💖HARAMTACCEN ZAMA💖
♠♠♠♠♠♠♠
23-24
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari...
Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Tsayuwar ta fara gajia da ita ta ciro wayarta tana dubawa, ba don tana da abunyi da ita ba, sai don kawai ta rasa abinyi gashi har lokacin ba wani motan da zata hau.
Wata haɗaɗɗiyar mota ce ja, mai shegen kyau ta wuce inda take, sai kuma akayi reverse da motar aka dawo saitin da take, kaudar da kanta tayi sannan ta matsa gefe. Kusan mintina biyar mai motan bai fito ba kuma shi bai tafi ba ita kamar ma batasan da wani mota a wurinba.
Buɗe motan yayi ya fito da takunshi na k'asaita, "Masha Allah" na faɗa saboda irin kyaun dana hango a tattare dashi, harna kusan jefar da wayata kasancewar darene ina tunanin ko Aljani ne, dai dai inda Majeeda take ya tsaya.
"Da alama kina jiran Abin hawa, gashi kuma dare ya fara nisa zai miki wahalan samu" kajimin mutum ko ina ruwanshi dani
"hakane zan samu insha Allah"
"Zai miki wahalan samu fa, kiyi shawara da zuciyarki idan harta amince miki zan kaiki har inda kikeso, babu daɗi kamilalliyar mace kamarki ta tsaya a titi a cikin darennan"
Maganarshi fa hakane, idanma ya tafi ya zata samu wanda zai kaita gida? Kuma da alamar natsuwa a tattare dashi ta san bazai cutar da ita ba, gaba tayi wurin motar kawai ba tace komi ba, ya buɗe mata yaci gaba da karanto addu'ah a ranta.
Har k'ofar gidanta ya kaita "ajjeni nanma yayi" yayi parking ta fito tana mishi godia, murmushi kawai yayi yaja motanshi, dai dai lokacin majeed shima ya sako motanshi kuma yaga lokacinda ta fita daga motan.
Kamar wanda ake hankaɗawa ya shiga gidan tana dai-dai shiga ɗakinta yasha gabanta,
"daga gidan ubanwa kike?" na ɗauka "gidan ubanka zatace"😄 tunda gidansu taje,anma sai tace "gaishe dasu Umma mana, kana da matsala da fitata ne?"
"k'arya kike tun ɗazu Umma tacemun kin taho, wane ɗan iskane ya maidoki?"
"kash!" ta dafe kanta da hannu ɗaya "kaga nama mnta ban tambaya sunanshi ba, ragemin hanya yayi, babu ruwan wani da harkar wani" shiru yayi yana kallonta yama rasa bakin magana, tohh meyasa ma ya tanka mata? Shi ina ruwanshi kowa ma zata kula.
Ta juya ta barshi anan zata shige ɗakinta, k'afarta ta zamo bata ankara ba ta taho zata faɗo da sauri ya tare ta ta faɗa a k'irjinshi ta tallabeta da hannuwanshi, kallonshi take cikin fargaba saboda yanda ta kusa faɗuwa, sai maida numfashi take, shima kallonta yake cikin ido, wani irin yanayi da bai taɓaji ba ya ziyarceshi wannan kallon da suke ma juna.
K'ara matseta yayi a k'irjinshi, tsawon lokaci suna a haka kafinta lumshe kyawawan idanunta ta buɗe, idonshi dai-dai laɓɓanta ta buɗesu a hankali tace "da zafi" yanda ya mata rik'on, sakinta yayi yana dai-daita kanshi, sannan ya juya ya tafi yana waiwayenta, itama kasa motsawa tayi daga inda take ta k'ura mishi ido cikin wani yanayi harya shige ɗakinshi.
Jiki a sanyaye ta shige ɗakinta, ta kasa mantawa da yanayin data motsa fuskar majeed ce ke mata yawo a sanda take a k'irjinshi.
Haka Majeed ma ya kwanta barci da tunanin abinda ya faru, daya rufe idonshi yanayin yake dawo mishi, koda ya buɗe kuwa bazai daina ganinshi da majeeda rungume ba, juyi kawai ya dingayi a lallausar katifarshi yana jiran lokacin da barci zai ɗaukeshi.
Hmm niko nace kome hakan ke nufi??
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment