💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
39-40
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Suna cin Abinci suna firarsu, sai dariya duke, kallonsu kawai zakayi ka gane masoya ne dake matuk'ar son juna,
Alama ya mata da idanu data juya taga wasu tsofaffi mata da miji A bayansu, suma soyayyarsu sukesha kamar ba tsofi ba ko a nigeria, da jikanyarsu y'ar yarinya mai kyau, A hankali yace mata,
"na k'agara mu zama kamar tsofinnan"
"nima sun burgeni sosae"
Sun gama suna fitowa suka haɗu da Aisha a hanya, tun kafin su ganta ta tsaya tana kallonsu, hannunsu mak'ale da juna, suna tafiyarsu gwanin sha'awah zuciyarta sai bugawa.
Majeeda taa rigashi ganinta, itama saida k'irjinta ya fara bugawa wani irin kishinta takeji, ta fara k'ok'arin zare hannunta daga nashi, ya rik'eta tsam don shima yaga Aishan, har sukazo suka wuce inda take tsaye kamar bai ganta ba, ta juya taci gaba da kallonsu har suka shiga mota.
Batace mishi komi ba, anma duk jikinta yayi sanyi, shikam baima nuna mata alaman komi ba yaci gaba da janta da fira har saida yaga hankalinta ya kwanta.
"plz Yaya Majeed muje gidansu momie da gidansu Umma"
"Marece yaa farayi sai dai gobe" ta marairaice fuska.
"kaifa kace saina gaji"
"nifa naso mu koma gida, anma ki zaɓa ɗaya dai"
"nidai tohh muje gidan Umma na daɗe banga zahra ba"
"Gidan momie zamuje nan kika daɗe bakije ba"
"Duk yanda kace mijin gidanah" ya harareta da wasa
"mijin gidanki ma ba mijinki ba?" tayi daria sosai,
"hakane mijina, kuma MASOYINA NA HAR ABADA (mrs Umar)"
"gsky naji sunannan yaimin daɗi"
Text ya shigo a wayarshi, tana hannunta tana game, shi kuma yana driving.
"Dubamun text ɗin waye?"
Tayi minimizing sannan ta shiga duba text ɗin, sai da kanta ya sara ganin mai turowan, anma tadai dake.
"karantamun mana" da ɗan washe fuskarta ta fara karanta mishi,
"Wai honiee yaushene zaka daina wahalar da zuciyatah ne? Yanzu don kana tare da wannan banzar matar da bama son ta kake ba zaka shareni" ta k'yalk'yale da daria bayan ta gama karantawa,
"ke kuma miye na daria, sai akace miki ki karanta duka, Aisha ce ko?"
"harma akwai wata bayanta kenan? Nifa aka mawa ba kaika ba, da gaske dariyar ta bani"
"nidai naji haushi, ba tun yau ba nasan kina sane da bata gabana"
"yanzunma ban tambaya bafa"
"tohh nayi shiru matar gidana" sukai dariya lokacin sunzo k'ofar gidansu, aka buɗe mishi gate suka shiga.
Tare suka jera suka shiga falon momie na sallama da bak'uwa, ganinsu da tayi tare tama kasa ɓoye farin cikinta, tayi saurin sallamar bak'uwar ta taho sai k'ara washe baki take,
"tare kuke tafe?" Majeed ya shafa gefen gemunshi ya silalo daga saman kujerar kanshi a k'asa yana gaisheta, Majeeda ta koma inda take ta kwantar da kanta jikinta,
"Momienah inata kewarki"
"ba gashi yanzu kinzo kin ganni ba?"
"ba irin haka ba momie, gidannan ma dukanshi ina kewarshi"
"Rabani da shagwaɓarnan taki, kunyi sa'a ma daddynku yana gida"
Ta tashi tana murna,
"Anma naji daɗi sosae momie bara naje in gaisheshi"
"Tohh ɗiyar daddynta" yanayin momie kawai zaka kalla ka gane tsantsar farin cikin da take ciki.
Majeeda da Majeed tare suka jera suka shiga falon Abba, shima yaji daɗin ganinsu sosae a tare, ya dinga sanya musu Albarka.
Sannan gabanta ya shiga faɗuwa, tama kasa haɗa ido da Abba, duk a tsorace take gani take kamar zai iya gano abinda suke ciki, duk jinta take wata daban,
Ta gaya musu kyautar motar da Majeed ya mata, suka dunga mishi godia sosae,
Majeed ya lura da sukukun da Majeeda tayi, duk hankalinshi na kanta, basu daɗe ba suka tafi.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment