yarona in tafi"
   "Ni naa tambayeki ne? Ai gashinan saiku tafi, nima da kika ganninan mijin aure ne, kawai yaronne bani da, kuma ina matuk'ar son yara da saurin shak'uwa dasu"
   "nima duk ban tambayeka wannan ba" sai lokacin yayi dariya sosae harya fara bata haushi,
   "wai matar aure, don kuna kama dashi shine zai zama ɗanki? Matar aure ma kama ne da ita"
   "tunda kaa gane ina kama dashi, kasan ba satar shi zanba kenan? Ka saukeminshi in ɗauka" ya sauko daga samar motar ya saukeshi anma yaqi sauka,
   "gashinan masu ɗa"
Yaro fa yak'i sauka, sai daria yake yana rik'eshi,
   "ban juwa, didan"
  Duk yanda taso anma yak'i yarda da ita

©Rabiatu sk msh

Friday, 6 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 59-60

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  59-60

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

A gurguje..

Bayan shekara ɗaya
Abubuwa da yawa sun faru cikin, ɓangaren Majeeda ta gama makarantarta, hankalinta kwance ta fara mantawa da Majeed duk da abu mai wahala ne ta iya cire tunaninshi a ranta, anma tana k'ok'arin hakan,
      Abdallah yayi wayau, yana ɗan jagwalgwala magana, babu inda bai zuwa yawo koda gudu ne, kakanninshi kowanne ɓangare ji suke dashi, duk da ba'a yayeshi ba anma kusan kullum a gidansu Umma yake yini, ba k'aramin tausayin yaron sukeji ba, Aunty zainabu ma ta haifi ɗanta namiji, Abdul k'adir,

***
Anata shirye-shiryen bikin Majeed da Aisha, anyi hidima sosae duk da angon ba wani nutsuwa gareshi ba, mahaifinta ne ma ya matsa akayi saboda yanda ta guji auren kowa ita dai sai Majeed kullum tana gidansu, duk yanda Majeeda taso ta danne zuciyarta ta halarci bikin kasawa tayi, sai dai ta kulle kanta a ɗaki tayi ta kuka,
   An ɗaura aure, can kaduna state aka kai mishi amaryar don yanaso yayi nesa da gida,

   Dare yayi Amarya na can bedroom ansha lulluɓi ana jiran ango, kamar daren farkonshi da Majeeda shi kaɗai ya shigo da ledar kaji da drinks a hannu, ya tura k'ofar ɗakin zai shiga,
    Daren farkonshi da Majeeda ya faɗo mishi, yanda suka dinga faɗa kamar sun cinye junansu, baisan sanda ya saki laidar ba ya dawo da baya, kujera ya samu a falo ya zauna yana sharar hawaye, ba kaɗan ba yake kewar Majeeda,
     Shiru-shiru Aisha ba ango,  tun tana tunanin yana hanya ya kusan zuwa harta daina ta fara tunanin abinda ya tsaidashi,
   Har k'arfe ɗaya babu Ango, hankalinta fa ya tashi ta fara tunanin ko ina ya shige, shawarar kiranshi a wayane tazo mata, ta ɗauko wayarta ta kirashi, can falo ta dinga jiyo ringing ɗin wayar anma ba'a ɗauka ba, haka ta dinga kira tana katsewa, ta fara tsorata, cikin sadaukarwa ta lallaɓa ta fito falon,

Can ta hangoshi saman kujera yayi tagumi da alama tunani yake, ta daurema zuciyarta ta k'arasa inda yake, sai da ta ɗan taɓoshi sannan yasan da zuwanta,
      "Majeeda ko?" ta tambayeshi tana kallonshi da raunanniyar murya,
    "bazan miki k'arya ba Aisha, naa kasa mantawa da Majeeda, wlhy komai nake ita nake tunawa" cikin sigar lallashi tace,
    "ba abune mai sauk'i haka ba hniee, anma insha Allah nayi maka alk'awarin maye maka gurbinta, zan zame maka mace ta gari, zan maka dun abinda zai faranta maka in guji wanda zai ɓata maka, zan nuna maka soyayya fiye da wacce kake tsammani, ina sonka da yawa hniee"
   "ngde Aisha, kiyi hak'uri kinji, insha Allah zanyi k'ok'arin daina tunaninta"
    "ba komai fa hniee, taso muje ka kwanta, tunanin ya isa haka," haka taci gaba da lallashinshi da kalamai masu daɗi har sai da ta tabbatar hankalinshi ya kwanta,

   A daren ranar Majeeda tayi kukanda bata taɓayi ba tunda tazo duniya, yanzu ne ta k'ara tabbatar ma kanta da taa rasa Majeed, daman Momie ta faɗa mata namiji ba'asha mishi alwashi, shknan har yayi aurenshi,
   Ga wani ciwon kai daya matsa mata ko barcin ta kasa, ita kaɗai a ɗaki Abdallah na wurin momie yayi barci tace a barshi tunda ba tashi yake ba, sai faman shafa confo take a kai,
    Abubuwa sun mata yawa kamar ita kaɗai damuwa ta k'are mawa, ga faɗan Abba kullum maganarshi ta fiddo miji tayi aure, kamar tana zaune a saman kansu,
   Tohh ita wama zata aura? Ita da ba fita take ba ballantana wani yace yana sonta, inma fitar dole ta kama mata da dogon hijabinta da nik'ab take tafiya, ta saɓa Abdallah a kafaɗa kamar matar aure, dole aji shakkar mata magana,
   Yanzu haka sauran sati ɗaya lokacin da daddy ya bata ya cika, koya aura mata duk wanda yaga dama, ta riga ta hak'ura da koma wanene, tunda ta rasa Majeed bata da wani sauran zaɓi,

©Rabiatu sk msh

Thursday, 5 January 2017

HARAMTACCEN ZAMA 57-58

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  57-58

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

```It is sad when the person who gave you the best memories become a memory.```

www.babymsh.blogspot.com

    Har sukaje gida Majeeda kuka take, babu wanda yayi k'ok'arin rarrashinta, kamar ranta zai fita haka take wannan kuka,
      Suna zuwa Aunty ta rakata tsohon ɗakinta, kayanta komi sunanan, ta kwance mata goyon Abdallah ta ajjeshi sannan ta juya ta barta nan,
  Jawoshi tayi ta ɗaura saman jinyarta ta tsura mishi ido, kowanne hali babanshi yake ciki? Shikenan fa kamar k'iftawar ido komai ya gama faruwa, rungumeshi tayi a jikinta taci gaban da kuka,

Bayan kwana biyu,
Majeeda babuci, babusha, saita kama dole, tayi wata uwar rama tayi bak'i sosae, kullum cikin kuka take, daga Momie har daddy babu wanda ya kula da halin da take ciki, Abdallah kanshi yayi ramar dole saboda bai samun isasshen abinci, sai dai da madara ake kaɗa mishi,
   Kullum cikin kiran layin Majeed take bai shiga, babbar damuwarta kenan da batasan halin da yake ciki ba, rayuwar gaba ɗaya taa burkice mata da babu Majeed a tare da ita,
    Sai a kwana na Uku ne Momie ta fara gajia da halin da take ciki, tunda ta shiga ɗakin bata fito ba, abinci yanda aka kai mata haka za'a ɗaukeshi, ruwa kawai take ɗura ma cikinta,

Tana kwance ta saka waya a gabanta tana kuka, bayan ta gama kiran layin Majeed,
   Momie tace "tashi Zaune" babu gardama ta mik'e zaune tana share hawaye, momie ta jawo kwanon Abinci ta ajje mata gabanta,
   "banson gardama, ki maza ki cinye abincinnan idan baso kike muci gaba da sanya miki ido ba" kuka ta fashe dashi sosai ta faɗa jikin momie,
    "Don Allah momie kuyi hak'uri"
   "naji tashi kici abinci nace" ta tallabota, sai da ta tabbatar taci mai yawa sannan ta k'yaleta bayan tasha ruwa, da kanta ta fita da kwanonin sannan ta dawo zauna tana fuskantar Majeeda,

    "Damuwar me kike?" tayi shiru ta kasa ɗago kanta, momie ta zare wayarta dake sak'ale a hannunta,
   "bamu isa mu rabaki dashi ba Majeeda? Yanzu kiran menene kike mishi?" shiru ba amsa,
   "ke ba k'aramar yarinya ba da basai an zauna ana miki faɗa ba, yanzu duk bayan wannan neman wata alak'a kike a tsakaninku? Ki zauna kiyi tunani kanki ne kike cuta, kece mace, daga inda ya samu wata macen zai manta dake, kekau kina nan kullum kina cutar zuciyarki da tunaninshi, kiyi tunani idan har yana sonki me yasa ya sakeki? Da yake kanki rashin hankali ya k'are kika zauna kikaci gaba da zama dashi, kullum kuna cikin saɓon ubangiji, kuna tara ma kanku zunubai, me zakuce da ɗanku idan ya girma ya gano ta hanyar da kuka sameshi? Ki godema Allah da abun ya tsaya a haka, damarkice da zaki zauna kita rok'ar yafiyar ubangiji, ki manta da Majeed da rayuwar da kukayi a baya,"

   "Momie wallahi na kasa ne, kullum ina k'ok'arin mantawa dashi, don Allah ki tayani da Addu'ah"
   "ki k'ara dagewa kam, don babu wani sauran zama a tsakaninku, babu inda kika taɓajin anyi saki Uku an koma, kema kina tashi kina addu'ah Allah ya yafe miki, ya kuma yaye miki sonshi, namiji ne da ba'asha mishi alwashi, duk yanda yakai da sonki wata rana shida kanshi zai goranta miki,......" nasiha dai sosae Momie ta shiga yi mata, gaba ɗata jikinta yayi sanyi, har momie ta barta tana zubar da hawaye,
   "Taya zan fara koyama kaina rayuwa babu Majeed?"

Majeed,
Shima tun daga ranar duk wani farin ciki ya k'aurace mishi, yana raye anma yafi kama da matacce, ko kukan ya kasa yi, idan ya fara kallon wuri ɗaya sai ya daɗe a haka, ko magana baiyi, tunsu Umma na ganin abun wasa harya fara damunsu, ada Zahra ce kawai ke kula dashi,
   Umma har sanyashi gaba take taita kukan kodai ya haukacene, gashinan dai har asibiti anje babu wani ci gaba, ko abinci aka ɗura sai anbi da ruwa zai haɗe,
  
Wata rana Zahra taje take bamasu Momie labarin halin da yake ciki, sai a sannanne majeeda na laɓe ta jiyo, taci kukanta harta gode ma Allah,
   Abdallah ne ta goya ta tafi dashi su Umma nata jajenshi, daga can ɗaki ya dinga jiyo kukanshi, takenan duk abubuwan da suka faru suka dunga dawo mishi, baisan sanda ya k'walla k'ara ba, sai a sannanne yayita kuka,
   Wani lokacinshi kanshi kukan yana maganin damuwa, sukaita murna jin ya dawo hankalinshi,

Aisha tana yawan zuwa ganinshi, duk da ba wata fira ke shiga tsakaninsu ba, anma tana k'ok'arin debe mishi kewa

A gurguje plz

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 55-56

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  55-56

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   "Aunty dgsk sabon gidan zaki kaini?"
   "da gaske mana, idan ba can ba ina zan kaiki?" shiru tayi sannan hankalinta ya fara kwanciya,
    "da tunanin me kikeyi?"
"ba komi Aunty, mu tafi" tana maida mata murmushinta, suka fito suka tafi, sai jan Aunty take da labari don ta tabbatar ba haushinta takeji ba, ita kuma taci gaba da biye mata,
   Bata ankara ba ta gansu hanyar gidansu Majeed, ta ɗago fuskarta cikin wani hargitsin tana kallon Aunty, tun kafin ta mata magana ta rigata,
    "Zamu biya ki musu ban kwana ne" sannan ta saki ranta, hankalinta kwance suka shiga gidan, kai tsaye ɗakin Abba suka wuce

   Kowah ya haɗu a ɗakin kamar ana wani taro, Daddynta da Momie, Umman Majeed da Abbanshi, harda Zahra ma, Majeed ta hango shima zaune, anma bata ga alaman damuwa a fuskarshi ba don shima ba'a mishi maganar ba, kuma bai taɓa kawowa a ranshi zasu san da maganar ba,
   Ganin haka itama bata damu da ganinsu ba, don bataga alamar Aunty taji maganar da tayi ba, suka samu wuri saman carpet ita da Aunty suka zauna, suna satar kallo ita da Majeed,

   Abban Majeed ne ya fara magana "bamu zauna nan don ku mana k'arya ba, ko mu saurari wani shirme naku, kun riga da kun gama kaimu k'arshe, ku faɗa mana tsakaninku da Allah wanne irin zama kuke tsakaninku"
  Ba wani shakku a ran Majeed yace "irin zaman da kukeso muyi Abba, mun daina faɗa, ina bata duk wani hakk'inta na aure, ka tambayeta kaji" tun kafin a tambayeta ta amshe
   "sosae ma kuwa Abba, yana kulawa dani, muna zaman mu lafiya"

Daddy ya jefa musu da tambayar da duk saida ta kusan katse musu en hanji,
   "Bayan kun raba auren naku kenan?" duk suka fara muzurai irinna mararsa gaskiya, dak'yar Majeed ya iya k'arfin hali,
     "Raba Aure kuma daddy kamar wasu mararsa hankali, mema zaija mana raba aure?"
   "Wa kake tambaya cikinmu?" inji Abba,
    "daman ina hankalin yake? Ban taɓa tunanin zaku iya aikata hakan ba, kun munafunce mu, kuma kun cuci kanku..." Majeed da har yanzu baisan yanda akai ba, yayi saurin cewa
   "Abba mufa ba abinda muka aikata, idan ma wani ne yakeso ya haɗamu daku wallahi sharri ne"
    "waye zai muku sharrin cikinmu? Koda yake, daman kun daɗe da maidamu shashashai tunda har kuke tunanin bazamu gano zaman da kuke ba" Abba ya mik'a hannu ya ansa wayar Aunty Zainabu data ɗauka kusa dasu, ta kunno recordn ɗin maganar Majeeda da hafsa yanda kowa zaiji,

   Majeeda kamar ta zunduma da gudu, tama kasa zama kamar wacce zafi ya kama, hawaye ne kawai ke kwararo mata ta ko ina, tunda take bata taɓa shiga tashin hankali haka a rayuwarta ba, tama kasa ɗaga kai ta kalli kowa, Majeed ma tunda ya ɗukar da kanshi bai k'ara ɗagowa ba, zufa kam rigarshi harta jik'e,
   Ɗakin yayi shiru, sai sautin kukan Majeeda dake fita a hankali,
   "Shima wannan ɗin sharri ne?" Abba ya tambayesu,
  "Anma na rantse Abba babu abinda ya shiga tsakanina dashi..."
  Wani irin k'wallo Daddy yayi da ita,
    “shi cikin Abdallahn a ruwa kikasha cikinshi? Ko har yawon iskanci kike fita?" tai saurin rik'e bakinta, tana dafe inda daddy ya sa mata k'afa saboda zafin da yake mata, idanunshi sunyi jajir da ɓacin rai,
   Sai lokacin takai kallonta ga Momie, ta duk'arda fuskarta tana share hawaye da alama kuka take, wannan wane irin tashin hankali ne yau take gani?

   Abban Majeed ma cikin rawar murya da alama dauriya yace,
   "kun cucemu, kun karya duk yarda da mukai daku, Alk'awari ne mukai ma mahaifinmu, Anma a sanadiyyarku mun kasa cikawa, Allah ya gani munyi iyakar k'ok'arinmu, anma kun nuna mana baku isa ba, HARAMTACCEN ZAMA?, bansan a ina kuka samo wannan tarbiyyar ba, kuma kunyi kaɗan kuce mune muka baku ita, me kukeso jama'a suce a kanmu? Mun muku auren dolene kuka maida kanku haka? Wlhy k'arya kuke duniya ta zagemu a kanku, bazamu taɓa yafe muku...."
   Umma tace "duk meya kawo hakan Alhaji? Yanzu kuma inka musu baki ya kakeso su zama?"
    "harna yaushe kuma? ZAMAN DADIRO fa, wallahi zaifimin daɗi ace mutuwa sukai da inga wannan rana" duk k'arfin halin da Abba yake  da kuka ya k'arasa maganar,
   Can ciki Majeed shima Yace "Ayi hak'uri Abba, kuskure...." wani irin Mazga da Abba yakai  mishi a baki har saida yayi jini, cikin tashin hankali ya buɗe bakin sai gashi har hak'ori ya fita,

   Hakan baisa Abba ya saurara mishi ba, saima ya tashi ya rufeshi da duka ta ko ina, daddy na rik'eshi anma kamar yana k'ara mishi k'arfi, shiko Majeed ko motsawa baiyi ba, yana zaune yanda yake Abba na jibgarshi, dak'yar daddy ya k'waceshi ya matsa sai huci yake,
    "ka k'yaleni in kasheshi in huta da wannan bak'in cikin nashi, ai duk laifinshine, shine babba kuma sakaran banza, inama amfanin haihuwarshi?"
   "A'ah Yaya, idan har akwai laifinshi tohh nata yafi yawa"
      "laifinta data buɗa baki ta sakeshi? Idan har ya daraja maganarmu bai saketa ba zata saki kanta ne? Ko zata ma kanta ciki ne? Shine lalataccen ɗan iskan da yayi sanadin komi, ita tana da raunanniyar zuciya, da kalamai en kaɗan zai iya galaba a kanta" yana gama faɗi ya shige bedroom ɗinshi,  Umma ta tashi ta bishi,

  Haka su Daddy suma suka fita, Aunty Zainabu taja Hannun Majeeda suka tafi anan kowa ya watse akabar Majeed kamar wani zararre,
   Saida Zahra ta dawo ta mishi magana sannan ya mik'e ya tafi yana tangaɗi ko kallon gabanshi baiyi harya shige ɗakinshi

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 55-56

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  55-56

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   "Aunty dgsk sabon gidan zaki kaini?"
   "da gaske mana, idan ba can ba ina zan kaiki?" shiru tayi sannan hankalinta ya fara kwanciya,
    "da tunanin me kikeyi?"
"ba komi Aunty, mu tafi" tana maida mata murmushinta, suka fito suka tafi, sai jan Aunty take da labari don ta tabbatar ba haushinta takeji ba, ita kuma taci gaba da biye mata,
   Bata ankara ba ta gansu hanyar gidansu Majeed, ta ɗago fuskarta cikin wani hargitsin tana kallon Aunty, tun kafin ta mata magana ta rigata,
    "Zamu biya ki musu ban kwana ne" sannan ta saki ranta, hankalinta kwance suka shiga gidan, kai tsaye ɗakin Abba suka wuce

   Kowah ya haɗu a ɗakin kamar ana wani taro, Daddynta da Momie, Umman Majeed da Abbanshi, harda Zahra ma, Majeed ta hango shima zaune, anma bata ga alaman damuwa a fuskarshi ba don shima ba'a mishi maganar ba, kuma bai taɓa kawowa a ranshi zasu san da maganar ba,
   Ganin haka itama bata damu da ganinsu ba, don bataga alamar Aunty taji maganar da tayi ba, suka samu wuri saman carpet ita da Aunty suka zauna, suna satar kallo ita da Majeed,

   Abban Majeed ne ya fara magana "bamu zauna nan don ku mana k'arya ba, ko mu saurari wani shirme naku, kun riga da kun gama kaimu k'arshe, ku faɗa mana tsakaninku da Allah wanne irin zama kuke tsakaninku"
  Ba wani shakku a ran Majeed yace "irin zaman da kukeso muyi Abba, mun daina faɗa, ina bata duk wani hakk'inta na aure, ka tambayeta kaji" tun kafin a tambayeta ta amshe
   "sosae ma kuwa Abba, yana kulawa dani, muna zaman mu lafiya"

Daddy ya jefa musu da tambayar da duk saida ta kusan katse musu en hanji,
   "Bayan kun raba auren naku kenan?" duk suka fara muzurai irinna mararsa gaskiya, dak'yar Majeed ya iya k'arfin hali,
     "Raba Aure kuma daddy kamar wasu mararsa hankali, mema zaija mana raba aure?"
   "Wa kake tambaya cikinmu?" inji Abba,
    "daman ina hankalin yake? Ban taɓa tunanin zaku iya aikata hakan ba, kun munafunce mu, kuma kun cuci kanku..." Majeed da har yanzu baisan yanda akai ba, yayi saurin cewa
   "Abba mufa ba abinda muka aikata, idan ma wani ne yakeso ya haɗamu daku wallahi sharri ne"
    "waye zai muku sharrin cikinmu? Koda yake, daman kun daɗe da maidamu shashashai tunda har kuke tunanin bazamu gano zaman da kuke ba" Abba ya mik'a hannu ya ansa wayar Aunty Zainabu data ɗauka kusa dasu, ta kunno recordn ɗin maganar Majeeda da hafsa yanda kowa zaiji,

   Majeeda kamar ta zunduma da gudu, tama kasa zama kamar wacce zafi ya kama, hawaye ne kawai ke kwararo mata ta ko ina, tunda take bata taɓa shiga tashin hankali haka a rayuwarta ba, tama kasa ɗaga kai ta kalli kowa, Majeed ma tunda ya ɗukar da kanshi bai k'ara ɗagowa ba, zufa kam rigarshi harta jik'e,
   Ɗakin yayi shiru, sai sautin kukan Majeeda dake fita a hankali,
   "Shima wannan ɗin sharri ne?" Abba ya tambayesu,
  "Anma na rantse Abba babu abinda ya shiga tsakanina dashi..."
  Wani irin k'wallo Daddy yayi da ita,
    “shi cikin Abdallahn a ruwa kikasha cikinshi? Ko har yawon iskanci kike fita?" tai saurin rik'e bakinta, tana dafe inda daddy ya sa mata k'afa saboda zafin da yake mata, idanunshi sunyi jajir da ɓacin rai,
   Sai lokacin takai kallonta ga Momie, ta duk'arda fuskarta tana share hawaye da alama kuka take, wannan wane irin tashin hankali ne yau take gani?

   Abban Majeed ma cikin rawar murya da alama dauriya yace,
   "kun cucemu, kun karya duk yarda da mukai daku, Alk'awari ne mukai ma mahaifinmu, Anma a sanadiyyarku mun kasa cikawa, Allah ya gani munyi iyakar k'ok'arinmu, anma kun nuna mana baku isa ba, HARAMTACCEN ZAMA?, bansan a ina kuka samo wannan tarbiyyar ba, kuma kunyi kaɗan kuce mune muka baku ita, me kukeso jama'a suce a kanmu? Mun muku auren dolene kuka maida kanku haka? Wlhy k'arya kuke duniya ta zagemu a kanku, bazamu taɓa yafe muku...."
   Umma tace "duk meya kawo hakan Alhaji? Yanzu kuma inka musu baki ya kakeso su zama?"
    "harna yaushe kuma? ZAMAN DADIRO fa, wallahi zaifimin daɗi ace mutuwa sukai da inga wannan rana" duk k'arfin halin da Abba yake  da kuka ya k'arasa maganar,
   Can ciki Majeed shima Yace "Ayi hak'uri Abba, kuskure...." wani irin Mazga da Abba yakai  mishi a baki har saida yayi jini, cikin tashin hankali ya buɗe bakin sai gashi har hak'ori ya fita,

   Hakan baisa Abba ya saurara mishi ba, saima ya tashi ya rufeshi da duka ta ko ina, daddy na rik'eshi anma kamar yana k'ara mishi k'arfi, shiko Majeed ko motsawa baiyi ba, yana zaune yanda yake Abba na jibgarshi, dak'yar daddy ya k'waceshi ya matsa sai huci yake,
    "ka k'yaleni in kasheshi in huta da wannan bak'in cikin nashi, ai duk laifinshine, shine babba kuma sakaran banza, inama amfanin haihuwarshi?"
   "A'ah Yaya, idan har akwai laifinshi tohh nata yafi yawa"
      "laifinta data buɗa baki ta sakeshi? Idan har ya daraja maganarmu bai saketa ba zata saki kanta ne? Ko zata ma kanta ciki ne? Shine lalataccen ɗan iskan da yayi sanadin komi, ita tana da raunanniyar zuciya, da kalamai en kaɗan zai iya galaba a kanta" yana gama faɗi ya shige bedroom ɗinshi,  Umma ta tashi ta bishi,

  Haka su Daddy suma suka fita, Aunty Zainabu taja Hannun Majeeda suka tafi anan kowa ya watse akabar Majeed kamar wani zararre,
   Saida Zahra ta dawo ta mishi magana sannan ya mik'e ya tafi yana tangaɗi ko kallon gabanshi baiyi harya shige ɗakinshi

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 53-54

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  53-54

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

   Wani wahalallen miyau ne ta haɗe da k'yar, tayi tsuru-tsuru da ita kamar wadda aka dasa, buɗe baki tayi zatai magana ta kasa ta bar bakin buɗe tana kallon Aunty Zainabu,
   Jikinta bai tashi kyarma ba saida Aunty Zainabu ta doso inda suke, tana tafiya tana kallonsu fuskarta babu annuri, bata ankara ba sai dai taji ta fara jik'ewa da zufa ta ko ina,
   "Aunty wallahi zan miki bayani, don Allah ki dakata, abinda kikaji ba haka bane"
   Bata tankata ba harta k'araso inda take,  tuni taa gama sandarewa, sai dai taga ta duk'a inda take, ta ɗaga filo ta zaro wayarta, sannan ta juya tabar ɗakin, ba tare data tanka musu ba

   Wata munafukar ajiyar zuciyah ta saki sannan ta juyo inda hafsatul kiram take itama duk taa haɗa zufa, tama fita ruɗewa, (wanda suka karanta littafin hafsatul kiram sun santa da saurin ruɗewa, abu kaɗan ke sakata kuka), tuni hawaye suka wanke mata fuska, harta so ba Majeeda dariya,
     "Akwai matsala fa" inji Majeeda,
   "Matsalan me kina ga batace komi ba, da alama bataji mu ba"
   "Zanyi fatan hakan hafsat, anma nifa hankalina bai kwanta ba da irin kallon da take mana" duk sukai shiru kowa ya rasa abun cewa,

  Sun daɗe a haka babu wanda ya iya cewa komi, k'arar shigowar text ne ya katsesu a wayar Majeeda, duk saida suka firgita, sannan ta daure ta duba, kamar wata marar lafiya,
     "I don't say it enough, but wanted to let you know that I love you."
   "luv uh too i swear, ina ka shige?"
    "cikin zuciyarki...lol ina hanya hope kowa dai ya gama tafiya, ina kewar matata da yawa"
   Ta sauke ajiyar zuciyah, addu'ah ta shiga yi Allah ya kawoshi gidan da wuri, tare da Addu'an Allah yasa Aunty Zainabu bataji su ba.

   Firarma kasawa sukai ita da hafsat, da gudu ta tafi toilet ta zazzagar da fitsarin data kusan saki shigowar Aunty, tana dawowa ta zari jikkarta,
   "Tohh Aminiyah, nidai zan tafi"
   ta tashi da sauri tana gyara ɗaurin zane, "ina kuma zaki tafi ki barni cikin wannan bala'i?"
    "Haba, ki kwantar da hankalinki mana komai zai dai-daita insha Allah, zamuyi waya Ya Umar yana waje"
   "kema fa hankalinki tashe yake taya zan kwantar da nawa?" dafa kafaɗarta hafsat tayi, suka fito tana kwantar mata da hankali,

   Sai dai me? Falonta wayam babu furnitures nata, komai an kwashe kamar sabon gini, duk suka saki baki suna kallo har Aunty Zainabu tazo ta bangajesu ta wuce bedroom ɗin nata tana sauri,
    Kayan sawarta ta dinga kwashesa tana juye mata a akwatunanta, hafsat na ganin haka ta mata sallama ta tafi, bata samu maa ta amsa mata ba,
    Tafiya tayi da sauri inda Aunty take ta rik'e mata hannu,
    "Aunty ina za'a kaimin kayan kike kwasarsu?"
Bata tankata ba taci gaba da kwashewa, sai da ta gama kwashe komai, ko k'yalle bata bari ba ta jasu tayi waje dasu, Majeeda ta k'ara shan gabanta,
    "Aunty don Allah ki faɗamun ina zaki kaimun kaya?" k'ara shareta tayi taci gaba da jan kayan,
   Duk ta ruɗe kuka kawai take kamar wacce ake zare ma rai, ta kwanta nan k'asa kamar k'aramar yarinya tana gunjin kuka,
     "Don Allah ki rufamun Asiri Aunty yanda naki ya rufu, ki taimakeni karku rabani da Yaya Majeed, shine rayuwatah, don Allah Aunty ki tausayamun" idan Aunty Zainabu ta tankata ku da kuke karatunnan kun tanka, haka taci gaba da kuka har muryarta ta soma sik'ewa,

  Tana ji tana gani suka kwashe komai na ɓangarenta,  harta Abdallah goyeshi tayi a bayanta, ta wurga mata mayafi,
    "ki tashi mu tafi nace"
Da tafiyar gwiwa ta gangaro inda Aunty take ta rik'e k'afafunta,
   "ki kasheni ma kawai Aunty, zaifimun sauk'i da rayuwa babushi, don Allah karki Rabani da Yaya Majeed Aunty, ina sonshi" ta k'ara fashewa da kuka hannuwanta rik'e da k'afafun Aunty Zainabu,

   Ji tayi Aunty ta k'yalk'yale da daria,
   "lallai Majeeda bansan sanda soyayya ta rufe miki ido ba haka, ranar da za'a kawoki kin cika ma mutane kunne, 'don Allah karku kaini, bazan iya rayuwa dashi ba,' yau kuma kece da cewa bazaki iya rayuwah babushi ba, Sabon gidan da Dadd ya baku zaku koma, ko wani kike ba ajiyar kuɗin da za'a sake miki wasu kayan?"
   Wata doguwar ajiyar zuciyah ta saki tana jan numfashi, ta ɗago kanta tana kallon Aunty cikin shakkun maganar data faɗa, murmushi taga tana mata,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 51-52

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  51-52

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

Ranar suna yaro yaci suna Abdallah, ba k'aramin shagali akai ba a wannan rana, gida yaa cika da mutane, Anyi abinciccika kala-kala, nama ko ko shi kaɗai kakeso sai kaci ka k'oshi, ga gassasun kaji da soyayyun ma,
    Kayan barka ma Majeeda ta samesu harta rasa wurin ajjewa, banda kudaɗen data samu, gida cike da jama'a babu masaka tsinke, muryarta harta soma shak'ewa saboda hidima da jama'a,

    Tana cikin canja kaya text ɗin Majeed ya shigo mata,
    "Hey babe, i cant stop thinking about uh koma me nake ke nake gani, ina kewarki plz bzan ganki ba?" sai da ta ɗanyi murmushi sannan ta maida mishi,
    "miss uh more dear, hidimar jama'a sai a hankali, zaima zama abun magana idan nace zanzo"
   "plz babe, kwalliyan kawai zan gani" sai da ta ɗauka lokaci sannan ta maida mishi amsa, saboda yanda mutane keta shigowa,
   "ka duba pics a whatsapp yanzu"
   "nidai ban yarda ba, ga frnds ɗina ma zaku gaisa, sunata so su ganki"
    "Wlhy babu damar barin ɗakinnan fa, muyi waya dasu mana?"
    "Shikenan bazaki zo ba"
   "M srry nawan"
   "owk ki samamin lokaci da dare plz"

    Bata mishi reply ba wata frnd ɗinta ta anshe wayar, suka ci gaba da fira, haka a gajiye ta k'are hidimar, bata samu zuwa ba sai dai suka sha waya da dare,
   Washe gari su Aunty Zainabu suka dawo gyara mata gida saboda yanda aka ɓata ko ina, tare da wasu mutanenta da Zahra suka shiga gyaran,
       Tana can cikin bedroom ɗinta ta fara jiyo magana kamar ta hafsatul kiram sama-sama, gabanta ne yayi mummunan faɗuwa, ta tashi a hankali take tafiya zata lek'a taga kowacece, sukai kociɓus da ita tana shirin shiga bedroom ɗin,
    Sai da taja ta baya kamar wacce taga Abun tsoro,
     "Amaryar jego"
   "ke kuma haka ake dawowa babu labari?"
    "daman ayna faɗa miki mamaki zan baki" ta k'arasa inda Abdallah yake kwance ta ɗaukeshi,
     "Masha Allah, wannan kyakkyawan babe"
    Ita dai Majeeda binta kawai take da murmushin yak'e ko zama ma taa kasa yi, hafsat ɗinma ganinta take kamar wata mutum daban,
    "Ki zauna mana, kinsan ina da tarin tambayoyi sosae a baki na" duk taa ruɗe take magana,
   "tambayoyi kuma? Ay kya bari dai kisha ko lemu ne"
   "Haba gidanki nazo fa, kamar dai wata bak'uwa"
   "saiki zama bak'uwar mana tunda zuwanki na farko ne, kedai bara na kawo miki"
     "nidai ki barshi ki zauna" bata saurareta ba ta nufi hanyar fita, tana mata magana anma saida ta fita,
   Zahra ta rok'a Alfarma, ta kai mata drinks ɗin, sannan ta samu wuri inda su Aunty Zainabu suke ta Zauna, don ganin hafsatul kiram take kamar wata surukarta,
   Saida ta aiko kiranta ba don taso ba ta tashi ta tafi,

   "kin ganmu nan aiki muke ta fama dashi"
   "Shine kuma zaki barni ni kaɗai zuru"
     "kizo mu tafi falon mana kamar wata bak'uwa" ta mike zata tafi, hafsatul kiram ta kamo hannunta ta zaunar da ita, kanta ta dafe daya fara sara mata,
    "Daga ganin yanda kike kauce-kaucennan ya tabbatarmun da baki da gaskia, plz majeeda karki tabbatarmun da zargin da nake miki na HARAMTACCEN ZAMA kuke da Majeed"
    "kinga wannan ba lokacin da zamuyi maganar nan bane,"
    "sai yaushe zamu yita? Ko kina nufin wani auren kikai kika fito sannan kuka maida aurenku?"
    "keni babu wani auren da nayi, daman can wasa nake miki babu wani raba auren da mukai da Majeed" ta faɗa kanta a k'asa,
     "da gaske kike?" hafsat ta tambayeta tanason haɗa ido da ita,
    "da gaske mana"
  "k'arya kike Majeeda, akwai yanayin da mutum zaiyi wasa da kuma yanayin da mutum zaiyi magana a gane gaske ne, yanda kukai aure da Majeed babu abinda bazaku iya yi ba"

   Kuka ta fashe dashi, don kalmomin da zata kare kanta sun k'are mata, Hafsatul kiram ce kawai tasan matsalarta, kuma itace rufin asirinta, tasan zata bata shawara mai kyau,
   "ina sonshi hafsa, ina matuk'ar sonshi, bansan ta yanda akai na fara sonshi ba, anma bazan iya rayuwah babushi ba, ke kaɗai kikasan sirrinmu, shiyasa muka yanke shawaran muci gaba da rayuwanmu a haka, koda mun faɗa a gida tsinuwa ne kawai, Bama zanso abinda zai rabani dashi ba" hafsatul kiram hannunta har kyarma yake,
   "kina nufin bayan ya miki saki Ukun kuke zaune a tare?"
   "eeh don Allah ki taimaki rayuwatah karki faɗa ma kowa, wlhy bazan iya rayuwa babushi ba" duk ta rikice mata, tana kuka tana rok'arta, sai rirrik'eta take,
     "plz hafsa kicemun bazaki faɗa ma kowa ba"
     "Abunda naketa faɗa miki kenan Majeeda, anma ko sauraratah bakiyi ba, Yanzu idan kuka mutu a haka me zakuce da Allah? A haka zaku zauna kuna tara yara? Wata k'ila ni kaɗai nasan sirrinku a yanzu, kuna tunanin harku mutu Allah bazai to na asirinki ba? Duk son da kuke yima junanku bai kamata kuyi irin wannan zaman ba, kiyi tunani wannan ba soyayyah bace da zaku kai kanku da halaka, in banda abunki....."
     "Plz hakanan nidai, naji shawaranki, nidai kicemun bazaki faɗa ma kowa ba"
    "Abinda ya dameki kenan? Naji bazan faɗa ba Majeeda, sirrinki da yafi wannan ma ni mai rik'e miki ce, wannan Alk'awari ne tsakaninmu"
    Cikin farin ciki Majeeda ta rungumeta tana murna,
    "Na gode sosae Aminiyatah"
     "babu godia tsakaninmu"
Sannan ta ɗago fuskarta tana ci gaba da murmushi,

   Cak, fara'ar fuskarta ta ɗauke kamar wacce aka faɗa ma sak'on mutuwa, jikinta yahau rawa, hango Aunty Zainabu da tayi tsaye a k'ofa ta tsura musu ido,

©Rabiatu sk msh

HARAMTACCEN ZAMA 49-50

💖HARAMTACCEN ZAMA💖
    ♠♠♠♠♠♠♠
                  49-50

©Rabiatu sk msh
         ®NWA

Labari...
        Ilileee

www.babymsh.blogspot.com

  Awa shidda tayi aka sallameta, Asibitin cike da family ɗinsu, haka suka cika motoci suka nufi gidan Majeeda da Majeed,
      Anan ma saida Umma taso ta tafi da ita gidanta tayi wankan Arba'in, anma Majeed yak'i amincewa, shida kanshi ma yayi driving don kar Umma tace dole sai an kaita can,

  Murna sosae su Abba sukai da jaririnnan kasancewarshi jikansu na farko, duk da a yanzuma aunty Zainabu na ɗauke da juna biyu,
   Kyautar tsantsararren gida Abba ya musu, zasu koma bayan suna,
      Kullum gidan cike da Mutane kamar a ranar ne suna, su Majeeda ba zama sai hidima da jama'a kullum Majeed cikin k'orafi yake bata bashi lokaci,

   Zahra takai mishi abinci yace ta turo mishi da Majeeda, fitowarta wanka kenan, saida ta ɓata lokaci wurin shiryawa, nanma dak'yar k'awayenta suka barta ta tafi, jaririn na kukata ɗaukeshi kawai suka tafi ɗakin babanshi,
    Tana shiga ya maida k'ofar ya kulle, da dubara ta ajje babyn, tun kafin tayi magana ya haɗa bakinshi da nata, sun daɗe a haka tun suna a tsaye har suka zauna gefen gado, kukan babyn ya saka suka tsagaita, ya zauna yana kallonsu ta saka mishi abincinshi a baki,
   "ko kewata bakiyi ko?"
  "Fiye da kaima Yaya Majeed"
     "ban yarda ba, tun haihuwar yaronnan kika daina kula dani, baki damu da cina ba, baki damu da kizo kiga yanda na tashi ba, idan bana kiraki a waya ba bazaki kirani ba"
   "ka yarda dani Yaya Majeed komai nake kana cikin Raina, ni kaina na k'agara a gama hidimarnan" ya mik'a hannu ya ansheshi bayan yaa gama sha,

    "Na kaasa koyon barci ba tare dake ba"
      "nima haka dear, yanzu ai na kwana biyu ne kawai"
   "Yayimin yawa fa,"
  "kaaci abinci?" kai ya girgiza mata, da sauri ta tafi ta zubo mishi, ta zauna ta bashi saida ta tabbatar ya k'oshi sannan ta k'yaleshi, taa daɗe har saida aka mata waya tayi bak'i sannan ta koma ɓangarenta,

   Tana ganinsu ta saki fara'a,
   "laah! Asiyah kardai ku cemun kune sai yau"
    "donma kin ganmu kenan, mu da ba'a faɗa nawa ba?"
   Fatima tace "ke kike maganarmu, yanda suke da hafsatul kiram ma ko ita bata faɗa mata ba" sai da gabanta ya faɗi da suka ambaci hafsatul kiram, na'urorin jikinta ne suka dakata da aiki na wani lokaci suna magana ma anma ko saurarensu ba tayi,
   Sai da Asiya ta taɓota, sannan ta dawo daga tunaninta duk ta rikice, ta fara murmushin yak'e,
   "Wa? hafsatul kiram? Kema kinsan bata k'asarne, kuma na rasa numberta tunda ta canja sim"
     "itama haka tace sanda na faɗa mata haihuwarki, halan tunda ta tafi bakuyi waya ba?" kai Majeeda ta ɗaga ma Fatima, sai kuma ta zaro ido da taji abinda tace,
    "kika faɗa mata na haihu, ya akai kika faɗa mata?" duk suka tsaya suna kallonta ganin yanda duk ta rikice lokaci ɗaya, Aunty Zainabu dake tattara wankin baby ta kalleta shek'ek'e,
    "miye don An faɗa mata?" ta k'ara washe hak'oran yak'e,
   "Ba komi Aunty kawai dai naso in bata mamaki ne"

   Fatima tace "kinga barama na mata waya ta fara miki k'orafin rashin kiranta tun yanzu" Majeeda sai k'ok'arin dai daita nutsuwarta take, ita tsakaninta da Allah ko tunawa da hafsat bata sonyi, tana cikin tunani Fatima ta mik'o mata wayar,
    "Aminiyatah!!" inji hafsat,
  "Na'am, Amaryar Umar shikenan an manta da mutane babu wani zumunci"
     "Haba! Ni zance miki haka, har ki sake aure bazaki sanarmin ba?"
  "Wai Aure? Ni ɗin?"
  "tohh daa wa?"
    "kinga besty zan kiraki, kinsan hidimar jama'a, yaushe zaki dawo?"
    "nan kusa, amma bazan faɗa miki ba nima, ki gaishemin da baby" a sanyaye tace "zaiji" sannan ta saki ajiyar zuciyah bayan ta kashe wayar,

   Basaina faɗa muku ba, kunsan nutsuwa taa k'are ma Majeeda a wannan rana, haka ta yini da tunani sosae, duk taa shiga damuwa,

©Rabiatu sk msh

Popular Posts

 
]]>All content on thisblog are copyright protected and cannot be reproduced on other websites without permission.