💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
43-44
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Aunty na zaune bayan an shiga da Majeeda, Majeed kam sai zagaye wurin yake yaje ya dawo, har Aunty zainabu ta gaji tace mishi,
"wai bazaka zauna ba Majeed?"
"Aunty yazan zauna bayan ita tana can tana shan wahala"
"tohh ci gaba da zagayen ku raba wahalan"
Nurse ce ta fito,
"likita yace zaku iya shiga" tun kafin Aunty zainabu ta mik'e ya rigata shiga ɗakin, Abokinsa Mukhtar ne ya hango, ana ce mishi Dr. Shaheed, ya taho da fara'arshi yana bashi hannu,
"ka ce mana Amaryar da aka hanamu rakiyar ango don karmu ganota ne aka kawomin har inda nake"
Majeed yayi daria sosae "kasan dai yanda abun yake, anma ay har gida naso muzo da ita"
"har yanzu na biyo bashi kenan?"
"yanzu dai Aboki ya jikin nata?"
Dr. Shaheed, Ya washe baki tare da k'ara mik'a mishi hannu,
"ina tayaka murna"
"banson iskanci fa, matata na kwance asibiti kace kana tayani murna, meke damunta plz?"
"Koma menene ai aikinka ne mutuminah"
"ni kuma? Kaifa ɗan iskane rashin lafiyar matar tawa ma saika jamun rai?" Dr. Shaheed sai dariya yake mishi ganin ya damu sosai yace,
"Amaryarmu tana ɗauke da juna biyune, na tsawon sati shida"
Ya fiddo duka idanunshi cikin tashin hankali ne koko mamaki? K'ila kuma duk tsantsar farin ciki ne,
"ciki shaheed?"
"k'warai kuwa Aboki, idanta farka zaku iya tafiya, anma bayan ka bani goron Albishir ɗina" ya faɗa cikin zolaya,
Aunty Zainabu dake tsaye a k'ofan tace, "Ai wannan babbar Albishir ne Dr, ni da kaina zan kawo maka"
"Tohh Aunty godia nake,"
Duk majeed yayi sukuku har Dr. Shaheed ya fita, Aunty ta wuceshi taje inda Majeeda take kwance, idanuwanta a buɗe ta farka, anma hawayene kawai ke zuba a idanunta,
"Miye haka Majeeda? Keda zanga murna da farin ciki a fuskarki, miye na kuka kuma?
Shiru tayi ta kasa koda k'ifta idanunta ne, sai dai hawayenda takeyi kawai, Aunty Zainabu tayi maganar harta gaji,
"Aunty Zainabu ina ganin fa murna ce taima Majeeda yawa, wannan kyautah ce Allah ya bamu da ba kowa yake bama ba"
"hakane, ayni namayi tunanin ko ciwonne"
"A'ah da akwai matsala daya faɗamun"
"hakane fa" ta zunguri Majeeda,
"Tashi mu tafi tohh, tun yau kin fara tunanin ciwon nak'uda" saida Majeed yayi dariyar dole,
A hanya ta dinga kiransu momie tana musu Albishir, Abdul-Majeed yana driving ya juyo,
"wai ya kike faɗa musu tun yanzu Aunty?"
"tohh sai yaushe zan faɗa musu? Kaga kuwa yanda suke murna" shiru bai ce mata komi ba, har gidanta suka ajjeta, tana k'ara nanata musu shawarar likita yanda za'ana kula da Majeeda,
Saida ta fita sannan Majeeda ta samu damar fashewa da kuka, baiyi k'ok'arin lallashinta ba har suka isa gidansu, tun kafin ya gama parking ta fito daga motan har tana shirin faɗuwa, ta ruga ta shige ɗakinta, sulalewa k'asa tayi ta ɗaura kanta saman gefen gadon tana kuka,
Ya daɗe a tsaye jikinshi a sanyaye, sannan ya matsa inda take, ya mik'a hannu zai jawota ta buge hannu, ya k'ara mik'a hannu ta tureshi tana ci gaba da kukanta, cikin sanyin jiki ya zauna gefen gadon, sai kuma ta maida kanta samanshi sannan taci gaba da kukan,
Hannunshi yasa yaci gaba da shafar gashin kanta,
"Ya isa hakanan tohh, meye na kuka" ta k'ara k'arfin kukan nata,
"Miye na kuka? Idan banyi kuka ba dariya zanyi saboda ina murna da wannan abun dake jikina?"
"kenan baki murna saboda ɗana yana a jikinki?" tayi tsit tana share hawaye,
"Anma bata wannan hanyar ba Yaya majeed"
"saita wacce hanya? Kenan kuwa har abada bazamu ga ɗanmu ba, kina nufin har yanzu baki kallona a matsayin mijinki?" ta shiga girgiza kai,
"abunda ya kamata muyi murna da farin ciki ne, ki daina kallon cikin dake jikinki a matsayin wanda muka samu a HARAMTACCEN ZAMA, ki kalleshi a yanda kowa ke kallonshi, kema kina sonshi ko?" ta daga mishi kai,
"nima inason duk wani abu dazai fito a jikinki, ina sonki sosae Majeeda"
Ta tashi taɗan rage tsawonta, ta kwantar da kanta jikinshi tana wasu hawayen, ya ɗago da fuskarta
"bazan taɓa bari kiyi kuka ba Majeeda indai ina tare dake" ta juya bayan hannunta tana murmushi zata share hawayenta, ya rik'e hannun,
"na miki alk'awarin share hawayenki, a duk halin da kika tsinci kanki, na farin ciki kona damuwa, ina tare dake"
Ya saka harshe yana share mata hawayen, sai kukan natama ya koma na farin ciki, ya haɗa bakinshi da nata yana kissing ɗinta, har saida yaga hankalinta ya kwanta, sannan ya saketa,
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment