♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
26-30
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Washe gari tunda Yasseer yadawo daga masallaci, ya koma ya kwanta, bai farka ba sai wurin 11 saboda k'arancin barcin daya samu da dare, ya duba inda Saude take batanan, ya mik'e ya fita wajen ɗakin, can ya hangota tana kwashe shara, daga inda yake yanata kallonta tana aiki.
"Sannu k'anwata, aiki kikasha?"
Juyowa tayi anma bata yarda sun haɗa ido ba, har k'asa ta durk'usa,
"Ina kwana"
"lapia lau ina gajia?"
"Alhmdlh, babu"
"Haba duk wannan aikin da kikasha, waya faɗa miki amarya na aiki?"
"uhm" tace, ta wuceshi zuwa ɗakin daya tashi,
Shima gyaranshi ta shigayi, komai tsaf, daman gyaran katifar ya rage mata da shara, tana cikinyi ta jiyoshi yana kiranta, ta tafi da hanzarinta sai gashi sun haɗu a hanya,
"Saude ina muka samu ruwa? Naaga ko ina a cike"
"Nice na ɗeboshi da asuba"
Da mamakinshi yace "ke kuma? Dagayin auren saiki fita ɗebo ruwa?"
Ta k'ara k'asa da kanta, "babu ruwan da zanyi amfanine, kuma sanda na fita ma harna dawo babu mutane"
"idan fa wani abu ya sameki? Banson ɗebo ruwannan daga yau, zan dinga sawa a ɗauko miki"
"tohm bazan k'ara ba"
"Yauwah, bara in samo mana abun kalaci, nasan kina jin yunwa"
Harya juya tace "Nayi girki fa"
"Kuma dai Saude? A ina kika samu abinda kika girka?"
"Cikin kayanka"
"Kinci abinci kenan?"
"A'ah fa"
"tohh kawomun in gani" ya koma ɗakin, tabi bayanshi, tukunyar abincin ta ɗauko, ta ajje mishi, sannan ta kawo mishi kwano da cokali,
"sannu Saude, mantawa nayi ince miki basai kinyi girki ba, kinga ni bani ma iya break fast idan ba da tea ba" ta ɗaga kai tana kallonshi, don ba duka maganarshi ta gane ba,
"zubamun inci tunda ke kika girka," tace "tohh" sannan ta buɗa tukunyar zata zuba mishi, ya k'walalo ido yana kallon cikin tukunyar,
"menene kika girka?" donshi yamafi mishi kama da tuwon da yayi ruwa, sai kallo yake yaa rasa gane menene, ga k'amshin daudawa kuma yanaji, kodai jallof ɗin tuwo ne?😉
"taliyarnan ce ta cikin leda?" ta bashi amsa,
"taliya kuma?" ya tambayeta da mamaki don duk cikin kayan abincinshi babu taliya,
"ɗaukomun in gani," ta tafi da sauri ta kwaso mishi ledojin indomie, yana gani ya maida kallonshi cikin tukunyar, ta wani dafe, gashi taa huce harta sandare,
"Yanzu wannan taliyarce kikama dahuwar haka?"
Ta ɗaga mishi kai tana murmushin, "eeh mana tafi daɗi idan aka mata dahuwar daudawa"
"nina gani kam, bara in fita in samo bread"
"Abincin fa?"
"kici kawai, anjima zanci"
"Tohh a dawo lafiya"
Yana fita ta zuba indomie ɗinta, ta faraci, itadai tayi mata daɗi, sai da taci sosae taji cikinta ya ɗauka, sannan ta koma ɗaki, ba abinda zatayi, anma bata saba zama hakanan sai tayi ta neman aikin da zatayi.
Bai daɗe ba ya dawo da bread da kayan tea, yace ta ɗaura mishi ruwan zafi, ta haɗa icce ta dafa ta kawo mishi, ya haɗa musu cup biyu,
"tohm taho ki ɗauka naki"
"naci abinci cikina ya cika"
"tohh taho ko tean kisha"
"A'ah na k'oshi"
"Gardama ko Saude?"
"Da gaske Allah"
"tohh shknan",
Saida ya gamasha ya k'oshi, ya koma saman katifan ya kishingiɗa, tana can gefe taa zauna wurin k'ofa, su duka sunyi shiru,
"taso kizo nan Saude" cikin bin umarni ta tashi har inda yake ta tsuguna,
"nan zaki zauna" ta kalli inda yake nuna mata, sannan ta sadda kai bata tashi ba,
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment