New Post

Sunday, 16 October 2016

ABDUL WAHAB 23

ABDUL WAHAB 23

©Rabiatu sk msh
          ®NWA

Hidimar bikin fatima kawai ake, kullum basu da zama, shirye shirye kawai suke da tsarin yanda bikin zai kasance, ga rabon i.v da gyaran jikin amarya, itama sadeey ba'a barta a baya ba don akwaita da son gyara.

Duk hidimar bikinnan bata yarda ta 'kara zuwa gidansu Abdul, har fatima taayi nacinta taa gaji, sai dai ta biyo mata su wuce.

Koda satin bikin ya kama aka fara programmes babu wanda sadeey taje, fatima har fushi tayi da ita, Mami ma har fad'a tayi mata ta saka mata kukan ita ba zata iya zuwa ba, bata son duk wata hanya da zata had'a ta da Abdul.

Shima duk hidimar bikinnan baida wani aiki sai zaman d'akinshi, gashi yanzu hajia ko kad'an bata sakar mishi fuska, tun tuni taso a had'a bikinshi dana fatima anma yaa'ki ya kawo mata, yanzu gaisuwarshi ma da'kyar take amsawa, duk damu taa taru taayi mishi yawa.

Raheem ne yace "Abokina dolene fa kayi abnda hajia zata huce dakai, kuma sadeey ma ka wanke laifin da kayi mata," Yace "ta wacce hanya kenan? Banji me yace mishi ba sai dai Abdul yace "kana ganin hakan zai yiwu? Raheem yace "sosae ma kuwa, don kai kanka kasan sadeey na matukar sonka, Alhajin kawai zaka samu da maganar, ko kanaso ka cemin kai baka fara sonta ba?

Sai yanzu naga murmushin Abdul Yace "ba farawa ba Raheem, sai yanzu na gane soyayyar da nake yima sadeey, da da na kasa ganewa, tabbas nayi kuskure, anma kai zaka taimakamin wurin gyarota.

Yace "shikenan anjima nizan rakaka wurin Alhajin.

Koda sukajema Alhaji da maganar, kasa 'boye farin cikinshi yayi, don shima yasan irin sonda sadeey ke yima Abdul kuma yaa dad'e da sha'awar had'asu aure, hajia ma taaji dad'i sosae koda Alhaji ya nemi shawararta cewa tayi komi yayi dai dai ne su duka yaranshi ne.

Mami ce ta bada shawarar kar a fad'ama sadeey yanzu, kowa ya amince da shawararta.

Dedicated to Mr. Smiles😃

❤❤Rabiatu sk msh❤❤

Related Posts:

  • MAKASHINKA 15-16```MAKASHINKA...```           15-16 ©Rabiatu sk msh Tunda ta dawo daga rakiyar khadija take ta zagaye falon tunani da yawa cunkushe a zuciyarta. Da dare ta kwanta, bata samu b… Read More
  • MAKASHINKA 13-14```MAKASHINKA...```             13-14 ©Rabiatu sk msh Khadija bata matsa ba sadeey sai tasan abinda ke damunta ba, ita a ganinta ma ko aljanune suka taɓata, da … Read More
  • MAKASHINKA 17-18```MAKASHINKA...```          17-18 ©Rabiatu sk msh Kwananta biyu bata kula wayarta ko saƙo yaa shigo, ko kiranta akai tunda ta lura ko kasheta tayi tana kunnuwa, duk inda zata… Read More
  • MAKASHINKA 11-12```MAKASHINKA...```           11-12 ©Rabiatu sk msh~ Zama tayi tana kallonshi cikin jin haushi da ƙara ƙuluwa, duk da haka bai bar dariar ba, saida yayi mai isheshi … Read More
  • MAKASHINKA 9-10```MAKASHINKA...```          9-10 ©Rabiatu sk msh Tananan zaune har 10pm, saiga momie ta fito, har zata wuce ɗakin Abba ta hangota ta taho inda take tana mata kallon mamaki M… Read More

0 comments:

Post a Comment

Popular Posts