💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
13-14
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
Batayi wani barcin kirki ba saboda yanda ta k'agara gari ya waye, ga uban kukan da tasha da safe duk idanunta sun kunbura. Gari na gama haske ta shirya wurin 11 tace ma Momie taa tafi gidan Aunty Zainab, da yake tasan matsalanta da damuwanta kuma bata da wani abokin shawara kamar Aunty Zainab ɗin shiyasa momie bata hanata taje ta kwantar mata da hankali ba.
Napep ta tara ya kaita gidan Aunty Zainab, tana sauka daga napep ɗin yana fitowa da motarshi daga gidan, ta juyar da kanta gefe kamar bata ganshi ba, yayo kanta da mota kuwa har ya kusan take mata k'afa sannan ya fito daga motar.
Yana nunata da ɗan yatsa yace "ina fatan kinsan abinda ke faruwa, kuma baki amince musu ba" sai data gatsina sannan tace "kaima kasani ai bazan taɓa amince da auran ka ba"
"Yaa miki kyau, don wallahi aka aura min ke gutsun-gutsun ina iya miki in jefar dake, don ko kaɗan baki cikin kalar matan da nake so"
Tsoki kawai taja ta juya ta tafi don batason tsayawa magana dashi ma, wata tsanar shi ce ke k'ara zo mata ta shige gidan Aunty Zainab kawai.
Tun daga ranar kullum cikin damuwa suke, babu wanda bai kwanta rashin lafiya a cikinsu ba, k'iyayya sosai suke nuna ma junansu, anma iyayensu sukai watsi dasu sai dai hidimar biki kawai suke.
Duk yanda suka so a fasa auren sai da aka ɗaura shi su duka babu mai so, a tunaninsu iyayen idan akayi auren daga baya zasu warware ne suci gaba da son junansu, basu sanda babban kuskure ne suka tafka ba (inji rash kardam).
A gurguje dai😜
Mu koma labari....
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment