♡MATATAH CE♡
♡♡♡♡♡♡
60
©Rabiatu sk msh
®NWA
Labari....Ilileee
www.babymsh.blogspot.com
Su Saude, Aww Saudat😄 anci gaba da zuwa makaranta, kullum mai mata lesson yana zuwa bata gajia da karatu, tanason ckul d'inta sosai, a can kowa so take tayi k'awance da ita, gashi ba iya shiga mutane tayi ba ko k'awar kirkima bata da ita.
Ahmad ne rik'e da wayar Najib hannunshi yana kallon hoto duk ya yamutsa fuska, hotan Saude yake gani wanda tana er k'yauyentane sosai.
"Waida wannan ce Sauden? Gaskia Abokina ka badani, haba idan kana cemun er k'yauyece duk ban d'auka taakai haka ba, gaskia wannan bata dace dakai ba, inaa wannan in mukazo biki ma ai sai abokanmu suna mana dariya"
Yana cikin maganganunshi, Najib ya gano mishi wanda tayi a er birninta,
"Tohm ga Saudat kuma"
"wacece Saudat d'in?"
"Gani da kanka"
"wow Aboki, wannan irin had'uwa haka, ashe daman abunda ka dad'e kana b'oyemun kenan, kullum maganarka baka tashi soyayya yanzu ba, ashe kasan tanajin da kayi, ita kuma wannan ina ka samota?"
"Saude ce"
Coffee daya kurb'ane a bakinshi ya furzar dashi har yana k'warewa,
"Saudence ta koma haka?" ya d'aga mishi kai fuskarshi d'auke da murmushi.
Hotanta na k'yauye da wannan ya ringa comparing, donshi duk bai yarda ba, ya ringa kallon hotan.
"Kai Matan Aurece fa kake mata irin wannan kallon"
"hhh ni kuma abokin mijinta ne"
"wallahi ita d'ince fa, gashinan komai iri d'aya, sai yanzu na lura ana k'yauyenma ashe kyaune da ita sosae, kai Aboki kaayi babban kamu fa, ashe akwai abinda ka gano a bazawarar er k'yauyennan"
"Kaa cika surutu"
"aina kasa tsaida maganata ne, plz indai kaa fasa by any chance, let me know"
"Kayi me dan U***ka, kaifa Namamajo ne"
"Indai na samu kamar wannan aina daina kula kowacce mace, nasan kana son Saudat, anma dai zan k'ara fad'a maka ka rik'eta amana, karka cutar da zuciyarta ta kowanne hanya"
"ina son Saude da yawa Aboki, Soyayyar da ko kaina banayi mawa, ko wani ya b'ata mata rai sai nawa yafi b'aci, Soyayyarta bazata tab'a bari na mata wani abu da zataji ba dad'i ba, Idan harna rasa Saude bani da sauran jin dad'in rayuwa, ita na fara so, kuma da ita nake burin k'are rayuwatah".
"Allah yasa ta soka kamar yanda kakesonta, sai yaushene zaka fad'a mata?"
"saita fara sona"
MOSCOW
Yasseer ne kwance yana barcin rana, wani irin mafarkin Saude yake mai razanarwa, a firgice ya farka yana fad'in.
"MATATAH CE! MATATAH CE!! MATATAH CE!!!" duk ya Had'a zufa don ba k'aramin firgita yayi da mafarkin ba, ada idan yana mafarkin Saude cikin kuka take zo mishi tana neman taimakonshi, anma yanzu cikin farin ciki yake ganinta wani na neman k'wace mishi ita.
Ana gobe zasu tafi moscow saida yaje k'yauyensu Saude cikin dare ya isa da niyyar da safe zai d'aukota ya maida birni ko bada sanin danginshi ba, baije gidan ba saida safe don yaga kalan murnar da zatayi idanta ganshi, sai kuma ya had'u da bak'in labari wai a safiyarnan tabar garin, yasha nemanta harya gaji, ya hak'ura dai ya koma gida kuma a ranar yabar k'asar da maraice, ita kuma a daren ta isa gidansu Yasseer d'in.
Ta bayanshi ta kwanto tana sumbatar wuyanshi ta ko ina, rumtse hannunta yayi cikin nashi ya d'an juyo da fuskarshi yana lumshe ido, muryarta a sark'e tace "waye yace Rabi'ah ba matarka bace? Ni taka ce, sai dai ka k'ara jaddada musu"
Ta had'a bakinta da nashi tana sumbatarshi hannunta akan k'irjinshi, duk taa fara rikitashi, dak'yar yakai hannu ya shafi cikinta a kunne ya rad'a mata,
"Yaushe ne zamu sama baby? Inason yara Rabi'ah"
Buge hannunnashi tayi, "Ba yanzu ba, duka yaushene auren namu? Kuma ko ckul ban fara ba, saina gama gaskia, raino wahala"
Ya jawota jikinshi, "Plz Rabi'ah" tureshi tayi, ta mik'e zata tafi,
"Zan kawo wacce zata haifamun idan ke yana miki wahala" da sauri ta dawo tana huci, ta nunashi da yatsa
"karma ka fara, kai nawane ni kad'ai, babu macen data isa ta rabani dakai" shi dariyama take bashi idan tana nuna kishinnan,
"bazan b'oye miki ba Rabi'ah, hak'urina ya fara k'arewa, inason yara" maganar taa fara gundurarta, ta mik'e ta bashi wuri, yabi bayanta da murmushi kawai.
Rabiah rigima, matsalanshi da ita kawai rashin haihuwa, anma in akazo b'angaren abun ko gajia batayi, kuma yana samun kulawa sosae daga gareta.
Saude ce ta fad'o mishi rai da yaron cikin daya barta dashi, ko wanne hali suke ciki? Dukan k'irjinshi ya shiga yi, ko zaiji sauk'in bugawar da zuciyarshi take mishi, shi kanshi yasan bai kyauta ba, kuma kullum zuciyarshi cikin azabtuwa take da rashinta, 'Ya Allah ka nunamin Saude, da abundata haifa, ya Allah kasa tana tunawa dani kamar yacce koda yaushe take cikin tunani nah'
Tunawa yayi da Rabi'ah fa fushi tayi, yaja tsoki ita abun b'acin rai bai mata wahala, kitchen ya tafi ya sameta, ya kwanto ta bayanta.
"Me ake girka mana duk k'amshi ya cikamun hanci" tureshi tayi ba tare da tace komai ba, ya k'ara kwantotah, ta k'ara tureshi,
"Shikenan, ni daman duk sona da kike cewa nasan ba haka bane tunda kina fushi dani" ya juya kamar zai tafi, da gudu ta tafi ta fad'a mishi tana kuka.
"Plz hniee ka dainamin maganar kishiyarnan, Ina sonka da yawa karka saka zuciyatah ta fashe"
D'ago da fuskarta yayi "ke miye na kuka? Nifa wasa nake miki, banson ganin hawayennan plz" ya saka hannu ya fara share mata, tayi murmushi, "tohm kaima ka daina"
"na daina, bara inje wanka" ta d'aga mishi kai.
Suna zaune dinning ta zuba mishi abinci yanaci, cokalin farko kawai yakai tunanin Saude ne kawai ke dawo mishi, ko tana ina? Wanne hali take ciki? Ita tamaci abincin kuwa? Ji yayi bazai iya ci gaba da ci ba, a yanzu tunanin Saude duk yafi damunshi, ya ajje cokalin kawai ya tashi zai tafi, ta kalleshi duk ta marairaice fuska.
"Bazaka ci abincin ba?"
"zanci sai anjima"
"kodai bai maka dad'i ba?"
"kawai banjin ci ne" yana fad'ar haka ya wuce zuwa d'akinshi, har dare baida wani sukuni, baima k'ara fita ba a ranar, da wuri yayi shirin barci ya kwanta.
Saida ta gama duk abunda take ta shigo d'akin, ta kunne haske idonshi biyu anma da alama tunani yake, ta kashe sannan itama ta haye gadon, shiru bataji ya tanka mata ba kamar baisan da shigowarta ba, ta matsa inda yake ta saka hannu ta fara yawo dashi wurin wuyanshi, jin bai hanata ba ya sanyata komawa samanshi wani fitinannan kiss da dinga binshi dashi, tana aika mishi sak'onni, anma ko motsi baiyi ba, ita kad'ai ke kid'inta da rawarta, wani irin haushinshi taji, takai mishi duka a k'irji.
"koba komai ai saika fad'amun u're not in d mood" jin baiyi magana ba ta k'ara kai mishi wani dukan, ko a jikinshi, tashi tayi ma tabar mishi d'akin.
"Plz Saude ki dawo rayuwatah hakanan, kece farin ciki na"
Yau da gobe a kwana a tashi su Saudat har lokacin fara jarawa (J.S.C.E/J.L.S) yayi, kullum bata da lokaci saina karatu, bataso ta bama Najib kunya, sai dai kuma yawan tunani dake damunta, kullum cikin tunani.
Ranar laraba suka fara exam, tunda wuri take shiri bayan ta gama duk aikin da zatayi, cikin hanzari ta shirya ta tafi makarantar, lokacin da taje har an shiga, ta ajje littafinta harta tafi ta dawo ta k'ara dubawa sannan ta tafi da gudu ta shiga, malamin dake dubasu ne ya tsayar da ita.
"Saudat muhammad! Sai yanzu kike zuwa exam d'in don baki d'auketa serious ba?"
"M srry sir" ta tafi zata wuce sumi-sumi, ya k'ara kiranta.
"ki jira anan, yanda bakizo da wuri ba bazaki fara da wuri ba" idonta kamar zatayi kuka tace "pls sir" hannunshi ya d'aura saman bakinshi, sannan ya nuna mata inda zata tsaya, duk ranta ba dad'i.
Saida suka dad'e da farawa sannan ya mata alamar taje ta zauna, cikin dubara ta share hawayenta taje ta zauna, lokacin daya rage baida yawa, aka mik'a mata question paper ta fara dubawa, amsar data sani baida yawa a ciki nanta fara k'ok'arin tuna hardar da tayi anma kamar wacce akama satar k'walwa, komai ta kasa tunawa, bata rubuta komai a takardarta ba har aka amsa takardar, tun anan ta fara kuka.
Da gudu ta shiga falon Momie ta tare ta,
"Lafiyanki?"
Ta duk'e gabanta tana wani irin kuka, Momie ta dafa kafad'arta tana lallashinta,
"meya faru dake a makarantarne, kukanme kike?"
Ta k'ara fashewa da kuka,
"Nayi karatu Momie, wallahi nayi karatu sosai"
"ni kaina shaidace, fad'amun meya faru?"
Cikin kuka ta bata labarin duk abunda ya faru a wurin exam, sannan ta k'ara da cewa "wallahi nayi karatu momie"
"ki kwantar da hankalinki kinji, yanzu yaushene zaku k'ara wata?"
"friday"
"kinga kina da lokacin karatu sosai, ki daina damuwa nasan zaki iya, nasan bazaki bamu kunya ba"
Ita dai duk hankalinta bai kwanta ba, ta tashi d'akinta tana kuka.
Da Najib ya kira waya Momie ta fad'a mishi, yace a bama Saude wayar, shima kuka kawai ta saka mishi ya ringa lallashinta dak'yar ya samu tayi shiru, sannan ya tambayeta,
"Baki gane lesson d'in da ake miki ne?"
"nifa nayi karatu, komai saida na hardace ina zuwa na manta"
"nasan kinyi karatu, anma daman waya kaiki harda? Indai kika maida hankali kika gane basaikin harda ba kinji ko"
"tohm"
"Yauwah zan dawo gobe, sai in tayaki karatun"
Sannan tayi dariya, "Da gaske gobe zaka dawo?"
"ai naji ko murna bakiyi, nama fasa"
"A'ah dad'inne har yamun yawa, Allah ya kawoka lafiya"
"Ameen k'anwata"
"Ina Hafsat?"
"ta tafi tahfiz"
"tohm bani labari"
"labarin me?"
"komai ma, bani na kanki dai, yau me kika saka? Nasan kinyi kyau sosae"
"umm"
"umm kuma? Fad'amun zakiyi" Momie ta kalla, ba kallonta take ba anma tasan da tayi magana zataji.
"mezan girka maka gobe?"
"kunyar Momie ta hanaki bani amsa ko? Ni saikin fad'amun"
Tashi tayi daga d'akin Momien sukaci gaba da waya, bai k'yaleta ba saida ya tabbatar hankalinta ya kwanta bata da sauran damu, sannan ya yarda ta ajje wayar.
©Rabiatu sk msh
0 comments:
Post a Comment