💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
31-32
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Duk wani ihu da take tana tuttureshi harda cizo da yakushi bai tsaya saurara mata ba, baimasan tanayi ba har saida ya fara jinshi dai dai sannan hankalinshi ya dawo jikinshi, kwantawa yayi gefenta yana maida numfashi kamar wanda yasha gudu.
Kasa koda motsi tayi, har lokacin hawaye take, maido nepa da akayi ne ya sakashi mik'ewa ya haɗa mata ruwa mai zafi a toilet, yazo inda take ya saka hannu zai ɗauketa ta buge hannu, yaja baya, "kinga karki k'arama kanki wahala idan kin shiga ruwan zafi zaki rage jin ciwon" dak'yar ya lallaɓata ya kaita toilet ɗin, sai harararshi take, shikam dariya yake abinshi saboda wani irin farin ciki da yakeji.
Cikin kwamin wankan ya direta, taga yak'i ya fita, "me kuma kakemin anan" ya shafi gemunshi "wankan da kika tambayeni kozan taimaka in tayaki, shine zan miki",
"Haba Yaya majeed, plz nidai ya isa haka, ka ficemin plz", "tohm saikin fito, ga wani ruwan nan a bocket wanda zaki wankan tsarki" "naji" kawai tace da taga alaman in batayi magana ba bazai fice ba, sannan ta maida kanta tana jin wani yanayi daban.
40mnts later
Ta fito tana tafiya dak'yar, har ya gyara shimfiɗar ya canja zanin gado, ta kwanta gefen gadon sannan ta juya mishi baya, mirginowa yayi inda take ya kwantar da kanshi saman kafaɗarta ta tureshi muryarta da alaman kuka take tace, "wai me kakeyi haka Yaya Majeed? Kasanfa abinda kakeyi haramun ne" ya ɗan rage fara'arshi, bayan ya kamo hannuta yana wasa dashi "me nayi da ba dai-dai ba? Ɗazun da kika k'udundune a jikina na hanaki ne?" ya kai mata cizo a yatsanta daya saka a baki ta saki k'ara, da sauri takai mishi bugu a k'irji, "bafa wasa ake ba Yaya Majeed" sai kuma ta fashe da kuka sosai.
"Ka cuceni yaya majeed, shikenan ka rabani da abinda nake tak'ama da, yanzu wanne namiji ne zai aureni a haka bayan kai kamin saki uku? Zina fa kenan muka aikata, da wanda bai sona kuma"
"Bayan NI DAKE, wa yasan zina muka aikata? Kin manta duk duniya tana mana kallon miji da mata ne? NI DAKE ne kawai mukasan babu aure a tsakaninmu"
"Zamuci gaba da zama a haka ne? Kasan dai duk daɗewa dolene zanje na auri wani" hannunta dake rik'e a nashi ya ɗaura a bakinshi,
"ki daina faɗar haka plz, karki rabu dani Majeeda, sai yanzu na gane sosai ina buk'atarki a rayuwatah, wannan sirrine tsakanin NI DAKE, kinsan dai idan har iyayenmu suka san halin da muke ciki tsinuwa ne kawai, kuma dole su rabamu" ya marairaice fuska, "banson na rasaki a rayuwatah"
Tunda ya fara magana take kallonshi kamar wani zararre, anya Yaya majeed yana cikin hankalinshi? Baki a buɗe tace "HARAMTACCEN ZAMA zamuyi kenan?"
"kada ki zurfafa tunaninki mana, ki manta kawai da yanzu babu aure a tsakaninmu, ki kalleni a matsayin mijinki, tunda babu wanda yasan sirrinmu, muma mu manta abinda ya faru", hafsatul kiram ce ta faɗo mata a rai, ita kaɗaice tasan sirrinta da majeed, tohh anma yanzu ai basu k'asar sun tafi moscow ita da umar ɗinta, kuma ta yarda da ita bazata taɓa faɗama wani sirrinta ba.
"nidai bazan iya HARAMTACCEN ZAMAn nan ba, kowa yaci gaba da harkarshi kawai tunda daman ba sona kake ba, kawai sha'awanah kake"
"Waye ya faɗa miki bana sonki?" yayi saurin katseta.
"bai kamata wannan maganar ta fito daga bakinki ba, ni kaina bansan sanda na fara sonki ba Majeeda, anma ki yarda dani ina sonki, tun lokacin dana kasa ɗauke idanuna daga kallon kyakkyawar fuskarki a wancan ranar, na tsinci kaina da matsananci tausayinki a lokacin da kika fara rashin lafiya, har nakejin daman ciwon ya dawo a jikina, wannan ba so bane? Duk inda zanje koda na fita daga gida tunanina yana a kanki ta yanda bazan iya ɗaukar lokaci ba sai nazo na ganki, a hakan ba sonki nake ba?, da meyasa bana sha'awar jikinki sai yanzu? Idan har banisonki bazan taɓa sha'awarki ba, bansan yaushene ba ko kuma tayaya na fara sonki, anma na rantse da wanda raina yake a hannunsa ina sonki fiye da yanda nake son kaina,"
"kafin yanzu ina buk'atar, abinci, ruwa da iska ne kawai don in rayu, anma yanzu rayuwatah tana matuk'ar buk'atarki majeeda"
Share hawayenta tayi cikin farin ciki ta kwantar da kwanta a k'irjinshi, "nima ina sonka sosai yaya majeed" ya saka hannu yana shafa gashin kanta shima cikin jin daɗi yace, "Kin yarda zamuci gaba da zaman aurenmu?" ta ɗaga mishi kai.
OMG😱 ZAMAN AURE KO DADIRO? mamakin kam bai barni naa ci gaba da rubutu ba har suka shige bargo suka barni hangame da baki😷
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment